Sashe 78
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Umma ta k’ara masa godiyan d’awainiyar da yake da kub’utar da Sadiya hannun ‘yanta’adda da yai.
Kansa a k’asa yaketa sakin murmushi a hankali. Aunty Larai na taya Umma. Daga bisani Umma mik’ewa tai Ta basu waje shida Aunty Larai, nan Aunty Larai d’in ke fad’in bari a kawo masa abinci.
Ya d’an girgiza kai yace zai koma asibiti wajen Assad ne.
Aunty Larai ta mik’e tana fad’in “A’a haba dai Malam D’ansanda da ganinka baka wani ci abinci ba.. Kaga barin turo maka Amaryar taka ta kawo maka..”
Jin zata turo Sadiya ta kawo masa yasa baice komai ba Sai murmusawa kawai da yai.. Aunty Larai ta mik’e ta nufi ciki.
Sadiya na tare da k’annenta Aunty Larai ta shigo.. Sadiya ta kuma gaisar da Aunty Larai cikeda girmamawa kafin Aunty Larai taceda Ita ta taso suje kitchen..
Babu musu Sadiya ta mik’e tabi bayanta.. Suna kitchen d’in Aunty Larai tana nuna mata abubuwan da Zata tayata dasu, Sai janta da hira take Dikda Sadiya ba wani amsawa take ba sai murmusawa da take.. Nan Anty Larai Ta hango alamun cannula hannunta tace “Na mance ashe fah sirkar tamu patient ce... Amma bara na tayaki da d’aukan masu nauyi Kinsan ba’a barin mai Gida da yunwa..”
Sadiya dai batace komai ba sai murmushi da take wanda yafi kama da yak’e. Ta kula Matar akwai magana bakinta baya shiru sam.
A haka suka nufo parlorn rik’e da trays na abincin. Bakin Aunty Larai bai shiru ba. Sadiya tana direwa Ta mik’e da zummar tafiya saiji tai Aunty Larai ta rik’ota ta dawo da ita.. “A’a Haba Amaryarmu.. A ina kika tab’a jin an k’yale maigida yaci abinci shi kad’ai.. Zauna gefensa kunaci tare yana kallon kyakkyawar fuskar nan taki haka akeyi.. Kakanninmu sunce hakan na k’ara dank’on k’auna tsakanin ma’aurata.”
Mu’azzam ya saci kallonta jin abinda Aunty Larai Ta fad’i.. Kana ganinta kasan dan dole take aiwatar da komai.. Dan dai Babu yanda ta iya ne.
Aunty Larai Ta mik’e Ta kunna masu tv tana mai fad’in “Yauwa na barku lafiya.. Ku cinye komai mu gidan nan ba’a bari mana sauran abinci..” Tana ida fad’in haka ta shige ta janyo k’ofar corridor d’in ta rufe aka barsu su biyu parlorn.
Kaman babu mai cewa komai Mu’azzam ya d’an dubeta kafin yai gyaran murya yace “Aren’t you hungry..?”
Ta girgiza masa kai alamun a’a..
“You must be.. Bayan drip babu abinda kikaci..” Ya fad’i yana dubanta kafin yace “Serve us now..”
Ita mamaki ma yake bata yanda yakeyi kaman dai babu wani abinda ya faru.
Ta d’an d’ago baki a ture tace “I’m Ok.. Ni bazanci ba..”
Ya jinjina kai yace “Toh ni zan ci.. Serve your husband..”
Gyara zamanta Ta d’anyi kafin tace “Mr Inspector.. As far as I know the mission is over now.. kuma na baro GIDAN ARO.. Why don’t you end this fake marriage once and for all.. Ka sanar dasu cewa auren mission mukai kuma ya k’are..”
Murmusawa yai kad’an kafin yace “As far as I know, I didn’t sign any agreement.. Bamuyi haka a rubuce ba.. Iyakacin abinda na sani shine inada shaidu da zasu tabbatar da cewa ni mijinki ne, and that means zakiyi duk abinda na umarceki... And don’t get this wrong dan na kawoki nan.. I brought you here because of what the Dr said.. Ba dan yace a kawoki nan d’in ba da Gida muka wuce.”
Ya nad’e hannaye kafin yai mata alama da ido zuwa plate d’in “Serve your husband..”
Ta d’an juyar da kanta tana fuzar da fuci kafin ta juyo tana dubansa “Kana tinanin na mance abinda kai mun ne.. Bazan tab’a yafe maka ba kuma zanyi k’ararka a ofishinku na ‘yansanda..”
Wannan karon dariya ne yazo masa, ya d’an ciza labb’ansa na k’asa kad’an had’ida kauda kansa yana mai danne dariyarsa. Lokaci guda ya juyo yana dubanta “Oh really..? Toh idan kikaje filing case d’in mai zakice..?”
Tana huci tace “First I’ll file a case of kidnapping.. And second..” Sai kuma tai shiru kaman wacce aka rufe mata baki, Ta kasa duban cikin k’wayar idanunsa, sai ma kauda kai da tai tana sakin huci a hankali.
Mu’azzam ya murmusa kafin ya janyo plate d’in ya soma zuba abincin yana ci gaba da fad’in “A ina aka tab’a k’aran miji dan ya d’auke matarsa..? As far as I know babu dokar data hana haka koda ta yahudu ce.. Na biyunsa zakiyi k’arar miji dan zai amshi hakkinsa wajen matarsa.. Wanann ma banaji akwai yanda za’a saurareki.. Am I right..?” Ya k’adashe yana dubanta.
Idanunta sukai rau rau.. Tasa d’aya hannun nata tana gogewa.. Baice mata komai ba har ta gama goge hawayen kafin ya d’ibo abinci cikin spoon yace “You’re still weak, Oya open your mouth..”
Ta dubesa a dak’ile, sai kuma ta mak’e kafad’ar ta alamun ta k’oshi.
Ya tsime sosai wannan karon “Idan bakici ba Kinsan Allah zan d’aukeki mu tafi gida yanzun nan.. Kinsan zan kuma zan aikata hakan..”
Jin abinda yace ya sanyata bud’e baki a hankali. Ya saka mata spoon d’in cikin bakinta. Ta lumshe idanunta a hankali wani hawayen na gangaro mata.. Yayinda Mu’azzam yai mata K’uri yana duban fuskarta.
Ya sake d’ibo abincin ya kuma kaiwa saitin bakinta, ta kauda kanta gefe.. Tsareta da idanu wann karon yai ba tareda yace komai ba. Hakan yasa babu yanda ta iya ta kuma bud’e bakinta. Saida ya bata kusan five spoons kafin ta girgiza masa kai kaman zata saki kuka tana fad’in ita ta k’oshi.
Ya k’ura mata idanu yana mamakin yanda tsiwarta ya ragu, da da ne ba kuka zata sakar masa saidai ta murgud’a masa d’an bakin nan nata da yafi komai d’aukar hankalinsa a kyakkyawan fuskarta.
Wayarsa ce Tai k’ara ya duba yaga Yusuf ne mai kira. Ya d’an mik’e yana amsa wayar kaman zai fice da alama update yake basa kan Assad.
Ganin haka yasa Sadiya saurin mik’ewa zata nufi corridor.. Kafin ta isa k’ofar yai saurin fuzgo hannunta ta fad’o jikinsa, still yana wayar.. Ta soma k’ok’arin cire jikinta dags nasa amma ta kasa dukda cewa da hannu guda kawai ya rik’eta.
Sukai sallama da Yusuf yace masa yana nan tafe yanzun nan. Lokaci guda ya kashe wayar yana duban yanda take ta faman daddage k’arfinta tana k’ok’arin cire hannunsa daga jikinta. Harda ciza labb’a tai alamun Takai mak’ura wajen tattaro duka k’arfinta.
Ya murmusa kad’an kafin yai amfani da d’aya hannun ya tallafo kunkuminta, ya matso da ita kusansa sosai had’ida k’ura mata idanu.. Wani irin fad’uwan gaba ne taji ya sauk’ar mata musamman da ta d’ago ido taci karo da murmushin dake bisa fuskarsa.. Ita zata iya cewa tafi sabawa da d’aure fuska da yake.. Ta alak’anta fad’uwan gaban nata da wannan fake murmushin da Ta gani samar fuskarsa.
“Please let me go..” Ta fad’i kaman zatai kuka.
Hannunsa guda yasa ya d’ago hab’arta suna duban juna, zuciyarta naci gaba da yankewa. Ya soma matso da fuskarsa kusan nata kaman dai zai kai mata sunba.. Tai saurin rintse idanunta tana jin bugun zuciyarta na k’aruwa.
Saitin kunnenta na dama taji sauk’an labb’ansa, cikin sigan rad’a yake furta “Lets go back home.. The house misses you..”
K’ok’arin tattaro duka k’arfinta tai had’ida turasa baya “That house was never mine.. And it will never be.. Ka mance menene sunan gidan a wajena..? GIDAN ARO..” Ta jinjina kai kafin taci gaba da fad’in “You said it yourself, Mr Inspector..”
Murmusawa yai da gefen bakinsa kafin ya soma matsowa kusanta tana jada baya.. Har saida taji kujera ya tokareta alamun wajen gudu ya k’are kafin Ta tsaya tana mai kwantar da bayanta saman kujerar alamun bataso ya matso kusanta.. Ya kwanto shima had’ida mik’a hannunsa guda ya rik’o bayanta yace “Give your husband a goodbye kiss..”
Bugun zuciyarta ya k’aru ganin abinda yake, what if wani ya bud’e k’ofar ya gansu haka.. Bata ida tinanin ba tai saurin take k’afarsa guda da k’arfin gaske.
Ya d’an saki k’ara yana kame k’afarsa.. Ya janyota ya d’agota tsaye yana fad’in “Hey That was a kick and not a kiss..”
Ta k’unshe dariyarta ganin yanda ya rik’e k’afarsa yana d’an sakin k’ara a hankali kai kace zafi yaji da gaske.
Lokaci guda Ta jinjina kai tace “I know.. Abinda ya kamaceka kenan.. Mr Inspector..” Ta turasa da duka hannayenta biyu kafin ta isa a guje ta bud’e k’ofar ta shige cikin sauri bugun zuciyarta na k’aruwa.
Mu’azzam yabi bayanta da kallo yana murmushi kafin yasa kai ya fice daga parlorn.. Sadiya dake kallonsa ta ramin k’ofa yana ficewa ta Sauk’e ajiyan zuciya had’ida juyowa.
Ido hud’u sukai da Aunty Larai.. Gaba d’aya sai taji kunya ya rufeta..
Aunty Larai ta murmusa tace “Har angon namu ya wuce ne..?”
Sadiya ta sadda kanta k’asa kad’an kafin ta jinjina mata kai a hankali alamun eh.. Aunty Larai ta janyota tana fad’in “Ki saki jiki dani kinji koh.. Mu’azzam d’ah na ne amma babu wani surkunta tsakanina dake dan ked’in ma d’iyata ce.. Mu k’arasa ciki..” Suka shige ciki hannunta rik’e cikin na Aunty Larai suka nufi ciki suka tadda Su Umma.
**
FUFORE
Yau ma kaman kullum tana zaune tana tinanin mutumin da ko sunansa bata sani ba. Iyakacin abinda ta sani shine tayi kewarsa sosai sannan Gidan gonar ya canza tin sanda ya tafi garinsu.
Mama Hindu Ta K’araso Ta sameta tana nan zaune batai wankan ba. Ta d’an girgiza kai ta k’araso ta dafata kad’an tace “Ajidde Wai bazaki tashi Kiyi wankan ki baiwa Aunty Nuratu maganinta ba.. Duba kiga lokaci nata tafiya.. Waima tunanin mai kike ne..?”
Ajidde ta mik’e tana turo baki “Kai Mama Hindu Wai ni idan nazo gidan nan dole ne Sai nayi wanka.. Ni wllhi na gaji haba.. Wai dan Allah Mama Hindu waye ya saka mun wannan dokar a gidan nan..?”
Mama Hindu Ta murmusa tace “Idan ban Fad’a miki ba ma kinyita damuna kenan.. Modibbon Inne shi ya bada wannan dokar.. Yace kullum kafin ki baiwa mahaifiyarsa magani na tabbata babu datti jikinki.. Toh amma ko kefa yanzu Kinga kina wanka kina wanke bakinki.. Gashi asalin kyakkyawar bak’ar fatarki ta kuma fitowa tas gwanin kyau.. Ga hak’waranki yanzu sun dawo farare tas tas.. Tsafta da dad’i ai Ajidde..”
Kansa a k’asa yaketa sakin murmushi a hankali. Aunty Larai na taya Umma. Daga bisani Umma mik’ewa tai Ta basu waje shida Aunty Larai, nan Aunty Larai d’in ke fad’in bari a kawo masa abinci.
Ya d’an girgiza kai yace zai koma asibiti wajen Assad ne.
Aunty Larai ta mik’e tana fad’in “A’a haba dai Malam D’ansanda da ganinka baka wani ci abinci ba.. Kaga barin turo maka Amaryar taka ta kawo maka..”
Jin zata turo Sadiya ta kawo masa yasa baice komai ba Sai murmusawa kawai da yai.. Aunty Larai ta mik’e ta nufi ciki.
Sadiya na tare da k’annenta Aunty Larai ta shigo.. Sadiya ta kuma gaisar da Aunty Larai cikeda girmamawa kafin Aunty Larai taceda Ita ta taso suje kitchen..
Babu musu Sadiya ta mik’e tabi bayanta.. Suna kitchen d’in Aunty Larai tana nuna mata abubuwan da Zata tayata dasu, Sai janta da hira take Dikda Sadiya ba wani amsawa take ba sai murmusawa da take.. Nan Anty Larai Ta hango alamun cannula hannunta tace “Na mance ashe fah sirkar tamu patient ce... Amma bara na tayaki da d’aukan masu nauyi Kinsan ba’a barin mai Gida da yunwa..”
Sadiya dai batace komai ba sai murmushi da take wanda yafi kama da yak’e. Ta kula Matar akwai magana bakinta baya shiru sam.
A haka suka nufo parlorn rik’e da trays na abincin. Bakin Aunty Larai bai shiru ba. Sadiya tana direwa Ta mik’e da zummar tafiya saiji tai Aunty Larai ta rik’ota ta dawo da ita.. “A’a Haba Amaryarmu.. A ina kika tab’a jin an k’yale maigida yaci abinci shi kad’ai.. Zauna gefensa kunaci tare yana kallon kyakkyawar fuskar nan taki haka akeyi.. Kakanninmu sunce hakan na k’ara dank’on k’auna tsakanin ma’aurata.”
Mu’azzam ya saci kallonta jin abinda Aunty Larai Ta fad’i.. Kana ganinta kasan dan dole take aiwatar da komai.. Dan dai Babu yanda ta iya ne.
Aunty Larai Ta mik’e Ta kunna masu tv tana mai fad’in “Yauwa na barku lafiya.. Ku cinye komai mu gidan nan ba’a bari mana sauran abinci..” Tana ida fad’in haka ta shige ta janyo k’ofar corridor d’in ta rufe aka barsu su biyu parlorn.
Kaman babu mai cewa komai Mu’azzam ya d’an dubeta kafin yai gyaran murya yace “Aren’t you hungry..?”
Ta girgiza masa kai alamun a’a..
“You must be.. Bayan drip babu abinda kikaci..” Ya fad’i yana dubanta kafin yace “Serve us now..”
Ita mamaki ma yake bata yanda yakeyi kaman dai babu wani abinda ya faru.
Ta d’an d’ago baki a ture tace “I’m Ok.. Ni bazanci ba..”
Ya jinjina kai yace “Toh ni zan ci.. Serve your husband..”
Gyara zamanta Ta d’anyi kafin tace “Mr Inspector.. As far as I know the mission is over now.. kuma na baro GIDAN ARO.. Why don’t you end this fake marriage once and for all.. Ka sanar dasu cewa auren mission mukai kuma ya k’are..”
Murmusawa yai kad’an kafin yace “As far as I know, I didn’t sign any agreement.. Bamuyi haka a rubuce ba.. Iyakacin abinda na sani shine inada shaidu da zasu tabbatar da cewa ni mijinki ne, and that means zakiyi duk abinda na umarceki... And don’t get this wrong dan na kawoki nan.. I brought you here because of what the Dr said.. Ba dan yace a kawoki nan d’in ba da Gida muka wuce.”
Ya nad’e hannaye kafin yai mata alama da ido zuwa plate d’in “Serve your husband..”
Ta d’an juyar da kanta tana fuzar da fuci kafin ta juyo tana dubansa “Kana tinanin na mance abinda kai mun ne.. Bazan tab’a yafe maka ba kuma zanyi k’ararka a ofishinku na ‘yansanda..”
Wannan karon dariya ne yazo masa, ya d’an ciza labb’ansa na k’asa kad’an had’ida kauda kansa yana mai danne dariyarsa. Lokaci guda ya juyo yana dubanta “Oh really..? Toh idan kikaje filing case d’in mai zakice..?”
Tana huci tace “First I’ll file a case of kidnapping.. And second..” Sai kuma tai shiru kaman wacce aka rufe mata baki, Ta kasa duban cikin k’wayar idanunsa, sai ma kauda kai da tai tana sakin huci a hankali.
Mu’azzam ya murmusa kafin ya janyo plate d’in ya soma zuba abincin yana ci gaba da fad’in “A ina aka tab’a k’aran miji dan ya d’auke matarsa..? As far as I know babu dokar data hana haka koda ta yahudu ce.. Na biyunsa zakiyi k’arar miji dan zai amshi hakkinsa wajen matarsa.. Wanann ma banaji akwai yanda za’a saurareki.. Am I right..?” Ya k’adashe yana dubanta.
Idanunta sukai rau rau.. Tasa d’aya hannun nata tana gogewa.. Baice mata komai ba har ta gama goge hawayen kafin ya d’ibo abinci cikin spoon yace “You’re still weak, Oya open your mouth..”
Ta dubesa a dak’ile, sai kuma ta mak’e kafad’ar ta alamun ta k’oshi.
Ya tsime sosai wannan karon “Idan bakici ba Kinsan Allah zan d’aukeki mu tafi gida yanzun nan.. Kinsan zan kuma zan aikata hakan..”
Jin abinda yace ya sanyata bud’e baki a hankali. Ya saka mata spoon d’in cikin bakinta. Ta lumshe idanunta a hankali wani hawayen na gangaro mata.. Yayinda Mu’azzam yai mata K’uri yana duban fuskarta.
Ya sake d’ibo abincin ya kuma kaiwa saitin bakinta, ta kauda kanta gefe.. Tsareta da idanu wann karon yai ba tareda yace komai ba. Hakan yasa babu yanda ta iya ta kuma bud’e bakinta. Saida ya bata kusan five spoons kafin ta girgiza masa kai kaman zata saki kuka tana fad’in ita ta k’oshi.
Ya k’ura mata idanu yana mamakin yanda tsiwarta ya ragu, da da ne ba kuka zata sakar masa saidai ta murgud’a masa d’an bakin nan nata da yafi komai d’aukar hankalinsa a kyakkyawan fuskarta.
Wayarsa ce Tai k’ara ya duba yaga Yusuf ne mai kira. Ya d’an mik’e yana amsa wayar kaman zai fice da alama update yake basa kan Assad.
Ganin haka yasa Sadiya saurin mik’ewa zata nufi corridor.. Kafin ta isa k’ofar yai saurin fuzgo hannunta ta fad’o jikinsa, still yana wayar.. Ta soma k’ok’arin cire jikinta dags nasa amma ta kasa dukda cewa da hannu guda kawai ya rik’eta.
Sukai sallama da Yusuf yace masa yana nan tafe yanzun nan. Lokaci guda ya kashe wayar yana duban yanda take ta faman daddage k’arfinta tana k’ok’arin cire hannunsa daga jikinta. Harda ciza labb’a tai alamun Takai mak’ura wajen tattaro duka k’arfinta.
Ya murmusa kad’an kafin yai amfani da d’aya hannun ya tallafo kunkuminta, ya matso da ita kusansa sosai had’ida k’ura mata idanu.. Wani irin fad’uwan gaba ne taji ya sauk’ar mata musamman da ta d’ago ido taci karo da murmushin dake bisa fuskarsa.. Ita zata iya cewa tafi sabawa da d’aure fuska da yake.. Ta alak’anta fad’uwan gaban nata da wannan fake murmushin da Ta gani samar fuskarsa.
“Please let me go..” Ta fad’i kaman zatai kuka.
Hannunsa guda yasa ya d’ago hab’arta suna duban juna, zuciyarta naci gaba da yankewa. Ya soma matso da fuskarsa kusan nata kaman dai zai kai mata sunba.. Tai saurin rintse idanunta tana jin bugun zuciyarta na k’aruwa.
Saitin kunnenta na dama taji sauk’an labb’ansa, cikin sigan rad’a yake furta “Lets go back home.. The house misses you..”
K’ok’arin tattaro duka k’arfinta tai had’ida turasa baya “That house was never mine.. And it will never be.. Ka mance menene sunan gidan a wajena..? GIDAN ARO..” Ta jinjina kai kafin taci gaba da fad’in “You said it yourself, Mr Inspector..”
Murmusawa yai da gefen bakinsa kafin ya soma matsowa kusanta tana jada baya.. Har saida taji kujera ya tokareta alamun wajen gudu ya k’are kafin Ta tsaya tana mai kwantar da bayanta saman kujerar alamun bataso ya matso kusanta.. Ya kwanto shima had’ida mik’a hannunsa guda ya rik’o bayanta yace “Give your husband a goodbye kiss..”
Bugun zuciyarta ya k’aru ganin abinda yake, what if wani ya bud’e k’ofar ya gansu haka.. Bata ida tinanin ba tai saurin take k’afarsa guda da k’arfin gaske.
Ya d’an saki k’ara yana kame k’afarsa.. Ya janyota ya d’agota tsaye yana fad’in “Hey That was a kick and not a kiss..”
Ta k’unshe dariyarta ganin yanda ya rik’e k’afarsa yana d’an sakin k’ara a hankali kai kace zafi yaji da gaske.
Lokaci guda Ta jinjina kai tace “I know.. Abinda ya kamaceka kenan.. Mr Inspector..” Ta turasa da duka hannayenta biyu kafin ta isa a guje ta bud’e k’ofar ta shige cikin sauri bugun zuciyarta na k’aruwa.
Mu’azzam yabi bayanta da kallo yana murmushi kafin yasa kai ya fice daga parlorn.. Sadiya dake kallonsa ta ramin k’ofa yana ficewa ta Sauk’e ajiyan zuciya had’ida juyowa.
Ido hud’u sukai da Aunty Larai.. Gaba d’aya sai taji kunya ya rufeta..
Aunty Larai ta murmusa tace “Har angon namu ya wuce ne..?”
Sadiya ta sadda kanta k’asa kad’an kafin ta jinjina mata kai a hankali alamun eh.. Aunty Larai ta janyota tana fad’in “Ki saki jiki dani kinji koh.. Mu’azzam d’ah na ne amma babu wani surkunta tsakanina dake dan ked’in ma d’iyata ce.. Mu k’arasa ciki..” Suka shige ciki hannunta rik’e cikin na Aunty Larai suka nufi ciki suka tadda Su Umma.
**
FUFORE
Yau ma kaman kullum tana zaune tana tinanin mutumin da ko sunansa bata sani ba. Iyakacin abinda ta sani shine tayi kewarsa sosai sannan Gidan gonar ya canza tin sanda ya tafi garinsu.
Mama Hindu Ta K’araso Ta sameta tana nan zaune batai wankan ba. Ta d’an girgiza kai ta k’araso ta dafata kad’an tace “Ajidde Wai bazaki tashi Kiyi wankan ki baiwa Aunty Nuratu maganinta ba.. Duba kiga lokaci nata tafiya.. Waima tunanin mai kike ne..?”
Ajidde ta mik’e tana turo baki “Kai Mama Hindu Wai ni idan nazo gidan nan dole ne Sai nayi wanka.. Ni wllhi na gaji haba.. Wai dan Allah Mama Hindu waye ya saka mun wannan dokar a gidan nan..?”
Mama Hindu Ta murmusa tace “Idan ban Fad’a miki ba ma kinyita damuna kenan.. Modibbon Inne shi ya bada wannan dokar.. Yace kullum kafin ki baiwa mahaifiyarsa magani na tabbata babu datti jikinki.. Toh amma ko kefa yanzu Kinga kina wanka kina wanke bakinki.. Gashi asalin kyakkyawar bak’ar fatarki ta kuma fitowa tas gwanin kyau.. Ga hak’waranki yanzu sun dawo farare tas tas.. Tsafta da dad’i ai Ajidde..”