← Book details Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 152 OF 175

Sashe 152

Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Danger na murmushi da gefen bakinsa still Hajiya Faty tana cikin hannunsa yayi pointing d’inta da bindiga yake fad’in “Bazan tab’a baka wann satisfaction d’in ba Inspector.. Bazan tab’a tsayuwa ka kamani ba.. Never..”

Mu’azzam dake aika masa mugun kallo yunk’urowa yai zai k’araso yanda yake.. Take Danger ya kuma danna bakin bindigar akan Hajiya Faty yana fad’in “If you take one more step believe me I won’t hesitate to blow her head..” Lokaci guda ya amshe document d’in ya soma jada baya yana rik’eda Hajiya Faty daketa kuka tana fad’in kar ya kasheta, taga mutuwa muraran.

Mu’azzam yai mata alama da ido sanda zasu hauro saman rug cewa tai tuntub’e da carpet d’in.

Hajiya Faty zufa duk ya wanketa aiko ta fahimci abinda Mu’azzam ke nufi dukda tsoro da ya cikata.. Suna k’arasowa saman rug tai tuntub’e ta nufi k’asa.. Shiko Danger tuni ya saki harbi wa Mu’azzam yana mai arcewa a guje, saidai Mu’azzam ya kaucewa harsashin bata samesa ba.. A wani irin speed yabi bayan Danger a guje dake rik’eda document d’in yana kiran sunansa.. Danger yai tsalle daga saman balcony ya fad’o k’asa.. Mu’azzam ma ya kama k’arfen balcony din yai tsallen yana chasing d’insa.

Danger zai fice daga gidan kenan yaji sautin motan ‘Yansanda ya cika unguwar.. Cak ya tsaya yana sakin huci yana lissafin ta yanda zai arce.. Take ya kuma nufan wani hanyar cikin k’warewa da ta’addanci zai kama garu dudka tsaron dake saman garun.. Mu’azzam yai wata tsalle ya tokare bayansa ya fad’o.. Haba nan fah ya shiga naushin Danger yana kai masa hannu da k’afa.. Danger ya soma k’ok’arin ramawa saidai yanda Mu’azzam ke masa bugun zazzab’en dawa gaba d’aya ya fice a hayyacinsa.. Yai k’ok’arin kaima Mu’azzam d’in naushi a hanci wanda saida ya fitar masa da jini.. Mu’azzam ya fad’i gefe yana rik’e bakinsa da hancinsa.. Danger ya samu sararin rarrafawa ya d’auki takardan zai gudu Mu’azzam yai k’ok’arin mik’ewa ya tokari bayansa ya fad’i.. Cakumosa yai da duka hannayensa su duka biyun fuskokinsu jini ne.

Daidai nan ‘Yansandan suka soma shigowa cikin gidan.

Huci kurum Mu’azzam yake yana rik’eda Danger yana jinjina kai a hankali, lokaci guda yake furta “Finally, we get to see each other again.. What are you afraid of you Bastard.. Dying in prison or dying from a gunshot.?!” Ya k’arashe yana mai kuma kai masa wata naushin da Ta kuma gigita Danger.

Dikda layi da Danger keyi hakan bai hanasa murmusawa yana fad’in bazai bar Mu’azzam yaci nasara akansa ba. Mu’azzam ya kuma kai masa naushi da ta kusa sumar da Danger. Lokaci guda ya jefasa ma Yansandan yana fad’in “Take him away..” Suka sara masa suna masu janye Danger.

Ya k’arasa yana duban takardan envelope d’in wanda ga haruffan BAT rubuce sama, take yaji wani abu kaman hawaye na ciko idanunsa. A hankali ya mik’a hannunsa ya d’auki doguwar envelope d’in.

Daga k’arshe dai ya mallaki takardan cikin hannunsa.. Takardan da yakeda tabbacin shine ummulhaba’isin dik wani rikici da ahalinsa ke fuskanta.

Yana nan tsaye yana juya takardan Hajiya Faty ta k’araso tana hawaye.

Ya d’ago idanu yana dubanta envelope d’in rik’e hannunsa.

Cikin zuban hawaye Hajiya Faty ke fad’in “Wann shine takardan da nace zan baka.. Hajara ita ta bani ajiyan wann takarda.. Bayan abubuwan da Hajara ta sanar dani ta aikata naji tsoron duniya na kuma raina ma kaina da makircina na bin bokaye.. Nan na fahimci ashe ni k’aramar maras kunya ce idan zan jira boka ya min aikin asiri.. Hajara ita bata jira ta’addanci take a zahirinsa.. Mun aikata wani abu a baya da dole na nemi yafiyarka.. Mu’azzam..” Ta k’arashe tana mai duk’awa saman gwiwoyinta. Cikin rawar murya kanta a k’asa taci gaba da fad’in “Hak’ika yau ka cececi rayuwata.. D’an Nuratu ya ceci rayuwata daga hannun wann D’antaddan wanda ba kowa ya turo sa ba face Hajara..”

Mu’azzam yaci gaba da dubanta babu d’igon mamaki tattare dashi dan a halin yanzu baijin mamakin abubuwan da Mommy tai.. Saurin katseta yai da fad’in “Mai kuka aikata wa Mahaifiyata..?”

Hajiya Faty na duk’e tana hawaye take fad’in “Mahaifiyarka ba had’arin Mota tai ba a lokacin da za’a kawota gidan mijin Hajara.. An saka abin ne ya zamana tamkar dai had’arin mota ne.. Ni ce nan na raka Hajara wajen boka aka kwantar da mahaifiyarka bayan an tura mata bak’in Shaid’ani.. Da fari kasheta tasoyi har lahira da hannayenta sabida ita bata jiran boka ya mata a cewarta, toh amma kashe Nuratu daidai yake da kashe Alhaji Marwan sabida tsananin soyayyar da yake mata, shiyasa Hajara ta zab’i boka a ya mata aiki akan Nuratu Ta barta ita ba’a raye ba ita ba’a mace ba..!” Kuka ya hanata ci gaba da magana, yayinda Mu’azzam ke tsaye Cak yana dubanta da idanunsa da suka gama rinewa zuwa ja, hawaye na gangarowa daga cikinsu yana gaurayuwa da jinin dake fuskarsa.

Hajiya Faty taci gaba da fad’in “Hajara ta d’au alwashin cewa Nuratu zata rayu ne a Gidanta Tamkar tana a GIDAN ARO wanda dik rintsi zata fice ta bar wann gidan sann auratayya bazai tab’a shiga tsakaninsu da mijinta ba muddin tana numfashi hakan yasa a ranan da za’a kai mahaifiyarka gidan Marwan a ranan Ta had’uda mummunan had’arin.. Nayi nadama Mu’azzam, nayi nadaman muggan abubuwan da muka aikata.. Ban yarda Hajara zata iya kashe mutum da hannayenta ba saida Ta sanar dani yanda ta mallaki takardun nan.. Hajara ta jima tana kishi da mahaifiyarka Tun kafin ta zamto matar Marwan.. Bata tab’a zaton mutuwar mahaifinka ba komai zai kara mata da Nuratu ba face kusanci...!” Kuka ya hanata ci gaba da magana.

Cikin rarrabewan kalamai yake furta “Mai kike so kice..? Matar nan tanada saka hannu a mutuwar mahaifina..?”

Hajiya Faty Ta k’asa amsawa sai girgiza kai take tana hawaye.

Tsawa ya kuma daka mata jijiyonsa suna kuma bayyana “Did she kill my father.. Answer me..!”

Kasa amsawa tai sai rawa da jikinta yake tana girgiza kai alamun bata sani ba.

Jinjina kai yake a hankali yana dubanta hawaye mai k’una na gangarowa daga idanunsa guda, yana jin k’afafunsa kaman zasu gaza d’aukansa “Zaki maimaita wann statement d’in a police headquarters. Zaki maimaita.!” Ya k’arashe yana kuma jinjina kansa yana furzar da iska a hankali.

Hajiya Faty tai saurin d’ago kai tana dubansa tana girgiza kai “Na shiga uku dan girman Allah ka rufa mun asiri Mu’azzam.. Dan Allah kar ka kaini police station wllhi idan Senator yaji Ina police station aurena mutuwa zai.. Wayyo Allah na shiga uku..”

“Da kin tuna haka kafin ki zab’i rayuwar da kika zab’arwa kanki..” Ya fad’i murya a dake, lokaci guda ya dubi Yansandan dake tsaye gefe yace su wuce da Hajiya Faty.

Hajiya Faty na kuka aka shige da ita motan Yansanda.

Mu’azzam yaci gaba da juya takardan cikin hannunsa ya sakin huci a hankali, lokaci guda maganganun Hajiya Faty na Yawo a dodo kunnuwansa, a haka ya nufi Mota cikin sassarfa. Fuskar Mommy ne kawai ke masa gizo cikin idanunsa.. Rayuwar da sukai a baya, soyayya da k’aunar da ta nuna masu shida ‘Yaruwarsa da mahaifiyarsu.. Tsawon lokacin da mahaifiyarsa ta d’auka kwance tana jinya da yanda Mommy ta nuna kulawa da sadaukarwa wajen yi mata jinya.. Tafiya kawai yake saman kwalta amma hotunan abubuwan da suka faru baya su suke dawo masa maganganun da dik wasu memories da suka faru Sune ke masa Yawo a dodon kunnuwansa, k’wayan idanunsa da kwanyarsa.. Fuskarsa ta rine ta koma ja haka nan idanunsa, hannayensa da ya damk’e steering wheel dasu kuwa kai kace zai b’alla steering d’in ne.. A haka take driving ba wai dan yanada tabbacin yanda k’arfin halin tuk’a motar ba sai dan yanada tabbacin muddin na numfashi Sai ya cimma wann matar.. Wann matar data tarwatsa masa rayuwa da na ahalinsa.. Tafiya kurum yake yana ganin kaman Hajara ce gabansa saman kwalta yana taketa da mota..

**

A can gidan Daddy kaw koda Mommy Ta tabbata Musaddiq bai cikin gidan a guje Ta fito kaman mahaukaciya tana tambayan Yansandan dake tsaron gidan Ina Musaddiq.. Sai kururuwa take masu tana fad’in ina D’anta ina suka kai mata D’a..

Muryar abokin Mu’azzam Assad Ta sinkayo yana fad’in “Nasan yanda D’anki yake..!”

Mommy ta juyo zuciyarta na bugawa tana duban Assad.

Lokaci guda Assad yaci gaba da takowa gaban Mommy hannayensa dafe saman belt d’insa yake ci gaba da furta “Kinsan Ina Musaddiq ya kwanan.. Musaddiq ya kwana ne a ofishinmu.. Sann yayi confessing laifin da ya aikata.. Idan Kina neman Musaddiq yana tsare a ofishinmu.”

Wani k’atutun abu ne Mommy taji ya taso tin daga k’irjinta har zuwa mak’oshinta yana k’ok’arin tokare mata numfashi.

Wani irin k’ara Mommy Ta saki tana fad’in K’arya Assad yake, D’anta ba D’anta’adda bane sai Sun fito mata da D’a.

Tayo kan sauran Yansandan tana ihu tana fad’in Su fito mata da D’a D’anta Bazai tafi gidan yari ba.

Ihun Mommy da hayaniyarta yasa su Daddy da Uncle Salman dake zaune gefen mahaifiyarsu wacce har lokacin a kwance take.. Take suka fitowa babu shiri suka nufo haraban gidan.

Kiki dake d’aki wajen Safeenah tana kula da Safeenar da halinda take ciki saurin rufe windows d’in tai hawaye na gangaro mata dan bataso Safeenah taji wani abinda zai kuma worsen situation d’inta.

Mommy ta nufo Daddy a guje tana fad’in “Our son is not a criminal Marwan.. He’s not a criminal.. He didn’t commit the crime.. You need to help our Son Marwan.. Ka cece d’anmu he can’t go to jail for something he’s never committed.. Dan Allah ka cece D’anmu Marwan.. Wayyo na shiga uku Musaddiq..!”

Daddy ya soma girgiza kai cikin rashin fahimta yana duban Mommy “Hajara what are you saying..? Ina Musaddiq d’in.. Wai meke faruwa..?! Kimin magana Hajara.!”

Kuka kurum Mommy take tana ci gaba da girgiza kai tana fad’in “He didn’t rape her.. Wllhi Allah bai aikata ba na shiga uku.. ‘Ya’yana Marwan.. Safeenah gidan mahaukata Musaddiq gidan yari.. Kan laifin da duka ba nasu bane.. Wayyo Musaddiq d’ina.. Wayyo na shiga uku..!”
Chapter 152 · 0% Book details