Sashe 109
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Koda ya gama wayan bai ce mata komai ba, ta saci kallonsa taga hankalinsa kacaukam naga tuk’a mota. Sai itama ta maida nata kan b’angarenta. Ta kuma jingina kanta tana kallan gari.
Har suka iso gida bai ce mata komai ba, dik sai taji jikinta yayi sanyi saikace ba shine ya gama cewa yayi kewarta ba ya wani k’i kulata yanata minding business d’insa. Tai k’wafa cikin zuciyarta.
Har dai Patrick ya k’araso yana musu sannu da zuwa welcome sir, welcome ma..” Still Mu’azzam bai kulata ba saima umartan Patrick da yake ya k’arasa da suitcase d’in nata k’ofar parlor.
Ko zarafin amsa Patrick dake gaisheta bata samu ba. Toh kardai fushi yai da ita.. Shin meye laifin dan tace ya barta ta kwana d’aya wajen Ummanta da ‘yanuwanta.. Kawai dai mai hali ne da bai fasawa amma itakam bataga wani abu cikin hakan ba.
Baibi takanta ba yai shigewarsa, tai k’wafa cikin zuciyarta tana jin zafin yanda yake ta wani basarwa yana shareta saikace ba yau ta dawo ba.. Dama k’ila babu wani missing d’inta da yai.. Da yayi kewarta bazai banza da ita haka ba. Ta K’araso parlorn jikinta dik a mace. D’ago kan da zatai taga gidan an canza masa tsari gaba d’aya. Kaf kayan dake cikin gidan an canza an zuba sabbi.. Taci gaba da takowa a hankali tana kallon tsarin gidan.. Gidan da tai zaton bazata kuma dawowa cikinsa ba. Gidan da tai masa lak’abi da GIDAN ARO. Zuciyarta ne ya yanke sanda ta tuna tangamemen hotonsa da Safeenah da ake soma hangowa idan ka nufi staircase. Ta d’ago idanu tana duban spot d’in da hoton yake.. K’irjinta ya kuma bugawa sakamakon ganin nasu hoton da tai.. Hoton da aka masu suna zaune a park farkon fitarsu mission da sukai tare. Ya matso da bakinsa kusan kennenta yana fad’a mata dik abinda suke acting ne cikin mission ne Ita kuma Ta saki murmushi wanda tasan yak’e ne kawai amma sai gashi a hoton baiyi kama da acting ba. Komai looks real kaman dai soyayya ce ta gaskiya. Ta saki murmushi a hankali still idanunta na kan hoton.
Juyowar da zatai ta gansa tsaye bayanta fuskarsa babu yabo babu fallasa. Sai ta d’an sha jinin jikinta ta sadda idanunta kad’an.
Ta soma takowa a hankali ta K’araso gaba gareshi. Still idanunta a k’asa take furta “Fushi kake dani.?”
Bai ce mata komai ba Sai dubanta da yake.
“I’m sorry.. Bansan maganar zai b’ata maka rai ba.. Kai hak’uri kaji..” Ta k’arashe muryarta na rawa kaman zatayi kuka.
D’an takowa yai ya matso dab da ita sosai kafin ya kamo hannayenta, ta d’ago idanunta kwantattun k’walla tab cikinsu tana dubansa. Murmushi ta hango saman fuskarsa wanda ba lallai ka fahimci hakan ba sai idan domin kai akayi.
Ya juyar da ita had’ida rungumarta ta baya ya d’aura hannayensa saman cikinta, su duka biyun suna fuskantar hoton nasu.
“Did you like my surprise..? Tsarin gidan ya miki..?” Ya tambaya yana rank’wafo da kansa kad’an zuwa wuyanta.
Mr Inspector kenan komai nasa burgeta yake. Wato bazai amsa mata ba saidai ya nuna mata a aikace. Ta lumshe idanunta kad’an kafin ta jinjina masa kai ba tareda Ta iya furta koda kalma ba.
Ya murmusa kafin yaci gaba da fad’in “Nan gidanki ne.. Everything here is yours.. Komai da komai dake cikin gidan naki ne.. Including me..” Ya k’arashe cikin wane irin siga mai kashe mata jiki.
Hawayen da suka jima mak’ale cikin idanunta suka gangaro.. Ba komai ta tuna ba face farkon zuwanta gidan da ya jaddada mata cewa gidan tamkar dai GIDAN ARO yake a wajenta wanda za’a iya sallamanta ko yaushe.. ta zauna cikin shiri sann kar ta baje kolinta dan ga duk mai hankali da hangen nesa ba’a baje koli a GIDAN ARO. Sannan dik abinda aka ce maka na aro ne akwai ranan da za’a karb’i wann abun. Hausawa sunce Kayan aro baya rufe katara.. Sann dik daren dad’ewa zaka mayar da abinda aka ara maka..
Juyo da ita yai suna fuskantar juna, ya saka yatsarsa guda yana goge mata hawayen dake gangaro mata.
“Baki son gidan ne.. Ko tsarin ne bai miki ba..?”
Ta Ware idanunta tana dubansa “Komai yayi mun... Thank you for this wonderful surprise.. But do you know something..” Ya tsareta da idanu, yayinda taci gaba da fad’in “Kaid’in kafi mun duk abinda ka zuba cikin gidan nan.. Soyayyarka da k’aunarka a gareni sun isheni..” Ta jinjina kai kad’an hawaye naci gaba da gangaro mata “A baya wad’ann k’yale k’yaleni sune mafarki na kuma sune burin Sadiya.. Nayi zaton Sune kad’ai suke haifar da soyayya.. Nayi zaton idan babu su babu wata kalma da ake kira So.. Saidai bayan had’uwata da kai na yarda akwai wann kalma da ake kira So koda babu k’yale k’yale na rayuwar duniya wacce za’a tafi a barta a nan duniya.. Ba kaman mutane guda biyu da suka rayu domin Allah suka so juna dan Allah.. A ranan k’iyama Allah ya tadasu tare.. Shin akwai soyayyar da tafi wann..?” Murmushi da hawaye gauraye saman fuskarta. Yayinda Mu’azzam ya k’ura mata idanu yana jin kalaman nata har cikin b’argo da tsokarsa.
Ta kuma murmusawa kafin taci gaba da fad’in “Akwai abubuwa da dama da Allah zai baka a duniyar nan kasan cewa ya gama maka arziki.. Kaman dai arziki na lafiya wacce babu arzikin da ya kaita bayan kaancewarka musulmi mai kad’aita Ubangiji.. Bayan naga Mamy da halin da ta tsinci kanta ciki na jarabawa Tabbas na yarda k’yale k’yale na duniya ba komai bane face rud’i ne na d’an wani lokaci da yake k’ayadadde.. Mafarki na ne a baya na kasance cikin daula da tarin arziki... Amma a halin yanzu na shafe wann mafarkin.. Kaine mafarki na.. Kuma kaine cikan burina Mr Inspector... Ina fata na rayu dakai a nan gidan Duniya wanda yake GIDAN ARO ne.. Sannan a rayuwa na gaba Ina fata Allah ya kuma tadani da kai k’ark’ashin Inuwa guda a gidan Gaskiya.. I love you so much my Detective..” Ta k’arashe tana mai rungumarsa.
Rungumeta yai yana mai lumshe idanunsa shid’inma siririyar Hawaye ta gangaro masa “I love you.. I love you more my Beautiful Stubborn head.” Ya k’arashe yana mai kuma matseta jikinsa.
Soyayya suka dinga nuna ma junansu wanda ya tabbatar masu cewa sud’in sunyi kewan juna sosai da sosai. Babu kaman Mu’azzam wanda har saida Sadiyar Ta tausaya masa taga wautanta da tace zata kwana gida bayan shafe kusan sati da yai baya tare da ita.
**
Coin d’in ya dinga juyawa yana tuna lokacin da yake k’arami cikin stuff d’in mahaifinsa ya sami exactly irin wann coin d’in wanda tsakiya an rubuta _Black African Team_ mai hakan yake nufi.. Ya akai ya sami exactly irin wann coin d’in a wajen Habeeb k’anin Sadiya..? Kodai su Danger ne suka yasar da Coin d’in a gidansu Sadiya Habeeb ya tsinta..? Toh kenan wann coin d’in ta iya yuwa nada alak’a da su Danger kenan..? Toh amma idan wann coin d’in nada alak’a dasu Danger ya akai ya sami irinta a cikin kayan mahaifinsa..? Gaba d’aya kansa ya k’ulle.. Anya coin d’in iri guda ne..? Babu abinda zai had’a mahaifinsa dasu Danger.. Ya dafe kansa kad’an kafin ya furta a fili “Su waye su Danger.?” Ya bama kansa amsa da fad’in “Sune mutanen da suka kashe mun k’anwa Ikram..” “Toh idan wann coin d’in nada alak’a da mutuwar Ikram kenan ta iya yuwa mutuwar mahaifinsa ba accident bane..? What if shiryawa akai..? What if su Danger Sun jima suna bibiyan ahalinsa..? What if mutuwar Daddynsa shiryayya ne..? Zuciyarsa yai wani irin yankewa. Ya shiga girgiza kai yana dafe kansa wanda gaba d’aya ya masa nauyi komai ya cunkushe masa. Tunanin yanda ya aje wancan coin d’in ya soma.. Ya zama dole yai comparing coins d’in ya tabbata idan sunada kamanceceniya. Da wann tinanin ya aje coin d’in gefen bedside ya janyo sadiya dake bacci zuwa cikin jikinsa, ya lumshe idanu yana shak’an k’anshinta mai sanyi wanda ya sauk’ar masa da natsuwa cikin zuciyarsa.
**
A can Fufore kaw Shemau k’arfe shad’aya na dare ta soma bugun k’ofar gidan k’awarta Baddo.
Da k’yar Baddo ta k’araso ta bud’e k’ofa cikeda tsoro dan dama mijinta baya nan yayi tafiya ga yanda duniyar ta zama kowa kaffa kaffa yake da rayuwarsa.
A razane Baddo take k’ok’arin tura k’ofa tana karanto addu’o’i dan Ta zaci mahaukaciya ce ko gamo tai cikin daren.
“Baddo nice Shemau dan Allah kar ki rufe k’ofar.. Ki ceceni Baddo banida yanda zanje. A cikin uku nake..!”
Baddo ta dafe k’irji tana duban Shemau cikeda tsoro dan bata ma ganeta ba saida Shemaun tai magana “Shemau kece haka..? Mai zan gani ni Baddo..”
Kuka Shemau Ta fashe mata dashi tana fad’in “Baddo ki taimakeni.. Wllhi cikin tara nake bama uku ba..”
Baddo ta shiga salallami tana tafe hannaye tana duban Shemau cikeda tsoron duniya..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*55*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Baddo ta canza position d’in taguminta yafi sau abinda yafi “Ni babu abu guda dana fahimta Shemau. Kinaso kice mun tin jiya da dare abin ya faru.. Toh a ina kika kwana..?”
Gajeren tsuka Shemau tai “Duk wann ba lallai kiji ba Baddo tinda Allah ya taimaka na wayi gari.. Da ace jiya kika ganni nayi imani Bazaki ganeni ba.”
Baddo tace “Yanzun ma da k’yar na ganeki wllhi saida kikai magana.” Ta ida maganar tana aje mata plate d’in indomie da ta dafa mata.
Shemau ta janyo plate d’in ta soma nad’an abincin hannu baka hannu k’warya.
Baddo ta rapka uban tagumi tai zaune gefe tana kallon Shemau matar Alhaji Salman Gamji yanda ta fice a hayyacinta cikin lokaci k’ank’ani. Ta gyara zama tana kuma canza position d’in taguminta “Wai ni mi ya faru dake ne.. Mai ya jefaki cikin wann ukun..?”
Shemau ta dubeta sai kuma tace “Safeenah ce ta jefani cikin wann bala’in.”
Baddo ta girgiza kai tace “Safeenah kuma..?”
Shemau ta janyo ledar pure water ta huda tana zuk’a saida ta shanye tas kafin ta dubi Baddo tace “Yo Safeenah Ta jazamin da na d’auki shawarinta..”
“Kika d’auki shawarinta kaman yaya..?”
Har suka iso gida bai ce mata komai ba, dik sai taji jikinta yayi sanyi saikace ba shine ya gama cewa yayi kewarta ba ya wani k’i kulata yanata minding business d’insa. Tai k’wafa cikin zuciyarta.
Har dai Patrick ya k’araso yana musu sannu da zuwa welcome sir, welcome ma..” Still Mu’azzam bai kulata ba saima umartan Patrick da yake ya k’arasa da suitcase d’in nata k’ofar parlor.
Ko zarafin amsa Patrick dake gaisheta bata samu ba. Toh kardai fushi yai da ita.. Shin meye laifin dan tace ya barta ta kwana d’aya wajen Ummanta da ‘yanuwanta.. Kawai dai mai hali ne da bai fasawa amma itakam bataga wani abu cikin hakan ba.
Baibi takanta ba yai shigewarsa, tai k’wafa cikin zuciyarta tana jin zafin yanda yake ta wani basarwa yana shareta saikace ba yau ta dawo ba.. Dama k’ila babu wani missing d’inta da yai.. Da yayi kewarta bazai banza da ita haka ba. Ta K’araso parlorn jikinta dik a mace. D’ago kan da zatai taga gidan an canza masa tsari gaba d’aya. Kaf kayan dake cikin gidan an canza an zuba sabbi.. Taci gaba da takowa a hankali tana kallon tsarin gidan.. Gidan da tai zaton bazata kuma dawowa cikinsa ba. Gidan da tai masa lak’abi da GIDAN ARO. Zuciyarta ne ya yanke sanda ta tuna tangamemen hotonsa da Safeenah da ake soma hangowa idan ka nufi staircase. Ta d’ago idanu tana duban spot d’in da hoton yake.. K’irjinta ya kuma bugawa sakamakon ganin nasu hoton da tai.. Hoton da aka masu suna zaune a park farkon fitarsu mission da sukai tare. Ya matso da bakinsa kusan kennenta yana fad’a mata dik abinda suke acting ne cikin mission ne Ita kuma Ta saki murmushi wanda tasan yak’e ne kawai amma sai gashi a hoton baiyi kama da acting ba. Komai looks real kaman dai soyayya ce ta gaskiya. Ta saki murmushi a hankali still idanunta na kan hoton.
Juyowar da zatai ta gansa tsaye bayanta fuskarsa babu yabo babu fallasa. Sai ta d’an sha jinin jikinta ta sadda idanunta kad’an.
Ta soma takowa a hankali ta K’araso gaba gareshi. Still idanunta a k’asa take furta “Fushi kake dani.?”
Bai ce mata komai ba Sai dubanta da yake.
“I’m sorry.. Bansan maganar zai b’ata maka rai ba.. Kai hak’uri kaji..” Ta k’arashe muryarta na rawa kaman zatayi kuka.
D’an takowa yai ya matso dab da ita sosai kafin ya kamo hannayenta, ta d’ago idanunta kwantattun k’walla tab cikinsu tana dubansa. Murmushi ta hango saman fuskarsa wanda ba lallai ka fahimci hakan ba sai idan domin kai akayi.
Ya juyar da ita had’ida rungumarta ta baya ya d’aura hannayensa saman cikinta, su duka biyun suna fuskantar hoton nasu.
“Did you like my surprise..? Tsarin gidan ya miki..?” Ya tambaya yana rank’wafo da kansa kad’an zuwa wuyanta.
Mr Inspector kenan komai nasa burgeta yake. Wato bazai amsa mata ba saidai ya nuna mata a aikace. Ta lumshe idanunta kad’an kafin ta jinjina masa kai ba tareda Ta iya furta koda kalma ba.
Ya murmusa kafin yaci gaba da fad’in “Nan gidanki ne.. Everything here is yours.. Komai da komai dake cikin gidan naki ne.. Including me..” Ya k’arashe cikin wane irin siga mai kashe mata jiki.
Hawayen da suka jima mak’ale cikin idanunta suka gangaro.. Ba komai ta tuna ba face farkon zuwanta gidan da ya jaddada mata cewa gidan tamkar dai GIDAN ARO yake a wajenta wanda za’a iya sallamanta ko yaushe.. ta zauna cikin shiri sann kar ta baje kolinta dan ga duk mai hankali da hangen nesa ba’a baje koli a GIDAN ARO. Sannan dik abinda aka ce maka na aro ne akwai ranan da za’a karb’i wann abun. Hausawa sunce Kayan aro baya rufe katara.. Sann dik daren dad’ewa zaka mayar da abinda aka ara maka..
Juyo da ita yai suna fuskantar juna, ya saka yatsarsa guda yana goge mata hawayen dake gangaro mata.
“Baki son gidan ne.. Ko tsarin ne bai miki ba..?”
Ta Ware idanunta tana dubansa “Komai yayi mun... Thank you for this wonderful surprise.. But do you know something..” Ya tsareta da idanu, yayinda taci gaba da fad’in “Kaid’in kafi mun duk abinda ka zuba cikin gidan nan.. Soyayyarka da k’aunarka a gareni sun isheni..” Ta jinjina kai kad’an hawaye naci gaba da gangaro mata “A baya wad’ann k’yale k’yaleni sune mafarki na kuma sune burin Sadiya.. Nayi zaton Sune kad’ai suke haifar da soyayya.. Nayi zaton idan babu su babu wata kalma da ake kira So.. Saidai bayan had’uwata da kai na yarda akwai wann kalma da ake kira So koda babu k’yale k’yale na rayuwar duniya wacce za’a tafi a barta a nan duniya.. Ba kaman mutane guda biyu da suka rayu domin Allah suka so juna dan Allah.. A ranan k’iyama Allah ya tadasu tare.. Shin akwai soyayyar da tafi wann..?” Murmushi da hawaye gauraye saman fuskarta. Yayinda Mu’azzam ya k’ura mata idanu yana jin kalaman nata har cikin b’argo da tsokarsa.
Ta kuma murmusawa kafin taci gaba da fad’in “Akwai abubuwa da dama da Allah zai baka a duniyar nan kasan cewa ya gama maka arziki.. Kaman dai arziki na lafiya wacce babu arzikin da ya kaita bayan kaancewarka musulmi mai kad’aita Ubangiji.. Bayan naga Mamy da halin da ta tsinci kanta ciki na jarabawa Tabbas na yarda k’yale k’yale na duniya ba komai bane face rud’i ne na d’an wani lokaci da yake k’ayadadde.. Mafarki na ne a baya na kasance cikin daula da tarin arziki... Amma a halin yanzu na shafe wann mafarkin.. Kaine mafarki na.. Kuma kaine cikan burina Mr Inspector... Ina fata na rayu dakai a nan gidan Duniya wanda yake GIDAN ARO ne.. Sannan a rayuwa na gaba Ina fata Allah ya kuma tadani da kai k’ark’ashin Inuwa guda a gidan Gaskiya.. I love you so much my Detective..” Ta k’arashe tana mai rungumarsa.
Rungumeta yai yana mai lumshe idanunsa shid’inma siririyar Hawaye ta gangaro masa “I love you.. I love you more my Beautiful Stubborn head.” Ya k’arashe yana mai kuma matseta jikinsa.
Soyayya suka dinga nuna ma junansu wanda ya tabbatar masu cewa sud’in sunyi kewan juna sosai da sosai. Babu kaman Mu’azzam wanda har saida Sadiyar Ta tausaya masa taga wautanta da tace zata kwana gida bayan shafe kusan sati da yai baya tare da ita.
**
Coin d’in ya dinga juyawa yana tuna lokacin da yake k’arami cikin stuff d’in mahaifinsa ya sami exactly irin wann coin d’in wanda tsakiya an rubuta _Black African Team_ mai hakan yake nufi.. Ya akai ya sami exactly irin wann coin d’in a wajen Habeeb k’anin Sadiya..? Kodai su Danger ne suka yasar da Coin d’in a gidansu Sadiya Habeeb ya tsinta..? Toh kenan wann coin d’in ta iya yuwa nada alak’a da su Danger kenan..? Toh amma idan wann coin d’in nada alak’a dasu Danger ya akai ya sami irinta a cikin kayan mahaifinsa..? Gaba d’aya kansa ya k’ulle.. Anya coin d’in iri guda ne..? Babu abinda zai had’a mahaifinsa dasu Danger.. Ya dafe kansa kad’an kafin ya furta a fili “Su waye su Danger.?” Ya bama kansa amsa da fad’in “Sune mutanen da suka kashe mun k’anwa Ikram..” “Toh idan wann coin d’in nada alak’a da mutuwar Ikram kenan ta iya yuwa mutuwar mahaifinsa ba accident bane..? What if shiryawa akai..? What if su Danger Sun jima suna bibiyan ahalinsa..? What if mutuwar Daddynsa shiryayya ne..? Zuciyarsa yai wani irin yankewa. Ya shiga girgiza kai yana dafe kansa wanda gaba d’aya ya masa nauyi komai ya cunkushe masa. Tunanin yanda ya aje wancan coin d’in ya soma.. Ya zama dole yai comparing coins d’in ya tabbata idan sunada kamanceceniya. Da wann tinanin ya aje coin d’in gefen bedside ya janyo sadiya dake bacci zuwa cikin jikinsa, ya lumshe idanu yana shak’an k’anshinta mai sanyi wanda ya sauk’ar masa da natsuwa cikin zuciyarsa.
**
A can Fufore kaw Shemau k’arfe shad’aya na dare ta soma bugun k’ofar gidan k’awarta Baddo.
Da k’yar Baddo ta k’araso ta bud’e k’ofa cikeda tsoro dan dama mijinta baya nan yayi tafiya ga yanda duniyar ta zama kowa kaffa kaffa yake da rayuwarsa.
A razane Baddo take k’ok’arin tura k’ofa tana karanto addu’o’i dan Ta zaci mahaukaciya ce ko gamo tai cikin daren.
“Baddo nice Shemau dan Allah kar ki rufe k’ofar.. Ki ceceni Baddo banida yanda zanje. A cikin uku nake..!”
Baddo ta dafe k’irji tana duban Shemau cikeda tsoro dan bata ma ganeta ba saida Shemaun tai magana “Shemau kece haka..? Mai zan gani ni Baddo..”
Kuka Shemau Ta fashe mata dashi tana fad’in “Baddo ki taimakeni.. Wllhi cikin tara nake bama uku ba..”
Baddo ta shiga salallami tana tafe hannaye tana duban Shemau cikeda tsoron duniya..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*55*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Baddo ta canza position d’in taguminta yafi sau abinda yafi “Ni babu abu guda dana fahimta Shemau. Kinaso kice mun tin jiya da dare abin ya faru.. Toh a ina kika kwana..?”
Gajeren tsuka Shemau tai “Duk wann ba lallai kiji ba Baddo tinda Allah ya taimaka na wayi gari.. Da ace jiya kika ganni nayi imani Bazaki ganeni ba.”
Baddo tace “Yanzun ma da k’yar na ganeki wllhi saida kikai magana.” Ta ida maganar tana aje mata plate d’in indomie da ta dafa mata.
Shemau ta janyo plate d’in ta soma nad’an abincin hannu baka hannu k’warya.
Baddo ta rapka uban tagumi tai zaune gefe tana kallon Shemau matar Alhaji Salman Gamji yanda ta fice a hayyacinta cikin lokaci k’ank’ani. Ta gyara zama tana kuma canza position d’in taguminta “Wai ni mi ya faru dake ne.. Mai ya jefaki cikin wann ukun..?”
Shemau ta dubeta sai kuma tace “Safeenah ce ta jefani cikin wann bala’in.”
Baddo ta girgiza kai tace “Safeenah kuma..?”
Shemau ta janyo ledar pure water ta huda tana zuk’a saida ta shanye tas kafin ta dubi Baddo tace “Yo Safeenah Ta jazamin da na d’auki shawarinta..”
“Kika d’auki shawarinta kaman yaya..?”