← Book details Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 112 OF 175

Sashe 112

Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mu’azzam kaw tuni security d’in ya hasko masa wann footage d’in. Tin daga parking lot har zuwa cikin asibitin. Aiko saiga Maleeka cikin shiga irinta ma’aikatan asibiti ta shige lab.. Jim kad’an ta fito ta shige wani store ta canza kayan jikinta fuskarta ya bayyana. Mu’azzam yace “Stop.. Zoom..”

Security d’in cikeda tsoro yai yanda Mu’azzam yace. Ana zooming saiga fuskar Maleeka ya fito b’aro b’aro..

Table d’in ya daka yana fad’in “I knew it.. My hunch was right about you Maleeka.. Believe me you’ll pay.. Zaki biya abinda kika aikatawa Abokina.!” Yana ida fad’in haka ya mik’e cikin sassarfa ya fito daga asibitin.

**

Yusuf yace daga d’aya b’angaren “I’m sorry for your loss.. Allah ya mata rahama.. Kina nan headquarters ne..?”

Maleeka ta girgiza kai kad’an tace “No na tafi gida ina shiryawa.. Zan tafi.. But before na tafi Ina so na fad’i gaskiya Yusuf.. Kana tare da Inspector Gamji ne..?”

Yusuf ya girgiza kai yace “Wane irin gaskiya..”

Maleeka tace gaskiyar abinda na sani gaba d’aya akan case d’in Officer Assad.. I’ll confess Yusuf.. Zan fad’i komai.. I’m ready to accept my punishment..” muryarta ya soma rawa alamun kuka sanda taci gaba da fad’in “Ku yafe mun team.. Ku yafe mun.. Naci amanarku.. Na yaudareku.. Naci amanan k’asata.. Na wulak’anta aikina.. Nid’in babbar mai laifi ce.. Dan Allah Yusuf ka rok’armun Assad gafara.. Kace masa ya yafe mun.. Nayi komai ne to save my ailing mother.. But at the end dik abinda nai bai hanata mutuwa ba.. Dan Allah kace ya yafe mun.. Ka fad’a ma Inspector Gamji I’m ready to confess.. Kuzo gidana na baku statement d’ina dan nasan idan na fice kuraye zasu iya farauta na..”

Yusuf yana waya da Maleeka Mu’azzam yana tafe cikin Mota yana kiran layin Yusuf d’in. Nan Yusuf yake ganin wayar Mu’azzam na shigo masa. Yai saurin jinjina kai kafin yace da Maleeka “Kinaji.. Don’t go anywhere Maleeka.. Zamu taho yanzu.!” D’if Yusuf ya katse kiran ya d’aga na Mu’azzam.

Kaman jira Mu’azzam yake ya soma magana cikin sauri “Yusuf na kamo b’eran.. My hunch was right about that girl.. Itace mai mana zagon k’asa.. Yusuf make sure baka barta ta fice ba.. Gani nan Ina tafe na nufo headquarters.”

Yusuf ya sanar da Mu’azzam duk yanda sukai da Maleeka. Take yace ya turo masa address d’in gidan Maleekan sai su had’u a can d’in. Yana kashe wayar kuwa sak’on ya shigo wayarsa Yusuf ya turo masa address d’in gidan Maleeka. Sai sauri yake yana fuzgan mota yana ganin kaman bazai isa ba.

**

Tana kwance Sun ida waya da Inne kenan ta soma jiyo hayaniya daga gate. Tai saurin mik’ewa zaune tana jin hayaniyar na k’ara yawa. Babu shiri ta mik’e ta nufi upstairs ta zira doguwar riga a jikinta had’ida tura sumarta cikin hula. Sauri sauri ta sauk’o k’asa ta bud’e k’ofar parlorn tana hangen abinda ke faruwa. Tuni Safeenah ta bangaje Patrick tana fad’in shi bai isa ya hanata shiga gidanta ba. Ko Boss d’in nasa ne bai isa ya mata iyaka da wann gidan ba.. Gidanta ne da sunanta aka gina bataga mahaluk’in da yakai ya mata iyaka da wann gidan ba. Ta nufo cikin gidan tana huci Patrick na biye da ita yana rok’onta tazo ta fice abinda takeyi na iya shafan aikinsa.

Sadiya kaw tana hangosu Ta maida k’ofa ta rufe tai zamanta.

Safeenah na k’arasowa ta shiga bugun k’ofar tana fad’in “Munafuka kizo ki bud’e mana.. Da kika ganni shine kika shige kika b’uya.. K’aramar maras kunya.. Kinyi sa’a wancan karon harsashin bai sameki ba.. Ki bar murna dan kin tsallake tuggun da na had’a miki.. Idan sunana Safeenah Gamji wllhi sai kin bar gidan nan.. Gidan nan nawa ne, mai gidan shima nawa ne ke Kinyi kad’an to come between us nida my Halal.. Kizo ki bud’e nace.!” Ta k’arashe tana mai waige waige tana neman abinda zata daki glass d’in window dashi.. Bata sami komai ba ta cire dogon talakalmin dake k’affunta.. Ta shiga bugun glass d’in window da tsinin takalminta “Zan shigo na taddaki na fitar dake daga cikin gidan da k’arfi.. Come out now.. Ki fito nace..!” Tanayi tana dukan glass da tsinin talkalminta.

Idan Patrick ya nufota tayo kansa da takalmin nata tana fad’in sai ta rapza masa.

Ana haka Sadiya ta bud’e k’ofar. Patrick ya k’araso da sauri yana fad’in “Ma’am Maiyasa kika bud’e k’ofar gashi nan ina kiran Oga amma baya d’agawa.. But I think I’ll just call the cops..”

Safeenah tace “Go ahead and call them.. Ka kirasu nida kai sai muga waye za’a tafi dashi.”

Sadiya ta dubi Patrick tace “K’yaleta Patrick. Jeka abinka I can handle her.”

But yace “But Ma’am wann fah ba mai lafiya bace.. What if Ta miki wani abun..?”

“Uwarka ce batada lafiya..” Safeenah ta basa amsa da fad’in haka.

Patrick yace “Ma’am kinaji koh.”

Sadiya ta jinjina kai tace “Naji Patrick.. Ni kam Karnukan nan yai ka fita dasu morning exercise.?”

Patrick ya girgiza kai yace “A’a Ma’am tun jiya baa fita dasu ba.”

Ta jinjina kai tace “Ka bud’esu susha iska zasu buk’aci hakan..” Tana ida fad’in haka ta maida k’ofa ta rufe.

Safeenah ta shiga tura k’ofar tana fad’in ta bud’e mata. Patrick kaw tuni ya shige bud’e Karnuka.

Safeenah sai kururuwa take tana fad’in Sadiya ta bud’e mata k’ofa.. Ganin bazata bud’e ba ga Karnuka Patrick na shirin kwance su babu shiri Safeenah ta rik’o takalamanta a hannu ta nufi gate a guje tana kuma tsinema Sadiya.

Ta window Sadiya ke lek’en gudun Safeenah sai dariya take har Safeenar ta fice tattare da rigarta takalma a hannu.

Patrick ma dariya ya dingayi yana fad’in lallai Ma’am ta basa satan amsa wann mahaukaciyar tana zuwa nan gaba abinda zai mata kenan ya k’yaleta Ta shiga ya kwance mata Karnuka tinda tana tsoronsu.

**

Maleeka tai zaune a parlor sai murza tafin hannunta take tana jin zuciyarta na wane irin tsinkewa, tasan abinda take k’ok’arin yi abu ne mai matuk’ar had’ari amma nata da wani zab’in da ya shige ta fad’i gaskiya koda za’ayi arresting d’inta ne.. Ji tai bazata iya tafiya da hakkin kowa ba ba tareda ta sanar dasu gaskiyar Al’amari ba. Tana nan zaune tana aikin tunani taji ana knocking daga k’ofa. Ta mik’e tsaye tana tinanin su Mu’azzam ne suka iso.. Batai wata wata ba ta bud’e k’ofar.. Saidai tuni tai wani irin Daskarewa ganin ba Mu’azzam bane ba Yusuf bane.. Wani mutumi ne sanye da bak’ak’en tufafi ya rufe fuskarsa da bak’in mask. Bata iya ganin komai na jikinsa. Take ya soma nunata da k’aramar bindigarsa irin wacce sam ko anyi harbi da ita bazakaji sautin harbinba.

Ta soma jada baya tana fad’in “Please don’t kill me.. Dan Allah kar ka kasheni..” Tana maganar tana k’ok’arin k’arasawa yanda makaminta yake. Mutumin da yake all in black na kuma nufota.. Baka ganin komai nasa sanye yake cikin bak’aken tufafi fuskarsa rufe da bak’ar mask hannayensa rufe cikin bak’ak’en black hand gloves.

Abinka da wacce tasha training itama tsalle tai cikin k’warewa ta naushi hannun mutumin bindigar ya fad’i.. Take mutumin suka soma fad’a da Maleeka. Dukansu biyun cikin k’warewa suke attacking juna. Kai da gani kasan fad’an wad’anda suka sha training ne. Take Maleeka ta soma kokawan yaye hular mask d’in dake kan mutumin yana k’ok’arin hana faruwar hakan.

Maleeka bata gajiya ba taci gaba da kokawan zame hular tana fad’in “Who are you.. Just show yourself.. You coward.. Jaja ne ya turoka ko.. Toh zan kashe ka na kuma kai masa gawarka.. Asirinku ya tonu.!” Ta k’arashe tana mai funcuke hular fuskar mutumin ya bayyana..

Cikin tsananin shock Maleeka ke jada baya.. Ta shiga nunasa da yatsanta dake tsananin rawa tana fad’in “You..you..!!”

Su duka biyun suka tsaya suna duban juna. Maleeka na nunasa cikin tsananin rawar jiki yayinda mutumin yai tsalle ya d’auki bindigar. Aiko nan Maleeka tayo tsalle ta fad’o kansa itama tana kokawan k’wace bindigar.. A haka bindigar na tsakaninsu kowa na kokawar k’wacewa cikinsu.. Tau.! Harsashi ya tashi. Zasu iya cewa basusan waye harsashin ta d’ana ba cikin su biyun dan bindigar a tsakaninsu take. Maleeka takai dubanta zuwaga cikinta yanda harsashin ya sameta. A hankali take duk’awa saman gwiwoyinta har ta isa k’asa tana dafe da cikinta yanda ya harbeta jini na zubowa.

Ta d’ago a galabaice tana dubansa. Take ya k’ara mata harsashi guda. Kan kace mai Maleeka ta zube tana fidda numfashi da k’yar.

Ba tareda ya bar wani trace ba yai gaggawan ficewa daga wajen abinka da k’wararre.

Mu’azzam sai sauri yake yana kuma kiran layin Yusuf. Yusuf d’in ma nan ya sanar dashi ya kusan isa holdup ne ya rik’es.

Kusan tare tare Yusuf da Mu’azzam suka iso gidan. Gidan babu kowa da shike duk ma’aikata ne duk sun tafi aiki.. A bud’e suka sami k’ofa, suka dubi juna kafin suka k’arasa cikin gidan sauri sauri.

Kwance suka hangi Maleeka cikin jini ta gama galabaita tana bud’e idanu da k’yar.. Yusuf bai k’arasa kanta ba sai Mu’azzam da ya isa cikin sauri yana ambato sunanta.

Girgiza kai take tana dubansa... Tana so Tai magana ta kasa sabida ta gama jigata gab take da amsa kiran mahaliccinta “B..! BA.!! BA.. You...You....” Kalman da ta iya fad’i kenan cikin rarrabewar harrufa a hankali idanunta suka rufe.. Tana kwance cikin jini...

Yusuf ya k’araso yana dubanta sai kuma ya girgiza kai yana duban Mu’azzam “I think she’s gone..” Ya fad’i daga nan yanda yake duk’e.

Mu’azzam ya dafe kansa had’ida shafe fuskarsa da tafukan hannayensa. Ya lumshe idanunsa a hankali. Take Yusuf ya mik’e yana fad’in “Zan kira backup.”

Mu’azzam bai iya furta komai ba, Sai duban Maleeka da yake. Yasan zai matuk’ar wahala su bar Maleeka a raye tinda yasan yanda Al’amara ke gudana a wajensu.

Allah ya wanke Assad ya kuma kub’utar dashi. Saidai kuma Maleeka ta tafi bayan taso tayi abinda ya kamata a k’urarren lokaci.

Yusuf ya dubesa sanda aka kewaye gawan Maleeka da igiya ana ana d’aukan bayanai.

Yusuf ya k’urawa gawan Maleeka da ake bincike akai idanu. A fili yake furta “She was ready to confess.. Tayi nadama.. Taso ta bayyana gaskiya.. But unfortunately sun kasheta. Basu bata dama ta fad’i abinda ta sani ba.”
Chapter 112 · 0% Book details