Sashe 71
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daddy ya jinjina kai yace “Naji sa’insan da kukai dashi.. Ka masa rashin kunya cewa ko ba dad’e ko jima sai ka karb’e position d’insa.. I was in his office that day, we were to inspect the factory together dan har mun saka rigunan leda irin wanda ake sakawa idan za’a shiga inspection.. Da naji tattaunawarku sai na fasa shiga inspection d’in nai niyyan komawa gida domin na samu Inne mu tattauna batun had’in kan ahalinmu dan tinda Baffah ya rasu kake rashin kunya wa Hamma.. Baka ganinsa da gashin ido ka kafa idanunka akan matsayin da yake rik’e dashi.. Na fito na barku a cikin Factory.. Koda na dawo gida labarin mutuwar Hamma ya riskemu cewa he was stuck in a cold room... I didn’t want to suspect you Salman because you are our brother.. Na aje wannan a cikin zuciyata ban sanar da kowa ba sabida banaso na raba kan ahalinmu ko na lalata zumuntar mu, sannan banaso bak’in ciki ya kashe mahaifiyarmu mu kuma rasa ahali... Nayi zaton idan ka samu abinda kake so Wato Company zaka rabu da Ahalin Hamma ka cire ido akan Kaso na dukiyar Mu’azzam.. But still ka d’auki tsana ka d’aura akan Mu’azzam kaman dai ba ciki guda kuka fito da Mahaifinsa ba.. Na zab’i na adana masu dukiyarsu sabida D’anuwa irinka Salman.. Shin ka zaci na rayu da wannan abun cikin zuciyata abu ne mai sauk’i..?!” Daddy ya k’arashe yana girgiza kai hawaye na gangaro masa.
Uncle Salman murmusawa yai kafin yace “Is this how you welcome a guest, Dear Brother..?” Ya kuma murmusawa kafin yace “Matsalar shine baka da wata shaida da zata nuna cewa ni na kashe Yaya.. Quite alright na fad’i duk abubuwan da kace nace amma abinda bazan tab’a yarda na aikata ba shine kisan Yaya.. Ban kashsa ba lokacin sa ne yayi kuma shiyasa ya mak’ale a d’akin K’ank’ara..”
Daddy ya jinjina kai kafin yace “What if baka aikata ba amma maganganun da ka fad’a masa sun janyo ya yanki jiki ya fad’i a cikin d’akin K’ank’ara hardai ya mutu ba’asan yana ciki ba.. What if wann maganganun Naka sune silar mutuwarsa shin kana tunanin alhakin mutuwarsa baya wuyanka..?”
Uncle Salman ya kuma murmusawa kafin yace “Ko mai zakace bazan tab’a amsa laifin da ban aikata ba.. Sannan zaka iya fad’awa D’ansa after all shi jami’in tsaro ne.. Sai yai bincike kan mutuwar mahaifinsa wanda baiyi a baya, kaga yazo masa da sauk’i Sai ya had’a binciken tareda na ‘Yaruwarsa.. Zan d’auke matata mu tafi da alama ba’a maraba damu a gidan nan..!” Yana ida fad’in haka yasa kai fuuu ya fice ya nufi cikin gidan shashen Mamy yana dokawa Shemau kira.
Musaddiq ya fito daga mab’oyarsa yana jin gumi na kuma keto masa.. Meke shirin faruwa da ahalinsu.. Menene wannan daga wannan sai wancan..? Mai hakan yake nufi..? Kaman dai ahalin nasu mummunan baki na binsu.. Bacin haka meke shirin faruwa dasu..? Idan har Uncle Salman yanada saka hannu a mutuwar Uncle namesake (Kaman yanda yake kiran Baban Mu’azzam dan sunansa Musaddiq yaci) Toh kuwa ya kamata Mu’azzam ya sani.. Idan har za’a binciki Safeenah Maiyasa baza’a binciki Uncle Salman ba.. Da wannan tinanin ya shigo ya tadda Daddy ya had’a tagumi da hannayensa duka biyu.
Musaddiq ya k’araso ya zauna kusan k’afan Daddy, ya kifa kansa hawaye na gangaro masa. Lokaci guda yake furta “I heard everything Daddy.. Shin abinda ka fad’i kan Uncle Salman gaskiya ne..?”
Daddy ya shafi fuskarsa da duka tafukan hannayensa yana mai fuzar da fuci “Musaddiq you didn’t hear anything..!” Daddy yace yana duban Musaddiq d’in.
Musaddiq ya girgiza kai cikin rashin yarda kafin yace “Daddy that was a serious accusation, you know.. Tuhumar Uncle Salman fah kake da alhakin mutuwar Uncle namesake.. Daddy idan da gaske ne duk abubuwan da ka fad’i mai yasa bazaka bari a binciki Uncle Salman ba.. Karfa ka mance Daddy kai ka bada go ahead a tafi Safeenah a binciketa, tana a matsayin ‘yar cikinka.. Mai yasa zaka kare D’anuwanka idan har bazaka kare ‘yarka ba.. Daddy idan Uncle Salman shi yai sanadiyar mutuwar Uncle namesake then Mu’azzam needs to know..”
“No Musaddiq..! Koda wasa.. Kar ka kuskura ka sanar da Mu’azzam.. Ko wani cikin ahalinmu idan har kana so ahalin nan yaci gaba da zama a dunk’ule waje guda...!”Daddy yace cikeda gargad’i.
Musaddiq ya girgiza kai yace “But Daddy..”
Daddy ya kuma katsesa “Kana so ka tarwatsa zuciyar Mu’azzam..?”
Musaddiq ya girgiza kai a hankali kansa duk’e hawaye na gangaro masa.
Daddy ya jinjina kai kafin yace “Kana so ka tarwatsa Zuciyar Inne..?”
Nan ma girgiza kai Musaddiq yai alamun a’a.
Daddy yaci gaba da fad’in “Do you think it’s easy for me to live with this..? Musaddiq baka tunanin Mu’azzam ya shiga k’unci da tashin hankali masu yawa.. Ya rasa mahaifinsa tin yanada k’anan shekaru.. Mahaifiyarsa Ta gamu da tsananin jinya wanda tana nan ne tamkar ga babu.. Ya rasa k’anwarsa wacce akai Garkuwa da ita aka kuma kasheta.. Yana tsaka da bincike matarsa da akai niyyan sacewa tun a fari ta zamto prime suspect.. Allah ya rufa asiri ya wanketa da shike batada laifi.. Kwatsam yanzu sai a sanar dashi wannan batu..? Kai ma Kanka adalci kaima D’anuwanka Mu’azzam adalci shin ya cancanci a sanar dashi sa’insan da Uncle d’insa yai da mahaifinsa kafin ya bar duniya..?”
Musaddiq kuka yake sosai yana girgiza kai ba tareda ya iya furta komai ba.
Daddy ya jinjina kai yace “Idan har kana k’aunar Mu’azzam a matsayin D’anuwa bazaka sanar dashi duk abinda kaji yau ba.. Sannan bazaka sanar da kowa ba.. Kamin alk’awari Musaddiq..”
D’ago idanunsa masu zuban hawaye yai yana duban Daddy kafin ya mik’e k’unshe da bakinsa ya fice wani kukan na zuwa masa.
**
Babu abinda suka tadda a wannan location d’in Sai kangon gini da wasu dangin karyayyun kujeru. Mu’azzam ya shafi sumarsa zuwa fuskarsa yana fuzar da fuci.
Assad ma dafe kunkuminsa yai yana girgiza kai bayan sun gama searching entire location d’in “Mu’azzam stop being stubborn, let’s inform our team members about this..” Assad yace yana duban Mu’azzam d’in.
Da wutsiyar idanu yake duban Assad kafin ya girgiza kai yace “No I think we should inform the entire FCID.” Ya basa amsa da fad’in haka Kafin ya kifa kansa jikin garu. Lokaci guda ya d’ago yana duban Assad d’in. Fuci ya kuma fuzarwa yana shafe fuskarsa da duka hannayensa biyu “She’s so stubborn you know.. Na gargad’eta cewa kar Ta fita ko k’ofa amma saida ta fita.. Yanzu ga irinta nan.. D’aniskan nan ya d’auketa..!”
Assad yace “Ka kwantar da hankalinka Mu’azzam.. Babu abinda zai sameta and you ain’t gonna lose her..”
Da mamaki yake duban Assad jin kalamansa na k’arshe. A hankali ya girgiza kansa kafin yace “I’m only doing my job as a police officer. And I’ll make sure na cire mata stubbornness d’in dake kanta..” Ya fad’i yana murza tafin hannunsa a hankali.
Assad ya jinjina kai a hankali kafin yace “Yanzu Meye abinyi..?”
Duban Assad yai without uttering a word.. Lokaci guda ya d’an girgiza kai yasa kai zai shige saiji yai kaman yai tuntub’e da wani abu. Dakatawa yai ya kuma haska abun da ya taka da hasken wayarsa.
Hular sanyi ce yai tuntub’e da ita.. Ya duk’a a hankali yana kuma haska hular sanyin.. Assad ma ya duk’a yana duban abinda Mu’azzam d’in yake duba.
K’aramar Karan dake gefe Mu’azzam ya d’auka ya d’an tura hular dashi, hular ta bud’u sosai.. Bak’ar hula ce irinta sanyi gaban hular an rubuta B.A.T da manyan harrufa.. Mu’azzam yai shiru yana duban hular yayinda Assad ya zuba masa idanu ganin yanda yake examining hular da idanunsa.
“Assad nasan mai irin hular nan exactly..”
Assad ya dubesa da mamaki kafin yace “Could it be hular Sadiya..?”
Girgiza kai Mu’azzam yai kafin yace “Wait.” Ya shiga whatsapp account d’insa ya bud’e hoton dake display picture d’in Musaddiq, hoton su ne shida Musaddiq d’in da suka d’auka a cikin k’ank’ara a k’asar England ko wannesu yayi shiga irinta sanyi. Hular dake kan Musaddiq babu abinda ya rabata da wannan hular da suka tsinta a warehouse d’in da Danger ke business d’in drugs d’insa.
Zuciyar Mu’azzam yai wani irin yankewa. Assad ya dubi Musaddiq da hular sanyin dake kansa ya kuma duban hular da suka tsinta nan gabansu.
“What is this Assad.. Shin wannan zai iya zama hular Musaddiq ne..? Shin Musaddiq nada connection da Danger ne..? But how..?!” Ya k’arashe cikin tsananin rud’ani.
Assad ya girgiza kai yace “Mu’azzam wannan hula ce kawai, ba lallai ta zama na Musaddiq ba.. Mutane da yawa company guda d’aya.. Ta iya yuwa hular wani ne..”
Har lokacin duban hular yake kafin ya saka karan ya d’an bud’e cikin hular ya kunna hasken wayarsa yana haska cikin hular sosai, nan yaga alamun tsillin gashi cikin hular.
Ya d’ago ya dubi Assad kafin yace “I have an idea.. Ga alamun gashi cikin hular.. We will conduct a DNA test.. If it matches with Musaddiq kenan hular na Musaddiq ne.. And that means Musaddiq nada connection da Danger.”
Assad ya d’anyi shiru kafin yace “Toh amma wane connection Musaddiq zai samu da Danger..?”
Mu’azzam ya d’an gyara tsugunonsa kafin yace “Ka mance Musaddiq used to be a drug addict. Danger kuma drugs yake saida wa matasa.. Ka mance musabbabin zuwanmu wajen nan d’aya daga cikin customers d’in Danger shi ya bamu location d’in nan.. What if Musaddiq customer d’in Danger ne..?” Ya k’arashe cikin wane irin yanayi.
Assad ya shafi fuskarsa cikin rashin sanin mai zai furta.
Mu’azzam d’in ma zuba ma hular idanu yai cikin tsananin sanyin jiki. Muryarsa na rawa yake furta “Meke faruwa dani da ahalina Assad.. First Safeenah ce yanzu kuma Musaddiq.. Assad mai hakan ke nufi.. Assad I’m lost.. I .. I don’t know what to do or what to think... Shin wannan duka na cikin wasannin Danger ne..?”
Dafasa Assad yai kafin yace “We are still not sure idan hular nan ta Musaddiq ce Mu’azzam.. Ka kwantar da hankalinka zamuyi DNA test kuma zaka gani hular nan bata Musaddiq bace kawai kamanceceniya sukai kaji koh..”
Uncle Salman murmusawa yai kafin yace “Is this how you welcome a guest, Dear Brother..?” Ya kuma murmusawa kafin yace “Matsalar shine baka da wata shaida da zata nuna cewa ni na kashe Yaya.. Quite alright na fad’i duk abubuwan da kace nace amma abinda bazan tab’a yarda na aikata ba shine kisan Yaya.. Ban kashsa ba lokacin sa ne yayi kuma shiyasa ya mak’ale a d’akin K’ank’ara..”
Daddy ya jinjina kai kafin yace “What if baka aikata ba amma maganganun da ka fad’a masa sun janyo ya yanki jiki ya fad’i a cikin d’akin K’ank’ara hardai ya mutu ba’asan yana ciki ba.. What if wann maganganun Naka sune silar mutuwarsa shin kana tunanin alhakin mutuwarsa baya wuyanka..?”
Uncle Salman ya kuma murmusawa kafin yace “Ko mai zakace bazan tab’a amsa laifin da ban aikata ba.. Sannan zaka iya fad’awa D’ansa after all shi jami’in tsaro ne.. Sai yai bincike kan mutuwar mahaifinsa wanda baiyi a baya, kaga yazo masa da sauk’i Sai ya had’a binciken tareda na ‘Yaruwarsa.. Zan d’auke matata mu tafi da alama ba’a maraba damu a gidan nan..!” Yana ida fad’in haka yasa kai fuuu ya fice ya nufi cikin gidan shashen Mamy yana dokawa Shemau kira.
Musaddiq ya fito daga mab’oyarsa yana jin gumi na kuma keto masa.. Meke shirin faruwa da ahalinsu.. Menene wannan daga wannan sai wancan..? Mai hakan yake nufi..? Kaman dai ahalin nasu mummunan baki na binsu.. Bacin haka meke shirin faruwa dasu..? Idan har Uncle Salman yanada saka hannu a mutuwar Uncle namesake (Kaman yanda yake kiran Baban Mu’azzam dan sunansa Musaddiq yaci) Toh kuwa ya kamata Mu’azzam ya sani.. Idan har za’a binciki Safeenah Maiyasa baza’a binciki Uncle Salman ba.. Da wannan tinanin ya shigo ya tadda Daddy ya had’a tagumi da hannayensa duka biyu.
Musaddiq ya k’araso ya zauna kusan k’afan Daddy, ya kifa kansa hawaye na gangaro masa. Lokaci guda yake furta “I heard everything Daddy.. Shin abinda ka fad’i kan Uncle Salman gaskiya ne..?”
Daddy ya shafi fuskarsa da duka tafukan hannayensa yana mai fuzar da fuci “Musaddiq you didn’t hear anything..!” Daddy yace yana duban Musaddiq d’in.
Musaddiq ya girgiza kai cikin rashin yarda kafin yace “Daddy that was a serious accusation, you know.. Tuhumar Uncle Salman fah kake da alhakin mutuwar Uncle namesake.. Daddy idan da gaske ne duk abubuwan da ka fad’i mai yasa bazaka bari a binciki Uncle Salman ba.. Karfa ka mance Daddy kai ka bada go ahead a tafi Safeenah a binciketa, tana a matsayin ‘yar cikinka.. Mai yasa zaka kare D’anuwanka idan har bazaka kare ‘yarka ba.. Daddy idan Uncle Salman shi yai sanadiyar mutuwar Uncle namesake then Mu’azzam needs to know..”
“No Musaddiq..! Koda wasa.. Kar ka kuskura ka sanar da Mu’azzam.. Ko wani cikin ahalinmu idan har kana so ahalin nan yaci gaba da zama a dunk’ule waje guda...!”Daddy yace cikeda gargad’i.
Musaddiq ya girgiza kai yace “But Daddy..”
Daddy ya kuma katsesa “Kana so ka tarwatsa zuciyar Mu’azzam..?”
Musaddiq ya girgiza kai a hankali kansa duk’e hawaye na gangaro masa.
Daddy ya jinjina kai kafin yace “Kana so ka tarwatsa Zuciyar Inne..?”
Nan ma girgiza kai Musaddiq yai alamun a’a.
Daddy yaci gaba da fad’in “Do you think it’s easy for me to live with this..? Musaddiq baka tunanin Mu’azzam ya shiga k’unci da tashin hankali masu yawa.. Ya rasa mahaifinsa tin yanada k’anan shekaru.. Mahaifiyarsa Ta gamu da tsananin jinya wanda tana nan ne tamkar ga babu.. Ya rasa k’anwarsa wacce akai Garkuwa da ita aka kuma kasheta.. Yana tsaka da bincike matarsa da akai niyyan sacewa tun a fari ta zamto prime suspect.. Allah ya rufa asiri ya wanketa da shike batada laifi.. Kwatsam yanzu sai a sanar dashi wannan batu..? Kai ma Kanka adalci kaima D’anuwanka Mu’azzam adalci shin ya cancanci a sanar dashi sa’insan da Uncle d’insa yai da mahaifinsa kafin ya bar duniya..?”
Musaddiq kuka yake sosai yana girgiza kai ba tareda ya iya furta komai ba.
Daddy ya jinjina kai yace “Idan har kana k’aunar Mu’azzam a matsayin D’anuwa bazaka sanar dashi duk abinda kaji yau ba.. Sannan bazaka sanar da kowa ba.. Kamin alk’awari Musaddiq..”
D’ago idanunsa masu zuban hawaye yai yana duban Daddy kafin ya mik’e k’unshe da bakinsa ya fice wani kukan na zuwa masa.
**
Babu abinda suka tadda a wannan location d’in Sai kangon gini da wasu dangin karyayyun kujeru. Mu’azzam ya shafi sumarsa zuwa fuskarsa yana fuzar da fuci.
Assad ma dafe kunkuminsa yai yana girgiza kai bayan sun gama searching entire location d’in “Mu’azzam stop being stubborn, let’s inform our team members about this..” Assad yace yana duban Mu’azzam d’in.
Da wutsiyar idanu yake duban Assad kafin ya girgiza kai yace “No I think we should inform the entire FCID.” Ya basa amsa da fad’in haka Kafin ya kifa kansa jikin garu. Lokaci guda ya d’ago yana duban Assad d’in. Fuci ya kuma fuzarwa yana shafe fuskarsa da duka hannayensa biyu “She’s so stubborn you know.. Na gargad’eta cewa kar Ta fita ko k’ofa amma saida ta fita.. Yanzu ga irinta nan.. D’aniskan nan ya d’auketa..!”
Assad yace “Ka kwantar da hankalinka Mu’azzam.. Babu abinda zai sameta and you ain’t gonna lose her..”
Da mamaki yake duban Assad jin kalamansa na k’arshe. A hankali ya girgiza kansa kafin yace “I’m only doing my job as a police officer. And I’ll make sure na cire mata stubbornness d’in dake kanta..” Ya fad’i yana murza tafin hannunsa a hankali.
Assad ya jinjina kai a hankali kafin yace “Yanzu Meye abinyi..?”
Duban Assad yai without uttering a word.. Lokaci guda ya d’an girgiza kai yasa kai zai shige saiji yai kaman yai tuntub’e da wani abu. Dakatawa yai ya kuma haska abun da ya taka da hasken wayarsa.
Hular sanyi ce yai tuntub’e da ita.. Ya duk’a a hankali yana kuma haska hular sanyin.. Assad ma ya duk’a yana duban abinda Mu’azzam d’in yake duba.
K’aramar Karan dake gefe Mu’azzam ya d’auka ya d’an tura hular dashi, hular ta bud’u sosai.. Bak’ar hula ce irinta sanyi gaban hular an rubuta B.A.T da manyan harrufa.. Mu’azzam yai shiru yana duban hular yayinda Assad ya zuba masa idanu ganin yanda yake examining hular da idanunsa.
“Assad nasan mai irin hular nan exactly..”
Assad ya dubesa da mamaki kafin yace “Could it be hular Sadiya..?”
Girgiza kai Mu’azzam yai kafin yace “Wait.” Ya shiga whatsapp account d’insa ya bud’e hoton dake display picture d’in Musaddiq, hoton su ne shida Musaddiq d’in da suka d’auka a cikin k’ank’ara a k’asar England ko wannesu yayi shiga irinta sanyi. Hular dake kan Musaddiq babu abinda ya rabata da wannan hular da suka tsinta a warehouse d’in da Danger ke business d’in drugs d’insa.
Zuciyar Mu’azzam yai wani irin yankewa. Assad ya dubi Musaddiq da hular sanyin dake kansa ya kuma duban hular da suka tsinta nan gabansu.
“What is this Assad.. Shin wannan zai iya zama hular Musaddiq ne..? Shin Musaddiq nada connection da Danger ne..? But how..?!” Ya k’arashe cikin tsananin rud’ani.
Assad ya girgiza kai yace “Mu’azzam wannan hula ce kawai, ba lallai ta zama na Musaddiq ba.. Mutane da yawa company guda d’aya.. Ta iya yuwa hular wani ne..”
Har lokacin duban hular yake kafin ya saka karan ya d’an bud’e cikin hular ya kunna hasken wayarsa yana haska cikin hular sosai, nan yaga alamun tsillin gashi cikin hular.
Ya d’ago ya dubi Assad kafin yace “I have an idea.. Ga alamun gashi cikin hular.. We will conduct a DNA test.. If it matches with Musaddiq kenan hular na Musaddiq ne.. And that means Musaddiq nada connection da Danger.”
Assad ya d’anyi shiru kafin yace “Toh amma wane connection Musaddiq zai samu da Danger..?”
Mu’azzam ya d’an gyara tsugunonsa kafin yace “Ka mance Musaddiq used to be a drug addict. Danger kuma drugs yake saida wa matasa.. Ka mance musabbabin zuwanmu wajen nan d’aya daga cikin customers d’in Danger shi ya bamu location d’in nan.. What if Musaddiq customer d’in Danger ne..?” Ya k’arashe cikin wane irin yanayi.
Assad ya shafi fuskarsa cikin rashin sanin mai zai furta.
Mu’azzam d’in ma zuba ma hular idanu yai cikin tsananin sanyin jiki. Muryarsa na rawa yake furta “Meke faruwa dani da ahalina Assad.. First Safeenah ce yanzu kuma Musaddiq.. Assad mai hakan ke nufi.. Assad I’m lost.. I .. I don’t know what to do or what to think... Shin wannan duka na cikin wasannin Danger ne..?”
Dafasa Assad yai kafin yace “We are still not sure idan hular nan ta Musaddiq ce Mu’azzam.. Ka kwantar da hankalinka zamuyi DNA test kuma zaka gani hular nan bata Musaddiq bace kawai kamanceceniya sukai kaji koh..”