Sashe 27
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yanda duk yake a birkice yasa Mu’azzam zuba masa idanu yana karantarsa “Musaddiq will you calm down please..”
“Wane irin calm down kake magana. Inace maka b’arawo ne kaman naga ya shigo kana ce min calm down.. I know you’re a Corp shisa nazo wajenka direct.. Please you need to hurry..” Ya k’arashe yana mai janyo Mu’azzam d’in suka nufi k’ofa.
“Wait Musaddiq.. I need to get dressed first.” Mu’azzam ya dakatar dashi da fad’in haka.
Sai sannan Musaddiq ya tina towel ne jikin Mu’azzam d’in.
Mu’azzam ya d’an girgiza kai yana k’ok’arin nufan wardrobe.
‘Oh shitt.. He can’t see her in there.’ Musaddiq ya fad’i cikin zuciyarsa. Kafin Mu’azzam d’in ya bud’e wardrobe d’in wanda tuni Ajidde dake dubansa ta d’an tsakanin da bai ida rufuwa ba ta sadak’ar kawai ya kamata dan har toshe bakinta tai ta rintse idanunta tana jiran mai afkuwa ya afku. Kwatsam Musaddiq ya k’araso ya damk’o hannunsa ya hanasa bud’e wardrobe d’in lokaci guda yake fad’in “Dan Allah kazo muje kar ya gudu.. Zo ka gansa ta window..” Ya k’arasa da Mu’azzam jikin window yana yaye curtains yake nuna masa “Look look duba tacan ka gani..”
Girgiza kai Mu’azzam yai cikeda k’osawa yace “Musaddiq I can’t see anything..”
“Ok wait muje wajen ka gani..”
Ya d’an fuzar da fuci hannayensa saman kunkumi “Bani jallabiyata cikin wardrobe I just hang it there.”
Cikin sauri Musaddiq ya jinjina kai yayinda Mu’azzam d’in ya d’an girgiza kai yana mai fuzar da fuci.
Musaddiq na bud’e wardrobe d’in sukai ido hud’u da Ajidde da k’iris ya rage bata saki fitsari ba dan tsoro.. Ya aika mata mugun kallo kafin ya zaro jallabiyar dake lank’aye jikin hanger. Ya maida wardrobe d’in ya rufe kafin ya kawo wa Mu’azzam jallabiyar ya zira. Lokaci guda Mu’azzam d’in ya nufi waje ba tareda ya kuma bi takan Musaddiq ba.. Mu’azzam na ficewa ya dawo ya bud’e Ajidde yace “Kina jina kar ki sake ya ganki dan idan ya kamaki kashinki ya bushe.” Cikin sauri Ajidde da tuni Ta had’a gumi take jinjina kai alamun taji. Sauri sauri ta fice ta nufi d’akin Aunty Nurah tana sauk’e nannuyan ajiyan zuciya.
Tana shiga ta tadda Hindu ta kawo mata abin kari. Hindu ta dubeta tace “Ina kika fito ga abin kari na kawo miki tuntuni..”
Murmushin yak’e Ajidde tai tace “Oh wllhi makewayi na fita inata nema ai.”
Hindu ta murmusa tace “Banda abinki Ajidde ai da tambaya kikayi muje na kaiki.”
Ajidde tai saurin girgiza kai tace “A’a ki barshi kawai ai yanzu ma zan tafi bana so nayi rana.”
Hindu Ta d’an tab’e baki tace “Toh shikenan.. Abincin fah..?”
Ajidde ta juya taga kayan dad’in da aka kawo mata. Sai kuma ta dubi Hindu tana wage baki alamun tanaso taci.
Hindu ta murmusa tace “Ki zauna kici abincinki kafin ki tafi..”
Aiko Hindu na ficewa Ajidde ta shiga yagan pepper soup d’in kaza tana turawa bakinta, hannu bibbiyu takeci kaman wanda za’a k’wace.. K’arshe bud’e jakarta tai tana tura sauran ciki. Kaman wacce ta tina wani abu sai kuma ta d’ago tana duban matar nan majinyaciya. A hankali ta k’arasa kanta ta tsaya gabanta “Na gode kinji. Ba don ke ba da bazan shigo gidan nan har naci dad’i irin haka ba.” Ta k’arashe tana wage baki. Lokaci guda ta mutsuke hannayenta jikinta ta sab’i Jakarta ta nufo k’ofa.
Sauri sauri ta fice tana lek’e tamkar maras gaskiya.
Koda Mu’azzam ya fice baiga alamun kowa ba baiga alamun komai ba gajeren tsaki yai yana girgiza kai yasan bazai wuce shak’iyancin Musaddiq bane suka motsa. Ya yanke shawarin tuntub’ar securities ko sunga wani abu suspicious. Har zai nufa gate Musaddiq ya k’araso yana d’an haki alamun yayi gudu.
Mu’azzam ya dubesa yace “Are you sure kaga wani ya shigo.”
Sosa kansa yake yana duban Mu’azzam d’in “I think it’s just my imagination.”
Kafesa da idanu Mu’azzam d’in yai yana karantarsa “Are you alright.?”
“Of course.. I’m absolutely fine, Inspector.”
Jinjina kai Mu’azzam yai yace “Lets go and ask the security men Ko sunga mutumin da ka gani..”
“No no no.. Nace maka Ina tunanin imagination d’ina ne.. Babu kowa.” Yai maganar yana d’an ciza lab’e bakinsa kad’an irinta masu laifi.
Takowa Mu’azzam yake zuwa gabansa yana mai tsaresa da idanu
“Wait. Are you sure you’re not on drugs.?” Mu’azzam ya tambaya yana duban Musaddiq d’in.
“Kasan na daina tin ba yau ba.. kuma bazan k’ara komawa ruwa ba in sha Allah. Dik da ban maka alk’awari ba amma nace In sha Allah.”
Jinjina kai Mu’azzam yai yana mai kuma karantarsa ba tareda yace komai ba.
Daidai nan Jume ya k’araso suka gaisa da Mu’azzam kafin ya dubi Musaddiq yace ana nemansa a wajen aiki. A tare Musaddiq da Jume suka wuce yayinda Mu’azzam ya nufo cikin gida yana jin dad’in yanda Rayuwar d’an uwan nasa ya Inganta a gidan gonar cikin ikon Allah.
Can Ajidde ta hangosa zai shige, gabanta yai wani irin fad’uwa dan ba komai Ta tina ba sai ganinsa da tai d’aure da towel. Tai saurin rintse idanunta ga k’amshin wardrobe d’insa da ya kama illahirin jikinta. Koda ta rintse idanun ma shi take hangowa. Ta kuma bud’esu tana furta “Wayyo Ajidde shige shigen ki ya kaiki kika gano sa a haka.” Jikinta ta shiga shinshinawa tanajin k’amshin wardrobe d’insa da ya kasa barin jikinta.
Muryar data sinkaya daga bayanta ya sanyata juyowa babu shiri.
Musaddiq ne ke tsaye bayanta ya tsareta da idanu. Ta ganesa shine mutumin da ya taimaketa ya sanyata cikin wardrobe. Kan kace mai ta duk’a saman gwiwoyinta ta d’ago hannu tana rok’onsa ya rufa mata asiri.
“Kin ganeni..?”
Tambayar da ya mata kenan.
Tai K’uri tana dubansa, sai kuma tai saurin girgiza kai alamun a’a
Yashin dake wajen ya d’iba cikin hannunsa ya kakkab’e had’ida shafa sauran saman fuskarsa. Take fuskarsa tai hazon k’ura.
Ajidde na zaro idanu waje tace “Kuran tashe.!” Sai kuma ta soma dariya tana nunasa.
SameenaAleeyou 📚
*GIDAN ARO*
*17*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Harga Allah ta bawa Musaddiq dariya yanda tai maganar amma Sai ya gimtse yace “Zaki min bayani yanzu, what exactly were you doing in there..? Mai kike cikin d’akin mutumin nan..?”
Zaro idanu waje tai sai kuma tai dariyar yak’e tace “Ban d’aki nake nema kawai sai tsintar kaina nai a wannan d’akin.. Kai kuma fah.. Ba kace min baka shiga wannan gidan ba.. Ya na ganka a cikin gidan.. Kuma da alama ka saba shiga.. Watau dai k’arya ka min kenan..?” Ta k’arashe hannayenta saman kunkumi tana mai tsaresa da idanu tamkar wacce zata kai masa bugu.
“Wait what.. Ke ni nake miki k’arya..?”
Ajidde ta d’an murgud’a masa baki tace “Toh ni bance kayi k’arya ba amma Maiyasa kace min haka..?”
Tsareta da idanu yai dan a yanda ya d’auketa shashasha bai zaci zata iya d’ago zancen da sukai ranan ba.. Ya gyara tsayuwarsa yace “Tsaya ai idan ban mance ba nace miki inada aboki d’an gidan..”
Ajidde Ta zaro ido Tace “Wannan ne abokin naka..? Ai shine mutumin da ya biyoni ranan..”
Musaddiq ya zuba mata idanu da tsananin mamaki “Toh kin dai aikata laifin kenan.. Na tabbata ke mai laifi ce.. Zaki fad’a mun mai kike a d’akin ko kuma yanzu na shiga cikin gidan na sanar dashi komai..”
Cikin tsananin damuwa Ajidde take rok’onsa “Dan Allah ka rufa mun asiri.. Ka rufa mun asiri kar ka tona mun asiri wajensa.. Idan ka tona mun asiri shikenan bazan bawa matar nan magani ba.. Dan Allah ka barni na gwada sa’an magani na akan matar nan.. Nasan zakaso mahaifiyar abokinka ta sami lafiya..” Ta k’arashe cikin tsananin nuna damuwa.
Musaddiq ya jinjina kai yace “K’warai kuwa nafi kowa so Aunty Nuratu Ta sami lafiya.. Zan rufa miki asiri amma sai kin sanar dani gaskiyar Al’amarin..”
Ajidde ta had’iyi miyau da k’yar tana mai kuma zaro idanu “Zan fad’a maka amma saidai idan zaka mun alk’awari.”
Cikin wane irin yanayi yake dubanta wannan karon. Lokaci guda yananyin nasa ya canza, cikin wane irin kakkausar murya yake fad’in “I thought I’ve already told you.. I don’t make Promises.. Bana Alk’awari.. Ban tab’a cika Alk’awari ba.. Kuma bazan tab’a cika alk’awari ba... Kuma na rasata ne ta dalilin rashin cika Alk’awari na.!” Ya k’arashe siririyar hawaye tana gangaro masa.
Cikin tsananin tsoro Ajidde ke dubansa, idanunta Sun firfito waje sabida tsoro. A hankali Ta soma k’ok’arin jada baya..
“Ina zakije.. Bazaki bar wajen nan ba sai kin fad’a mun sirrinki..” Ya fad’i yana dubanta.
Cikin sauri take girgiza kai “Banida Sirri.. Ni d’in kawai magani nake kawowa..” Tana ida fad’in haka tasa kai zata shige.
Musaddiq yasha gabanta yana binta da wani irin kallo wanda ya kuma haifar mata da tsoro “You are a thief..! Ke b’arauniya ce.. Wancan ranan sata kika so yi masa sai ya biyoki kika b’uya.. Wannan karon ma sata kika shiga d’akinsa zaki masa sai Allah ya kawoni kafin ki ida nufinki.. Now you tell me.. Shin wacece ke.. Mai magani ce ke kokuwa b’arauniya ce.?!”
Idanun Ajidde suka kawo ruwa, Ta soma girgiza masa kai tana fad’in “Dan Allah ka rufa mun asiri wllhi nima umarni nake bi..”
“Umarni kike bi.. Umarnin wa..?” Ya kuma tambaya yana dubanta.
Ajidde ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana dubansa “Zan fad’a maka komai amma zaka yi shiru.. Bazaka fad’a ma kowa komai ba.. Idan har kana so na bawa matar nan magani.. Sannan zaka taimakeni..”
Musaddiq ya jinjina kai yace “Zanyi duk abinda kikace Idan kika fad’a mun komai..”
K’asar wata bishiya suka zauna Su duka biyun, Musaddiq ya dubeta yace “Ina sauraronki..”
A hankali Ajidde Ta soma karanto masa sana’ar da Kyallu ta d’aurata bisa, ta kuma sanar dashi k’udirin kyallu na cewa muddin tazo gidan bata sato masu wani abu ba ga uk’ubar da zata mata.. Wannan dalili shiyasa take k’ok’arin aikata satan da yace tana yi.
Musaddiq ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali yana dubanta “Toh ita Inna Kyallu bata tinanin watarana a kamaki.?”
Ajidde ta girgiza kai tace “Inna kyallu bata yarda da fad’uwa ba.. Dik abinda zatayi sai ta masa shiri sosai domin kuwa har layar zana ta bani.. Sannan idan aka kamani babu damuwarta dan cewa zatai dama tin can ni b’arauniya ce.”
“Wane irin calm down kake magana. Inace maka b’arawo ne kaman naga ya shigo kana ce min calm down.. I know you’re a Corp shisa nazo wajenka direct.. Please you need to hurry..” Ya k’arashe yana mai janyo Mu’azzam d’in suka nufi k’ofa.
“Wait Musaddiq.. I need to get dressed first.” Mu’azzam ya dakatar dashi da fad’in haka.
Sai sannan Musaddiq ya tina towel ne jikin Mu’azzam d’in.
Mu’azzam ya d’an girgiza kai yana k’ok’arin nufan wardrobe.
‘Oh shitt.. He can’t see her in there.’ Musaddiq ya fad’i cikin zuciyarsa. Kafin Mu’azzam d’in ya bud’e wardrobe d’in wanda tuni Ajidde dake dubansa ta d’an tsakanin da bai ida rufuwa ba ta sadak’ar kawai ya kamata dan har toshe bakinta tai ta rintse idanunta tana jiran mai afkuwa ya afku. Kwatsam Musaddiq ya k’araso ya damk’o hannunsa ya hanasa bud’e wardrobe d’in lokaci guda yake fad’in “Dan Allah kazo muje kar ya gudu.. Zo ka gansa ta window..” Ya k’arasa da Mu’azzam jikin window yana yaye curtains yake nuna masa “Look look duba tacan ka gani..”
Girgiza kai Mu’azzam yai cikeda k’osawa yace “Musaddiq I can’t see anything..”
“Ok wait muje wajen ka gani..”
Ya d’an fuzar da fuci hannayensa saman kunkumi “Bani jallabiyata cikin wardrobe I just hang it there.”
Cikin sauri Musaddiq ya jinjina kai yayinda Mu’azzam d’in ya d’an girgiza kai yana mai fuzar da fuci.
Musaddiq na bud’e wardrobe d’in sukai ido hud’u da Ajidde da k’iris ya rage bata saki fitsari ba dan tsoro.. Ya aika mata mugun kallo kafin ya zaro jallabiyar dake lank’aye jikin hanger. Ya maida wardrobe d’in ya rufe kafin ya kawo wa Mu’azzam jallabiyar ya zira. Lokaci guda Mu’azzam d’in ya nufi waje ba tareda ya kuma bi takan Musaddiq ba.. Mu’azzam na ficewa ya dawo ya bud’e Ajidde yace “Kina jina kar ki sake ya ganki dan idan ya kamaki kashinki ya bushe.” Cikin sauri Ajidde da tuni Ta had’a gumi take jinjina kai alamun taji. Sauri sauri ta fice ta nufi d’akin Aunty Nurah tana sauk’e nannuyan ajiyan zuciya.
Tana shiga ta tadda Hindu ta kawo mata abin kari. Hindu ta dubeta tace “Ina kika fito ga abin kari na kawo miki tuntuni..”
Murmushin yak’e Ajidde tai tace “Oh wllhi makewayi na fita inata nema ai.”
Hindu ta murmusa tace “Banda abinki Ajidde ai da tambaya kikayi muje na kaiki.”
Ajidde tai saurin girgiza kai tace “A’a ki barshi kawai ai yanzu ma zan tafi bana so nayi rana.”
Hindu Ta d’an tab’e baki tace “Toh shikenan.. Abincin fah..?”
Ajidde ta juya taga kayan dad’in da aka kawo mata. Sai kuma ta dubi Hindu tana wage baki alamun tanaso taci.
Hindu ta murmusa tace “Ki zauna kici abincinki kafin ki tafi..”
Aiko Hindu na ficewa Ajidde ta shiga yagan pepper soup d’in kaza tana turawa bakinta, hannu bibbiyu takeci kaman wanda za’a k’wace.. K’arshe bud’e jakarta tai tana tura sauran ciki. Kaman wacce ta tina wani abu sai kuma ta d’ago tana duban matar nan majinyaciya. A hankali ta k’arasa kanta ta tsaya gabanta “Na gode kinji. Ba don ke ba da bazan shigo gidan nan har naci dad’i irin haka ba.” Ta k’arashe tana wage baki. Lokaci guda ta mutsuke hannayenta jikinta ta sab’i Jakarta ta nufo k’ofa.
Sauri sauri ta fice tana lek’e tamkar maras gaskiya.
Koda Mu’azzam ya fice baiga alamun kowa ba baiga alamun komai ba gajeren tsaki yai yana girgiza kai yasan bazai wuce shak’iyancin Musaddiq bane suka motsa. Ya yanke shawarin tuntub’ar securities ko sunga wani abu suspicious. Har zai nufa gate Musaddiq ya k’araso yana d’an haki alamun yayi gudu.
Mu’azzam ya dubesa yace “Are you sure kaga wani ya shigo.”
Sosa kansa yake yana duban Mu’azzam d’in “I think it’s just my imagination.”
Kafesa da idanu Mu’azzam d’in yai yana karantarsa “Are you alright.?”
“Of course.. I’m absolutely fine, Inspector.”
Jinjina kai Mu’azzam yai yace “Lets go and ask the security men Ko sunga mutumin da ka gani..”
“No no no.. Nace maka Ina tunanin imagination d’ina ne.. Babu kowa.” Yai maganar yana d’an ciza lab’e bakinsa kad’an irinta masu laifi.
Takowa Mu’azzam yake zuwa gabansa yana mai tsaresa da idanu
“Wait. Are you sure you’re not on drugs.?” Mu’azzam ya tambaya yana duban Musaddiq d’in.
“Kasan na daina tin ba yau ba.. kuma bazan k’ara komawa ruwa ba in sha Allah. Dik da ban maka alk’awari ba amma nace In sha Allah.”
Jinjina kai Mu’azzam yai yana mai kuma karantarsa ba tareda yace komai ba.
Daidai nan Jume ya k’araso suka gaisa da Mu’azzam kafin ya dubi Musaddiq yace ana nemansa a wajen aiki. A tare Musaddiq da Jume suka wuce yayinda Mu’azzam ya nufo cikin gida yana jin dad’in yanda Rayuwar d’an uwan nasa ya Inganta a gidan gonar cikin ikon Allah.
Can Ajidde ta hangosa zai shige, gabanta yai wani irin fad’uwa dan ba komai Ta tina ba sai ganinsa da tai d’aure da towel. Tai saurin rintse idanunta ga k’amshin wardrobe d’insa da ya kama illahirin jikinta. Koda ta rintse idanun ma shi take hangowa. Ta kuma bud’esu tana furta “Wayyo Ajidde shige shigen ki ya kaiki kika gano sa a haka.” Jikinta ta shiga shinshinawa tanajin k’amshin wardrobe d’insa da ya kasa barin jikinta.
Muryar data sinkaya daga bayanta ya sanyata juyowa babu shiri.
Musaddiq ne ke tsaye bayanta ya tsareta da idanu. Ta ganesa shine mutumin da ya taimaketa ya sanyata cikin wardrobe. Kan kace mai ta duk’a saman gwiwoyinta ta d’ago hannu tana rok’onsa ya rufa mata asiri.
“Kin ganeni..?”
Tambayar da ya mata kenan.
Tai K’uri tana dubansa, sai kuma tai saurin girgiza kai alamun a’a
Yashin dake wajen ya d’iba cikin hannunsa ya kakkab’e had’ida shafa sauran saman fuskarsa. Take fuskarsa tai hazon k’ura.
Ajidde na zaro idanu waje tace “Kuran tashe.!” Sai kuma ta soma dariya tana nunasa.
SameenaAleeyou 📚
*GIDAN ARO*
*17*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Harga Allah ta bawa Musaddiq dariya yanda tai maganar amma Sai ya gimtse yace “Zaki min bayani yanzu, what exactly were you doing in there..? Mai kike cikin d’akin mutumin nan..?”
Zaro idanu waje tai sai kuma tai dariyar yak’e tace “Ban d’aki nake nema kawai sai tsintar kaina nai a wannan d’akin.. Kai kuma fah.. Ba kace min baka shiga wannan gidan ba.. Ya na ganka a cikin gidan.. Kuma da alama ka saba shiga.. Watau dai k’arya ka min kenan..?” Ta k’arashe hannayenta saman kunkumi tana mai tsaresa da idanu tamkar wacce zata kai masa bugu.
“Wait what.. Ke ni nake miki k’arya..?”
Ajidde ta d’an murgud’a masa baki tace “Toh ni bance kayi k’arya ba amma Maiyasa kace min haka..?”
Tsareta da idanu yai dan a yanda ya d’auketa shashasha bai zaci zata iya d’ago zancen da sukai ranan ba.. Ya gyara tsayuwarsa yace “Tsaya ai idan ban mance ba nace miki inada aboki d’an gidan..”
Ajidde Ta zaro ido Tace “Wannan ne abokin naka..? Ai shine mutumin da ya biyoni ranan..”
Musaddiq ya zuba mata idanu da tsananin mamaki “Toh kin dai aikata laifin kenan.. Na tabbata ke mai laifi ce.. Zaki fad’a mun mai kike a d’akin ko kuma yanzu na shiga cikin gidan na sanar dashi komai..”
Cikin tsananin damuwa Ajidde take rok’onsa “Dan Allah ka rufa mun asiri.. Ka rufa mun asiri kar ka tona mun asiri wajensa.. Idan ka tona mun asiri shikenan bazan bawa matar nan magani ba.. Dan Allah ka barni na gwada sa’an magani na akan matar nan.. Nasan zakaso mahaifiyar abokinka ta sami lafiya..” Ta k’arashe cikin tsananin nuna damuwa.
Musaddiq ya jinjina kai yace “K’warai kuwa nafi kowa so Aunty Nuratu Ta sami lafiya.. Zan rufa miki asiri amma sai kin sanar dani gaskiyar Al’amarin..”
Ajidde ta had’iyi miyau da k’yar tana mai kuma zaro idanu “Zan fad’a maka amma saidai idan zaka mun alk’awari.”
Cikin wane irin yanayi yake dubanta wannan karon. Lokaci guda yananyin nasa ya canza, cikin wane irin kakkausar murya yake fad’in “I thought I’ve already told you.. I don’t make Promises.. Bana Alk’awari.. Ban tab’a cika Alk’awari ba.. Kuma bazan tab’a cika alk’awari ba... Kuma na rasata ne ta dalilin rashin cika Alk’awari na.!” Ya k’arashe siririyar hawaye tana gangaro masa.
Cikin tsananin tsoro Ajidde ke dubansa, idanunta Sun firfito waje sabida tsoro. A hankali Ta soma k’ok’arin jada baya..
“Ina zakije.. Bazaki bar wajen nan ba sai kin fad’a mun sirrinki..” Ya fad’i yana dubanta.
Cikin sauri take girgiza kai “Banida Sirri.. Ni d’in kawai magani nake kawowa..” Tana ida fad’in haka tasa kai zata shige.
Musaddiq yasha gabanta yana binta da wani irin kallo wanda ya kuma haifar mata da tsoro “You are a thief..! Ke b’arauniya ce.. Wancan ranan sata kika so yi masa sai ya biyoki kika b’uya.. Wannan karon ma sata kika shiga d’akinsa zaki masa sai Allah ya kawoni kafin ki ida nufinki.. Now you tell me.. Shin wacece ke.. Mai magani ce ke kokuwa b’arauniya ce.?!”
Idanun Ajidde suka kawo ruwa, Ta soma girgiza masa kai tana fad’in “Dan Allah ka rufa mun asiri wllhi nima umarni nake bi..”
“Umarni kike bi.. Umarnin wa..?” Ya kuma tambaya yana dubanta.
Ajidde ta d’ago idanunta masu zuban hawaye tana dubansa “Zan fad’a maka komai amma zaka yi shiru.. Bazaka fad’a ma kowa komai ba.. Idan har kana so na bawa matar nan magani.. Sannan zaka taimakeni..”
Musaddiq ya jinjina kai yace “Zanyi duk abinda kikace Idan kika fad’a mun komai..”
K’asar wata bishiya suka zauna Su duka biyun, Musaddiq ya dubeta yace “Ina sauraronki..”
A hankali Ajidde Ta soma karanto masa sana’ar da Kyallu ta d’aurata bisa, ta kuma sanar dashi k’udirin kyallu na cewa muddin tazo gidan bata sato masu wani abu ba ga uk’ubar da zata mata.. Wannan dalili shiyasa take k’ok’arin aikata satan da yace tana yi.
Musaddiq ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali yana dubanta “Toh ita Inna Kyallu bata tinanin watarana a kamaki.?”
Ajidde ta girgiza kai tace “Inna kyallu bata yarda da fad’uwa ba.. Dik abinda zatayi sai ta masa shiri sosai domin kuwa har layar zana ta bani.. Sannan idan aka kamani babu damuwarta dan cewa zatai dama tin can ni b’arauniya ce.”