← Book details Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 175

Sashe 60

Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Katsesa yai da fad’in “I do not give a damn Assad.! Didn’t you hear what that imbecile was saying.? Ko bakaji abubuwan da yake fad’i bane..?” Ya fuzar da fuci yana duban Assad d’in “Kar ka sake dakatar dani Assad.. Idan kuma ba haka ba..?” Yaci gaba da girgiza kai kafin yace “I don’t know what I might do to you..!” Yana ida fad’in haka ya fice daga wajen gaba d’aya.. Yana ficewa ya hango Musaddiq ya fito daga motarsa. Sukai tsaye suna duban juna, kana ganin fuskar Musaddiq zaka fahimci yana cikin tsananin tashin hankali ne wanda baki bazai iya fad’i ba. Mutuwar Ikram ya dawo wa Musaddiq sabo.

Mu’azzam ya k’ok’arin danne nasa tashin hankalin kad’an yana mai k’arasowa kusan Musaddiq d’in.

Cikin wane irin yanayi Musaddiq ke dubansa “Is it true.?” Ya tambaya yana duban Mu’azzam d’in.

Mu’azzam ya d’an kauda Kai gefe kad’an yana fuzar da fuci a hankali.

Musaddiq ya sake fad’in “Da gaske ne.. Safeenah itace prime suspect.. Did she kill Ikram..? C’mon Mu’azzam answer me talk to me now.?!”

Jinjin kai Mu’azzam yai a hankali yana duban Musaddiq d’in “I’m afraid yes.!” Ya k’arashe yana jinjina kai alamun tabbatarwa.

Kauda Kai gefe Musaddiq yai yana mai rik’e bakinsa da duka hannayensa biyu.. Safeenah ta kashe masa Ikram. Ta rabasa da Ikram.. His very own sister.. Ji yai kaman bashi a duniyar, k’afafunsa na barazanar gaza d’aukansa.

Cikin sauri Mu’azzam ya tallafosa ya rik’esa sosai “She.. Killed her.. Ta kashe mun ita.. Ta rabani da ita.. Maiyasa zatayi haka.?!”

Saurin rungume Musaddiq Mu’azzam d’in yai yana jin zuciyarsa na masa rauni shima “That’s enough Musaddiq.. Ikram bazata wuce lokacinta ba.. Amma wad’anda suka kasheta need to pay.. I promise you, I’ll make them pay for what they did to her. They’ll pay dearly.” Ya k’arashe yana mai janyo Musaddiq d’in suka zauna nan saman wasu kujeru dake gaban wajen.

A can interrogation kaw Safeenah dai kasa cewa komai tai sai ma duban Ameer da take da matuk’ar mamaki. Ya akai Ameer yasan anyi arresting d’inta.? Waye ya sanar dashi.? Yama akai har yaji komai ya taho in a very short time..?

“Did I surprise you.?” Ya fad’i yana dubanta murmushi saman fuskarsa.

Dubansa take har lokacin tana mamakin yanda akai yasan tana ofishin Yansanda. Lokaci guda ta jinjina kai tace “And you know I don’t like surprises..” Ta d’an dakata kafin tace “Ameer ya akai Kasan anyi arresting d’ina.. How did you find out about this in such a very short time.?”

Ameer ya murmusa yana mai d’aura k’afa d’aya saman d’aya “Let’s say I do my homework.”

Safeenah Ta girgiza kai tace “Ameer what kind of game are you playing..? Bayan threatening da kakeyi cewa Kasan wani abu game dani.. Now you appear as my lawyer. What is this Ameer..? Tell me mai ka sani gameda abinda ke faruwa dani.?”

Ameer ya rage girman idanunsa yana karantarta irin dai yanda lauyoyi keyi idan suna karantar mutum gaskiya yake fad’i ko k’arya. Lokaci guda yake furta “Na fad’a miki I do my homework Safeenah.. And idan zaki tsaya kina b’ata ma kanki lokaci da tambayoyin da bazasu amfaneki na zaki tafi jail ne a banza a wofi ba tareda kin aikata laifin da ake tuhumarki ba.. Safeenah even your family basu baki support ba. you are all alone in this battle, ya kamata ki taimaki kanki ki cire kanki a wannan mess d’in.. And ni kad’ai ne mutumin da zai cireki a mess d’in da kika tsinci kanki ciki Safeenah..” Ya gyara zama yana mai tsareta da idanu “Now you tell me everything.. I mean kar ki b’oye min komai.. Ki fad’a mun duk abinda ya faru.”

“What if I don’t.” Ta fad’i tana dubansa

“You’ll have to Safeenah.. Idan har kinaso ki fita daga wannan mess d’in.. Unless kuma kinaso ki tafi jail for the crime you did not commit.”

Safeenah daketa murza tafukan hannayenta kauda FUSKA gefe tai kafin a hankali ta soma furta “Mommy zata turo min lawyer, a very good one.. I don’t trust you, and I don’t want you to handle my case.. Ka gane..”

Murmusawa yai yana dubanta kafin yace “What if nace miki Mommy ce ta turo ni.?”

In a shock take kuma dubansa, ta girgiza kai kad’an tace “Pardon..”

Ameer ya d’an matso kad’an yana mai d’aura duka hannayensa saman table d’in “Feenah.. You need to cooperate with me idan har kina so ki ceci kanki.. Kema kin sani Mu’azzam zai komai Domin ya Turaki gidan yari.. Kuma ina mai tabbatar miki a halin yanzu zai wuya yaci gaba a zama dake matsayin mata da miji.. We are talking about his sister here Feenah.. Kina dai ganin yanda ya bada himma wajen ganin yayi nasara kan binciken da yake.. Kar ki bari bayan saye zuciyarki da soyayyarsa da yayi ya kuma saye miki freedom d’inki.. Ki tashi ma kanki kafin lokaci ya k’ure I’m sure baza’a d’auki lokaci ba za’a tafi kotu.. You don’t belong here Feenah.. You deserve a good life tareda mijin dake knaunarki.. Kar ki bari Mu’azzam ya d’auke miki wannan..!” Ya k’arashe yana mai tsareta da idanu.

Hawaye ne Safeenah taji na zuwa mata. Cikin muryar kuka take furta “Ban aikata ba.. I swear I didn’t do it.. But I don’t know.. Ban San ya zanyi bayani Mu’azzam ya fahimceni ba..”

Katseta yai da fad’in “Ba wa Mu’azzam zaki fad’i ba Safeenah.. Idan kuwa kikai gangancin fad’iwa Mu’azzam zaki k’ara kulle kanki cikin case d’in ne.. Kar ki mance cewa Mu’azzam shi yake gudanar da bincike kan case d’in nan.. Sannan Ikram ‘yaruwarsa ce.. So ko mai zaki ce bazai yarda ba Safeenah.. Kece kawai zakiyi duk yanda zakiyi ki zame kanki.. And don’t forget, You are well and fully entrapped in this case.. You’ve no way out domin kuwa Tabbas an tura miki sak’on address na location d’in da aka tsinci gawan Ikram.. And you received that text message.. But don’t you worry zan wanke ki a Kotu in sha Allah.. And I’ll do it to the best of my abilities.. I promise you.. Kawai abinda nike so dake shine ki bani had’in Kai Safeenah.. Hundred percent.. Kin fahimta..?” Ya k’arshe yana kuma tsareta da idanu.

Safeenah ta share hawayen da ya zubo mata. Daidai lokacin Mu’azzam ya turo k’ofan ya shigo domin kuwa lokacin da aka d’ibar mata na ganawa da lawyer d’inta ya cika.

Ya tsaresu da idanu musamman Safeenah dake matsan k’walla.

Lokaci guda Maleeka ta kawo kujera ta ajiye ma Mu’azzam nan jikin table d’in. D’akin binciken ya zamto su uku kenan ciki.. Safeenah sai Ameer Wanda take lawyer d’inta ne saiko Mu’azzam mai gudanar da bincike.

Ajiye wayar Sagir Mu’azzam yai saman table d’in kafin yace “An tura miki wannan sak’on da lambar ki a ranan 12 ga watan June.. You can’t deny it domin kuwa munada shaidan da zai tabbatar an tura sak’on zuwa layinki sannan Kinyi receiving.. Just admit it already..!”

Ameer ne ya katseta da fad’in “Excuse me Mr Inspector.. Are you suggesting that my client committed that crime.?”

Wani duban Mu’azzam ya aika masa kafin yace “I don’t remember asking you.. Safeenah nake tambaya kuma ita zata amsa min.!”

Safeenah dake sakin huci tana duban Mu’azzam d’in lokaci guda itama take furta “I have the right to be assistant by a Legal Counselor.. And Ameer here, is my Lawyer.!”

Ameer ya murmusa yana duban Mu’azzam d’in “Calm down Inspector.. Ina fata ka saurari matarka, I’m only her Lawyer. So don’t bring up your personal issues with me here.”

A wulak’ance Mu’azzam ke aika masa wani irin duba kafin yace “I don’t give a damn about you, Mr lawyer. Now you tell your client to answer my question.!”

Safeenah ta girgiza kai tace “Wannan layin tsohon layina ne.. Kuma ni banyi receiving sak’on ba.”

Mu’azzam ya jinjina kai yace “Amma bayan wannan ranan kika canza layin..? Haka ne.. So definitely wannan sak’on ya isa miki.”

Wannan karon Ameer ne Yai maganar “You heard my client Mr Officer, batai receiving sak’on ba. Gidan biki ne kar ka mance kuma ita d’in Amarya ce wacce aka sani da zafin kai, so za’a iya tura sak’on wayar nata na hannun wani.. So ba lallai ita tayi receiving wannan sak’on ba. And da kake maganar canza layi ansan most of Amare suna canza layi idan sukayi aure.. So ina shawartanka da ka daina d’aura wa client d’ina laifi kai tsaye.. Sannan sauran tanbayoyinka zaifi kyau ka ajiyesu ka sanar da lauyanka har dai zuwa ranan da zamu tafi Kotu.”

Ameer yana ida fad’in haka ya mik’e yana gyara zaman suit d’insa.

Mik’ewa Mu’azzam d’in ma yai yana aika masu wane irin kallo “You must talk Safeenah.. Sai Kinyi magana tun kafin aje Kotu na miki alk’awari.. Zaki fad’i komai..!” Yana ida fad’in haka yasa kai ya fice daga room d’in.

Koda aka fito da Safeenah za’a kaita cell d’inta a nan ta had’u da Musaddiq yayi tsaye yana aika mata wane irin duba. Safeenah ta rok’i sergeant d’in Ta barta tai magana da D’anuwanta.

Musaddiq ya k’araso yana mai zuba mata rinannun idanunsa “Tambaya d’aya nake so na miki. Maiyasa kika aikata..? Why did you do it Safeenah..? Maiyasa kika rabani da Ikram..?”

Girgiza kai Safeenah take tana duban Musaddiq “Wllhi ban aikata ba Musaddiq ka yarda dani.. And I know nothing about it..”

Jinjina kai yai yana dubanta kafin yace “Idan ya tabbata akwai saka hannunki a kisan Ikram ki mance kinada D’anuwa Musaddiq..!” Yana ida fad’in haka ya juya ya fice Safeenah na kiran sunansa ko tsaya baiba balle ya tankata. Haka sergeant d’in ta tasa kanta ta turata zuwa cell d’inta..
Chapter 60 · 0% Book details