Sashe 30
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zuciyar Sadiya yai wani irin tsinkewa yayinda Sabeeran ta zuba mata idanu.
Umma ce tai k’arfin halin cewa “A’a Sabeera kece tafe.. Sannu da zuwa.. K’araso ki zauna.”
Ko gizau Sabeera batai ba saima duban Sadiya da take. Umma ta dubi Sadiya ta kuma dubi Sabeeran da irin kallon da take ma Sadiya. Kafin Umma tai wani aune Sabeera ta k’araso ta duk’a yanda Sadiya ke duk’e suna fuskantar juna saidai kan Sadiyar a k’asa yake.
“Ki fad’a mun gaskiya da bakinki.. Shin da gaske ne..? Sadiya da gaske ne abinda nake ji tsakaninki da mahaifina..?!”
Izuwa lokacin hawaye sun soma ambaliya saman fuskar Sadiya, ta kasa d’agowa ta dubi Sabeera sai hawaye dake zarya saman fuskarta.
Cikin zuban hawaye da tsananin d’aga murya Sabeeran ke ci gaba da fad’in “Talk to me Sadiya.. Tell me the truth.! Ki fad’a mun gaskiya.. Wacece ke a wajen mahaifina..! Ki fad’a mun Sadiya..!!” Ta k’arashe tana damk’o kafad’un Sadiya tana mai jijjigata da iya k’arfinta hawaye na ambaliya saman fuskarta a yayinda kukan Sadiyar ma ya k’aru.
Umma dake gefe ta kasa tab’uka komai sai hawayen da itama taji suna zubo mata.
Cikin muryar kuka ba tareda ta d’ago ta dubi Sabeeran ba take furta “I’m sorry.. I’m sorry Sabeera.. Please forgive me.. Dan Allah ki yafe mun..!”
Take jikin Sabeera ya sake gaba d’aya.. Maiyasa Sadiya take bata hak’uri.. Kenan da gaske ne.. Kenan maganganun da mutane suke fad’i gaskiya ne.. Sadiya da mahaifinta... Ji tai Ta kasa k’arasa tunanin sabida wani irin jiwa dataji na neman kaita k’asa. Take taji wani irin k’arfi yazo mata.. Ta hankad’a Sadiyar da k’arfin gaske Wanda saida ya kaita k’asa.. Sadiya ta buga kanta had’ida gwiwan hannunta da tuni ya karje ya soma jini.. Babu shiri Umma ta mik’e da k’yar dikda k’afarta dake mata ciwo Ta nufi kan d’iyarta.
Sabeera ta kuma yowa kan Sadiyar tana kuka sosai take fad’in “Sai na kasheki kafin ki zama matar Babana..!” Tayo kanta tana k’ok’arin fuzgota saidai tuni Umma ta raba tsakaninsu ta tallafi Sadiyar dake kuka sosai tana duban Sabeera dake k’ok’arin funcikota..
Cikin kuka Sabeera ke furta “I trusted you.. I believed in you.. I never doubted you.. I never judged you.. Duk abinda mutane zasu fad’i akanki Sadiya dai dai da rana guda ban tab’a yarda ba.. Ashe duk ba haka bane.. Ashe ked’in da gaske macijiyace mai bak’in guba.. Ta yaya zaki min haka.. Ta yaya zaki aminiyar data aminta dake irin haka Sadiya..!” Ta kuma yowa kanta tana kuma janyota tana fad’in sai tayi ajalinta.
Daidai lokacin Baban Sabeera ya shigo da shopping bags hannunsa, nan ya tadda wannan hargitsi dake tashi cikin gidansu Sadiyar.
Da tsananin mamaki yake duban Sabeera dake k’ok’arin kaima Sadiya duka Umma na tarewa.
“Ke Sabeeraa.!!” Ya fad’i cikin daka tsawa yana mai fuzgo Sabeeran had’ida d’aura mata mari maiji da lafiya..
Sabeera ta tsaya Cak tana duban mahaifin nata cikeda tsananin mamaki hannunta guda dafe da k’uncinta.
Sadiya kaw tuni ta rungume mahaifiyarta tana kuka sosai..
“Dan gidanku ashe bakida hankali.. Ashe ke shashasha ce ban Sani ba.. Uban wa ma ya baki izinin fitowa daga gida.. Matar nawa zaki daka dan bakida kunya bakida hankali Ko..!”
Baki sake kurum Sabeera ke duban mahaifinta da kalaman da yake, tana ganin kaman mafarki take ba gaskiya bane.. Tanada tabbacin ba don zafin sauk’ar marin dataji a k’uncinta ba zata iya cewa mafarki take ba gaskiya bane..
A guje Sadiya dake tsananin kuka ta shige parlor yayinda Baban Sabeera yai yunk’urin bin bayanta yana fad’in “Baby.. Baby kiyi hak’uri dan Allah I’ll deal with her myself..”
Cikin hawaye Umma Ta katsesa da fad’in “Ya isa dan Allah..!” Tai saurin bin bayan Sadiya tana ambato sunata ga k’annenta da tuni sun fito suna kallon abinda ke faruwa.
Baban Sabeera kaw hannunta ya damk’o yana fad’in “Shige muje ki sanar dani ubanda ya koya miki rashin kunya..”
Haka ‘yan lungun sukaita lek’e wasu na k’us k’us d’in an fara dan kaf lungun gidansu Sadiya ne bai rabuwa da hatsaniya da tashin hankali.. Daga wannan sai wancan..
Sadiya kam kulle kanta tai a d’aki tana kuka sosai kaman ranta zai fice.
A b’angaren Maman Sabeera kaw Ramatu tazo sun k’ule a d’aki suna tattauna lamarin tareda neman mafita.
Ramatu Ta nusa tace “Ai wllhi Rahina Kema da naki, idan b’era da sata daddawa da wari.. Ni tin yaushe nace ki raba ‘yarki da wannan yarinya Sadiya mai shegen kyau kaman aljana.. Wannan yarinyar tana shigo miki gida Ta shnatak’e kaman gidan Ubanta, santaleliyar yarinya irin wannan kice min mijinki bazai d’aura idanu kanta ba..”
Maman Sabeera tace “Wllhi Ramatu ban tab’a kawo haka ba tinda naga bama ya son alak’arsu.. Kuma ni ban tab’a yarda yarinyar lalatacciya bace kaman yanda ake cewa _Never judge a Book by its cover_ toh ban tab’a munana ma yarinyar nan zato ba dan wataran wanda kake zaton mutumin kirki ne bashi ne mutumin kirkin ba, wanda kayi zaton na banza ne sai kaga shine mutumin kirkin.. Ni da har ina sha’awanta ma Abdallah (yayan Sabeera dake karatu k’asar waje..) Amma ni koda wasa ban zaci Wai Alhaji zai d’aura idanu kanta ba...Yayi aurensa ni bazan hanasa ba ya auri ko wacece amma kam banda Sadiya k’awar Sabeera... Ina zan Kai wannan d’imbin bak’in ciki da tashin hankali ga uwa uba Sabeera taji komai..”
Ramatu ta tab’e baki tace “Rahina zama fah bai ganki ba, tashi zakiyi muje har gidansu yarinyar nan muci uban uwarta da kyau dan itace tsararmu ba d’iyarta ba.. Ki daina wannan simi simi d’in nan naki ki tashi ki karb’a ma kanki da yaranki ‘yanci idan kuma ba haka ba ki zuba ido ki zama ‘yar kallo cikin gidanki.. Kinaji kina gani yarinya ‘yar cikinki Ta k’unsa miki bak’in ciki. Keda gidanki yafi k’arfinki.”
“Ramatu sanin kanki ne ban isa na hana namiji son mata ba dan a halittarsu ne amma damuwar shine kar ya nemi na banza, yayi auren dan shine mafi a’ala tinda Allah ya huwace masa daman auren mace sama da guda. Sannan ni idan zai auren ya auro ko wacece amma tsakani ga Allah banda Sadiya.. Idan ni zan iya jura Sabeera fah.. Sabeera bazata iya jura ba.. Ni wllhi tashin hankalin da ‘yata zata shiga nake tunani.. Yaran nan fah bacci ne ke rabasu sanda suke makaranta kafin su tafi yajin aiki har karatu tare suke..”
Ramatu Ta katse Ta da fad’in “Ni dan Allah kin isheni, kin cika ni da surutun da babu gaira babu dalili.. Dik kin San da wannan shine kika d’add’agoni ko karin kummalo banyi ma mijina ba.. Dama Kinsan wa’azi zaki kirani kimin shine baki sanar dani tin a waya ba.. Ni wllhi indai hakane kar Ki sake neman shawari daga wajena.. Kije can ki k’arata da sanyin zuciyarki aita cutanki bak’in ciki ya turaki rami.. Idan kin canza shawri kya nemeni.. Ni Kinga tafiyata..”
Bata ida rufe baki ba sukaji kukan Sabeera na tashi Babanta rik’e da Ita yana fad’in ta gama rashin kunya daga yau..
A tare Maman Sabeera da Ramatu suka nufo parlorn.
Sabeera ta fad’a bayan mahaifiyarta a guje tana kuka.. Yayinda Babanta yaci gaba da aza babbar riga yana k’ok’arin ciro igiyar decoder yake fad’in “Har ni zakije ki wulak’anta.. Kije kici wa matar da zan aura mutunci sabida bakida hankali.. Yau zakiji a jikinki..”
Ramatu kaw yab’e baki saitin kunnen Maman Sabeera Ta rad’a mata“K’awata ni na wuce kafin mijinki ya had’a dani yace ni ce uwar zigi..”
Maman Sabeera da tuni Hawaye ya wanke mata fuska Ta tare d’iyarta tai tana fad’in “Wllhi bazan Barka ka daketa ba..” Lokaci guda ta tura Sabeerar d’akinta ta maida k’ofa ta rufe.. Tare k’ofar d’akin tai tana hawaye alamun bazata barsa ya shige ya daki Sabeera ba..
Sai sakin huci yake yana duban Maman Sabeera yana fad’in “Rahina ki bani hanya na koya ma yarinyar nan tarbiya.. Tarbiyar da kika kasa bata..”
Cikin zuban hawaye Maman Sabeera ke dubansa, lokaci guda take furta “Wane tarbiya kake magana..? Wane tarbiya ne zaka bata wanda na gaza bata..? Tarbiyar rufeta a gida ka hanata fita Ko k’ofa dan kana tsoron kar a lalata maka Ita Ko mai..?”
Da tsananin mamaki yake dubanta “Rahina kike fad’awa magana irin haka.. Kina cikin hankalinki Rahina..? Dan kawai nazo da batun zan k’ara aure sai ki nemi ki jefeni da sharri..!”
Cikin zuban hawaye Maman Sabeera ke fad’in “Ni ban jefeka da sharri ba, sannan ban tab’a zarginka da aikata abu maras kyau waje ba, na sani idan kana gida Kai nawa ne amma idan ka fice zaka iya zama na kowa idan ka zab’a hakan.. Saidai ka Sani yaran nan kanadasu.. Idan ka lalata na wani ko cikin Tandu kake saka Naka ka b’oye wllhi sai an rama irin abinda kayi ma na wasu akansu..”
Katseta yai da fad’in “Anya Rahina kina cikin hankalinki.? Ni kike yab’awa magana dan nace zanyi aure.. Toh bari kiji na fad’a miki Asabar d’in mai zuwa d’aurin aurena tareda Sadiya, Idan an kawota idan Kinga dama kar ki zauna..”
Da tsananin mamaki Maman Sabeera ke dubansa hawaye basu daina zarya saman fuskarta ba “Aure kace.. Aure wannan asabar d’in.. Yarinyar da kak’i jinin alak’arsu da Sabeera shine zaka zago kace ita zaka aura nan da kwanaki biyu rak..” Tai maganar tana mai d’ago yatsun ta guda biyu hawaye na gangaro mata..
Cikin sanyin jiki Ta nufi d’akinta ta maido k’ofa ta rufe ba tareda ta kuma cewa komai ba, amma kam kaida gani kasan da zata samu ta fidda bak’in cikin dake k’unshe cikin k’irjinta ko ta hanyar kuka ne da Ta d’an ji sanyi cikin zuciyarta.
Tsaki Alhaji Isyaku ya buga yana fad’in “Aikin banza aikin wofi.. Ni ma na tsaya Ina miki bayani.. Idan na aurota idan kinga dama kar ki zauna a gidan.. Aure kuma babu fashi.” Ya juyo ya dubi k’ofan d’akin Sabeera yace “Ke kuma k’ofa na kumaji kin lek’a balle har kije kici mutuncin matata sai na aurar dake sadaka a masallaci..” Daga haka sa kai yai ya fice daga gidan fuu kaman zai tashi sama yana aza babbar rigarsa.
**
Umma ce tai k’arfin halin cewa “A’a Sabeera kece tafe.. Sannu da zuwa.. K’araso ki zauna.”
Ko gizau Sabeera batai ba saima duban Sadiya da take. Umma ta dubi Sadiya ta kuma dubi Sabeeran da irin kallon da take ma Sadiya. Kafin Umma tai wani aune Sabeera ta k’araso ta duk’a yanda Sadiya ke duk’e suna fuskantar juna saidai kan Sadiyar a k’asa yake.
“Ki fad’a mun gaskiya da bakinki.. Shin da gaske ne..? Sadiya da gaske ne abinda nake ji tsakaninki da mahaifina..?!”
Izuwa lokacin hawaye sun soma ambaliya saman fuskar Sadiya, ta kasa d’agowa ta dubi Sabeera sai hawaye dake zarya saman fuskarta.
Cikin zuban hawaye da tsananin d’aga murya Sabeeran ke ci gaba da fad’in “Talk to me Sadiya.. Tell me the truth.! Ki fad’a mun gaskiya.. Wacece ke a wajen mahaifina..! Ki fad’a mun Sadiya..!!” Ta k’arashe tana damk’o kafad’un Sadiya tana mai jijjigata da iya k’arfinta hawaye na ambaliya saman fuskarta a yayinda kukan Sadiyar ma ya k’aru.
Umma dake gefe ta kasa tab’uka komai sai hawayen da itama taji suna zubo mata.
Cikin muryar kuka ba tareda ta d’ago ta dubi Sabeeran ba take furta “I’m sorry.. I’m sorry Sabeera.. Please forgive me.. Dan Allah ki yafe mun..!”
Take jikin Sabeera ya sake gaba d’aya.. Maiyasa Sadiya take bata hak’uri.. Kenan da gaske ne.. Kenan maganganun da mutane suke fad’i gaskiya ne.. Sadiya da mahaifinta... Ji tai Ta kasa k’arasa tunanin sabida wani irin jiwa dataji na neman kaita k’asa. Take taji wani irin k’arfi yazo mata.. Ta hankad’a Sadiyar da k’arfin gaske Wanda saida ya kaita k’asa.. Sadiya ta buga kanta had’ida gwiwan hannunta da tuni ya karje ya soma jini.. Babu shiri Umma ta mik’e da k’yar dikda k’afarta dake mata ciwo Ta nufi kan d’iyarta.
Sabeera ta kuma yowa kan Sadiyar tana kuka sosai take fad’in “Sai na kasheki kafin ki zama matar Babana..!” Tayo kanta tana k’ok’arin fuzgota saidai tuni Umma ta raba tsakaninsu ta tallafi Sadiyar dake kuka sosai tana duban Sabeera dake k’ok’arin funcikota..
Cikin kuka Sabeera ke furta “I trusted you.. I believed in you.. I never doubted you.. I never judged you.. Duk abinda mutane zasu fad’i akanki Sadiya dai dai da rana guda ban tab’a yarda ba.. Ashe duk ba haka bane.. Ashe ked’in da gaske macijiyace mai bak’in guba.. Ta yaya zaki min haka.. Ta yaya zaki aminiyar data aminta dake irin haka Sadiya..!” Ta kuma yowa kanta tana kuma janyota tana fad’in sai tayi ajalinta.
Daidai lokacin Baban Sabeera ya shigo da shopping bags hannunsa, nan ya tadda wannan hargitsi dake tashi cikin gidansu Sadiyar.
Da tsananin mamaki yake duban Sabeera dake k’ok’arin kaima Sadiya duka Umma na tarewa.
“Ke Sabeeraa.!!” Ya fad’i cikin daka tsawa yana mai fuzgo Sabeeran had’ida d’aura mata mari maiji da lafiya..
Sabeera ta tsaya Cak tana duban mahaifin nata cikeda tsananin mamaki hannunta guda dafe da k’uncinta.
Sadiya kaw tuni ta rungume mahaifiyarta tana kuka sosai..
“Dan gidanku ashe bakida hankali.. Ashe ke shashasha ce ban Sani ba.. Uban wa ma ya baki izinin fitowa daga gida.. Matar nawa zaki daka dan bakida kunya bakida hankali Ko..!”
Baki sake kurum Sabeera ke duban mahaifinta da kalaman da yake, tana ganin kaman mafarki take ba gaskiya bane.. Tanada tabbacin ba don zafin sauk’ar marin dataji a k’uncinta ba zata iya cewa mafarki take ba gaskiya bane..
A guje Sadiya dake tsananin kuka ta shige parlor yayinda Baban Sabeera yai yunk’urin bin bayanta yana fad’in “Baby.. Baby kiyi hak’uri dan Allah I’ll deal with her myself..”
Cikin hawaye Umma Ta katsesa da fad’in “Ya isa dan Allah..!” Tai saurin bin bayan Sadiya tana ambato sunata ga k’annenta da tuni sun fito suna kallon abinda ke faruwa.
Baban Sabeera kaw hannunta ya damk’o yana fad’in “Shige muje ki sanar dani ubanda ya koya miki rashin kunya..”
Haka ‘yan lungun sukaita lek’e wasu na k’us k’us d’in an fara dan kaf lungun gidansu Sadiya ne bai rabuwa da hatsaniya da tashin hankali.. Daga wannan sai wancan..
Sadiya kam kulle kanta tai a d’aki tana kuka sosai kaman ranta zai fice.
A b’angaren Maman Sabeera kaw Ramatu tazo sun k’ule a d’aki suna tattauna lamarin tareda neman mafita.
Ramatu Ta nusa tace “Ai wllhi Rahina Kema da naki, idan b’era da sata daddawa da wari.. Ni tin yaushe nace ki raba ‘yarki da wannan yarinya Sadiya mai shegen kyau kaman aljana.. Wannan yarinyar tana shigo miki gida Ta shnatak’e kaman gidan Ubanta, santaleliyar yarinya irin wannan kice min mijinki bazai d’aura idanu kanta ba..”
Maman Sabeera tace “Wllhi Ramatu ban tab’a kawo haka ba tinda naga bama ya son alak’arsu.. Kuma ni ban tab’a yarda yarinyar lalatacciya bace kaman yanda ake cewa _Never judge a Book by its cover_ toh ban tab’a munana ma yarinyar nan zato ba dan wataran wanda kake zaton mutumin kirki ne bashi ne mutumin kirkin ba, wanda kayi zaton na banza ne sai kaga shine mutumin kirkin.. Ni da har ina sha’awanta ma Abdallah (yayan Sabeera dake karatu k’asar waje..) Amma ni koda wasa ban zaci Wai Alhaji zai d’aura idanu kanta ba...Yayi aurensa ni bazan hanasa ba ya auri ko wacece amma kam banda Sadiya k’awar Sabeera... Ina zan Kai wannan d’imbin bak’in ciki da tashin hankali ga uwa uba Sabeera taji komai..”
Ramatu ta tab’e baki tace “Rahina zama fah bai ganki ba, tashi zakiyi muje har gidansu yarinyar nan muci uban uwarta da kyau dan itace tsararmu ba d’iyarta ba.. Ki daina wannan simi simi d’in nan naki ki tashi ki karb’a ma kanki da yaranki ‘yanci idan kuma ba haka ba ki zuba ido ki zama ‘yar kallo cikin gidanki.. Kinaji kina gani yarinya ‘yar cikinki Ta k’unsa miki bak’in ciki. Keda gidanki yafi k’arfinki.”
“Ramatu sanin kanki ne ban isa na hana namiji son mata ba dan a halittarsu ne amma damuwar shine kar ya nemi na banza, yayi auren dan shine mafi a’ala tinda Allah ya huwace masa daman auren mace sama da guda. Sannan ni idan zai auren ya auro ko wacece amma tsakani ga Allah banda Sadiya.. Idan ni zan iya jura Sabeera fah.. Sabeera bazata iya jura ba.. Ni wllhi tashin hankalin da ‘yata zata shiga nake tunani.. Yaran nan fah bacci ne ke rabasu sanda suke makaranta kafin su tafi yajin aiki har karatu tare suke..”
Ramatu Ta katse Ta da fad’in “Ni dan Allah kin isheni, kin cika ni da surutun da babu gaira babu dalili.. Dik kin San da wannan shine kika d’add’agoni ko karin kummalo banyi ma mijina ba.. Dama Kinsan wa’azi zaki kirani kimin shine baki sanar dani tin a waya ba.. Ni wllhi indai hakane kar Ki sake neman shawari daga wajena.. Kije can ki k’arata da sanyin zuciyarki aita cutanki bak’in ciki ya turaki rami.. Idan kin canza shawri kya nemeni.. Ni Kinga tafiyata..”
Bata ida rufe baki ba sukaji kukan Sabeera na tashi Babanta rik’e da Ita yana fad’in ta gama rashin kunya daga yau..
A tare Maman Sabeera da Ramatu suka nufo parlorn.
Sabeera ta fad’a bayan mahaifiyarta a guje tana kuka.. Yayinda Babanta yaci gaba da aza babbar riga yana k’ok’arin ciro igiyar decoder yake fad’in “Har ni zakije ki wulak’anta.. Kije kici wa matar da zan aura mutunci sabida bakida hankali.. Yau zakiji a jikinki..”
Ramatu kaw yab’e baki saitin kunnen Maman Sabeera Ta rad’a mata“K’awata ni na wuce kafin mijinki ya had’a dani yace ni ce uwar zigi..”
Maman Sabeera da tuni Hawaye ya wanke mata fuska Ta tare d’iyarta tai tana fad’in “Wllhi bazan Barka ka daketa ba..” Lokaci guda ta tura Sabeerar d’akinta ta maida k’ofa ta rufe.. Tare k’ofar d’akin tai tana hawaye alamun bazata barsa ya shige ya daki Sabeera ba..
Sai sakin huci yake yana duban Maman Sabeera yana fad’in “Rahina ki bani hanya na koya ma yarinyar nan tarbiya.. Tarbiyar da kika kasa bata..”
Cikin zuban hawaye Maman Sabeera ke dubansa, lokaci guda take furta “Wane tarbiya kake magana..? Wane tarbiya ne zaka bata wanda na gaza bata..? Tarbiyar rufeta a gida ka hanata fita Ko k’ofa dan kana tsoron kar a lalata maka Ita Ko mai..?”
Da tsananin mamaki yake dubanta “Rahina kike fad’awa magana irin haka.. Kina cikin hankalinki Rahina..? Dan kawai nazo da batun zan k’ara aure sai ki nemi ki jefeni da sharri..!”
Cikin zuban hawaye Maman Sabeera ke fad’in “Ni ban jefeka da sharri ba, sannan ban tab’a zarginka da aikata abu maras kyau waje ba, na sani idan kana gida Kai nawa ne amma idan ka fice zaka iya zama na kowa idan ka zab’a hakan.. Saidai ka Sani yaran nan kanadasu.. Idan ka lalata na wani ko cikin Tandu kake saka Naka ka b’oye wllhi sai an rama irin abinda kayi ma na wasu akansu..”
Katseta yai da fad’in “Anya Rahina kina cikin hankalinki.? Ni kike yab’awa magana dan nace zanyi aure.. Toh bari kiji na fad’a miki Asabar d’in mai zuwa d’aurin aurena tareda Sadiya, Idan an kawota idan Kinga dama kar ki zauna..”
Da tsananin mamaki Maman Sabeera ke dubansa hawaye basu daina zarya saman fuskarta ba “Aure kace.. Aure wannan asabar d’in.. Yarinyar da kak’i jinin alak’arsu da Sabeera shine zaka zago kace ita zaka aura nan da kwanaki biyu rak..” Tai maganar tana mai d’ago yatsun ta guda biyu hawaye na gangaro mata..
Cikin sanyin jiki Ta nufi d’akinta ta maido k’ofa ta rufe ba tareda ta kuma cewa komai ba, amma kam kaida gani kasan da zata samu ta fidda bak’in cikin dake k’unshe cikin k’irjinta ko ta hanyar kuka ne da Ta d’an ji sanyi cikin zuciyarta.
Tsaki Alhaji Isyaku ya buga yana fad’in “Aikin banza aikin wofi.. Ni ma na tsaya Ina miki bayani.. Idan na aurota idan kinga dama kar ki zauna a gidan.. Aure kuma babu fashi.” Ya juyo ya dubi k’ofan d’akin Sabeera yace “Ke kuma k’ofa na kumaji kin lek’a balle har kije kici mutuncin matata sai na aurar dake sadaka a masallaci..” Daga haka sa kai yai ya fice daga gidan fuu kaman zai tashi sama yana aza babbar rigarsa.
**