Sashe 56
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin sauri Meema ta jinjina kai ta shige mota ta d’auko ledar ultra d’in.
Police man d’in dake gate ya bud’e yana duban Meema da Safeenah da mamaki.. Kafin yai magana Safeenah ta d’aga crutch d’inta ta shiga rabza masa aka kaman Allah ne ya aikota.. Dik k’ok’arin sa ganin ya hanasu shiga abu yaci tura dan Safeenah hauka tuburan take nunawa. Daidai lokacin Kiki ta k’araso ta ceci Police man d’in da k’yar wanda tuni jini ya soma zubowa daga goshinsa Sabida k’arafan da Safeenah ta dinga rabza masa.
A haka suka nufi gidan Safeenah na sakin huci tana duban fad’in gidan da kalan cin amanar da mijinta Mu’azzam yai mata.. Gidanta ne amma wata ‘yar iska ce ciki har yana kiranta da matarsa.
Suna isa ta shiga bugun k’ofar parlorn da iyaka k’arfinta.
Sadiya da har lokacin tak’ure take waje guda tana kukan rashin sanin ina ahalinta suke kaman daga sama taji ana bugun k’ofar.. A d’ari ta mik’e ta nufi k’ofar dan a zatonta Mu’azzam ne ya dawo mata da labari mai dad’i ta bud’e tana fad’in “Have you found them already..!” Cak ta tsaya ganin ba Mu’azzam bane wasu ‘yanmata ne guda biyu.. Take ta juya tana kallon hoton auren Safeenah da Mu’azzam, nan ta fahimci matarsa ce wannan.. D’ayar kuma taso ganeta ta rasa a ina ne.. Lokaci guda ta tuna Sune ‘yanmatan da suka tab’a had’uwa dasu a Police Headquarters har suka take mata k’afar Umma da tayar Mota.
Sud’inma dubanta suke suna son d’ago ina suka tab’a ganinta.. Meema ce ta soma d’ago hannu tana nunata alamun ta ganeta.
“Addah Feenah itace.. Itace wacce muka bugesu a k’ofar police headquarters last two weeks itada wata mata.. Ta saba binsa har wajen aiki..!”
Ai Meema bata kai aya ba Safeenah dake tsananin huci tana duban Sadiya ta yunk’ura takai mata wata jahilar mari.. Saidai Sadiya bata bari marin ya sauk’a a fuskarta ba Ta rik’e hannun Feenah tana sakin huci itama.. Tin kafin Feenah takai hannunta k’asa Sadiya Ta maida mata Martanin marinta tasss..! Lokaci guda take nunata da yatsa tana fad’in “Wannan shine sakamakon take mun k’afar mahaifiya da kikayi da Mota..!”
Kan uban can.! Safeenah tai tsaye tana dubanta dafe da k’uncinta. Meema ma kame baki tai tana duban Sadiya data kashe Safeenah da mari mai lafiya har cikin gidanta..
“Idan ban kasheki yau ba sunana ba Safeenah Marwan Gamji ba.. Sai nayi ajalinki shegiya Karuwa..!”
Tana ida fad’in haka ta shiga kokawan janyo Sadiya sabida k’afarta dake da ciwo yasa batai nasaran capketa ba takai mata duka da sandar hannunta Ta kauce.. Lokaci guda Safeenah ke fad’i da Meema “Tare mun shegiya Meema kar ki barta ta fice..!”
Daidai lokacin Kiki ta shigo Safeenah tace su toshe mata Sadiya..
Sarkin yawa yafi Sarkin k’arfi aiko Meema dake duk Ta fisu jiki dama tuni ta k’arasa ta had’e Sadiya jikin garu ta matseta sosai Safeenah na fad’iwa Kiki Ta taimakawa Meema.. Kiki ta k’araso ta saka ma Meema hannu suka danne Sadiya a k’asa. Safeenah na huci ta b’arke ledar ultra d’in ta shiga turawa bakin Sadiya tana fad’in “Sai kin cinye yau tas dan uwarki.. Shegiya Karuwa sauran kwalta mai bin mazan mutane.. Yau sai kinyi nadaman sanin mijina da kikai har kika yarda ya kawoki gidana ya ajiye..”
Sadiya tana kiciniyar k’watan kanta fa Safeenah na tura mata sanitary pad cikin bakinta.. Kiki Ta sunkuya saitin kunnen Sadiyar ta rad’a mata a hankali “Zan sakeki kiyi k’ok’ari ki tura Meema batada wani balance sai ki gudu..”
Safeenah ta kamo sumar Kiki tana fad’in “Mai kike fad’a mata munafuka..!”
Daidai lokacin Kiki ta saki Sadiya ta taimaka mata suka hankad’a Meema ta fad’i gefe tana sakin k’ara.. A guje Sadiya ta nufi upstairs ya maida k’ofa ta rufe..
Safeenah tayo kan Kiki zata jibga wayar Meema ya soma ringing dan dik tashin hankali da Meema zata shiga bata rabo da wayarta.. Kiki ce ta k’arasa ta d’auka dan Meema kam ta kasa tashi tana nan zube wajen tana ihun k’afarta.
Ganin Aunty Shemau ce mai kira ya sanya Kiki Saurin d’agawa..
Cikin rawar murya Kiki ke fad’in “How’s Daddy doing Aunty Shema..? Alright gamu nan zuwa..!”
Ta juyo tana duban ‘yanuwan nata sai kuma ta fashe da kuka tana fad’in “Daddy ne.. Daddy babu lafiya.. Aunty Shemau ce ta kira tace maza muje gida yanzun nan..”
Babu shiri Safeenah ta finciki wayar tai jifa dashi “Babu yanda zamuje sai na kashe shegiyar nan..!”
Meema ta mik’e da k’yar tana fad’in “Toh wllhi saidai kiyi ke kad’ai Addah Feenah.. What if Daddy ya mutu muna tsaye a nan.. Kiki shige muje I want to see Daddy..!” Ta k’arashe tana kamo Kikin cikin d’ingishi.
Safeenah ta d’aga ido tana duban upstairs d’in “This is far from over..! Zan dawo dan Ubanki.. Kuma sai na kashe ki..!” Daga haka ta janyo crutches d’inta ta nufo bayansu.. Saidai suna fitowa sukaga d’akin karnukan a bud’e. Aiko nan karnukan suka soma haushi.. A d’ari suka arce suka nufo gate a guje suna ihu.. Harta Safeenah watsar da Crutches d’inta tai ta fito a guje.. har suna bangaje police d’in dake gate.. Dik gudun nan basu san k’ofar d’akin karnukan bane kawai a bud’e amma suna d’aure da chain d’insu.
Police d’in ya tattaro sandunan Safeenah ya mik’a masu cikin Mota yace a sauk’a lafiya.. Aka barsa da kumburarren goshi yanda Safeenah ta jibgesa da sanda.
**
CID
Bayan wayar tai chaji suka soma binkicen k’wak’waf cikin wayar. Suka soma Retrieving dik wani sak’o ko kira da aka fitar daga kan wayar. Lamba d’aya suka samu cikin wayar da kuma kan SIM card din, sannan wannan lambar ita kad’ai aka tab’a contacting da SIM card d’in.. Sannan sak’o d’aya ce aka tura da wayar kuma ma lamba d’aya tak aka tura sak’on.. Sak’on Address ne aka tura da wayar. Location d’in da aka sami gawar Ikram da Sagir.
Mu’azzam idanunsa sukai jazir yana karanta sak’on. Lokaci guda Assad ke fad’in “Let’s see idan zamu iya tracking lambar da aka aika ma sak’on..!”
Bai Kai aya ba Mu’azzam da gumi ke tsartsafo masa yace ya basa wayar. Babu musu Assad ya mik’a masa duk suka zuba masa idanu.
K’ura ma lambar da aka turama sak’on ido yai yana duban digits d’in yana karantsrsu one by one.. He’s familiar with number, for sure yasan wannan lambar... D’aukan lambar yai cikin wayarsa ya soma dialing yana jin bugun zuciyarsa na ninkuwa.
Sunan da ya fito masa b’oro b’oro saman screen d’insa shine ya sanyasa tsayawa Cak yana duban fuskar wayar tasa, lokaci guda yana jin duniyar na juya masa.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*31*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ji yai k’afafunsa suna barazanar kasa d’aukarsa, lokaci guda zuciyarsa na barazanar tarwatsewa.
Assad Yusuf harma da Maleeka mik’ewa sukai suna dubansa cikin tsananin kad’uwa da tashin hankali. Zasu iya cewa yanayin da suka gansa ciki basu tab’a ganinsa cikin irin yanayin a baya ba.
Assad ya matso yana jijjiga Mu’azzam wanda ya koma tamkar mutum mutumi “Mu’azzam.. Mu’azzam lafiya.. What’s wrong Mu’azzam..?!”
Mu’azzam bai iya amsa Sa ba sai zuba masa rinannun idanunsa da yai yana dubansa har lokacin takara bashi a duniyar haka yake jinsa.
Wayar hannunsa Assad ya amsa nan yaga sunan Safeenah ya bayyana saman wayar. Yusuf da Maleeka suka dubi juna bayan sunga sunan da fuskar wayar Mu’azzam ya nuna.
Lokaci guda Yusuf yai alamawa Maleeka da idanu cewa su fice. Babu musu Maleeka tabi umarnin Yusuf suka fice daga d’akin.
Gijif haka Mu’azzam ya zauna saman kujera idanunsa na k’ok’arin kawo ruwa . Cikin wane irin murya mai gauraye da tashin hankali had’ida rud’ani yake furta “It’s Safeenah’s phone number Assad..! That text message...was sent to her.!”
Ya d’ago yana duban Assad wanda tsananin shock shima ya nuna a fuskarsa, lokaci guda Mu’azzam yaci gaba da fad’in “But Assad how’s this possible..? I mean.. Safeenah is my blood.. And Ikram... Ikram was like a sister to her...!” Ya mik’e yana girgiza kai yana duban Assad d’in yake damk’e wayar Sagir cikin hannunsa, lokaci guda yake jijjiga wayar yana fad’in “Assad lambar matata.. Matata Assad, sak’on ma ita aka tura.. She couldn’t have killed my sister right..?!” Yanda yake maganar zaka fahimci yana cikin tsananin rud’ani ne da tashin hankali.
Kamo kafad’unsa Assad yai ya zaunarsa saman kujera yana k’ok’arin calming nasa “Please try to calm down Mu’azzam.”
D’ago idanu yai yana duban Assad d’in wanda gaba d’aya shima ya zama lost and confused.
Kauda Kai gefe kad’an Mu’azzam yai yana tinanin abubuwan da suka faru tun bayan rasa Ikram, lokaci guda yana dunk’ule hannayesa yana murzasu.
Assad ya d’an shafi kansa kad’an yana duban Mu’azzam d’in cikeda tausayawa. Fuzar da fuci yai kafin ya isa jikin window cikin rashin sanin abinda zai fad’iwa abokin nasa.. Tabbas Mu’azzam yana cikin yanayi mai matuk’ar wahala. Ace kana bincike kwatsam sai ka samu Matarka itace prime suspect na binciken da kake.. Kuma k’anwarka ce aka kashe sannan matarka ‘yaruwarka ta zamto Prime suspect.. Tabbas al’amarin akwai matuk’ar tashin hankali.
K’ok’arin saita kanta Assad yai kafin ya nufo Mu’azzam d’in wanda har lokaci ke zaune ya k’ura ma waje guda rinannun idanunsa.
Lokaci guda Mu’azzam d’in ke furta “All this while.. The killer’s right in front of me. Makashiyar tana nan a gabana.. Ina can inata neman makashin ba tareda sanin tana nan tare dani ba.. Claiming to be my wife.. wacce tafi kowa kusanci a gareni bayan mahaifiyata..”
Ya d’ago idonsa wanda siririn hawaye ke gangarowa daga ciki yana duban Assad. Lokaci guda yaci gaba da furta “She killed my sister Assad, and then she acts innocent.. Like she was also grieving for Ikram’s death.. She made me look like a complete idiot. Ina can inata bincike kaman wani wawa.. Tanata toshe duk wani hanyar da zanbi na samu gaskiya.. Assad she insulted my profession, you know.!”
Saurin dafasa Assad yai yana fad’in “Try to calm down first.. please Mu’azzam..”
Police man d’in dake gate ya bud’e yana duban Meema da Safeenah da mamaki.. Kafin yai magana Safeenah ta d’aga crutch d’inta ta shiga rabza masa aka kaman Allah ne ya aikota.. Dik k’ok’arin sa ganin ya hanasu shiga abu yaci tura dan Safeenah hauka tuburan take nunawa. Daidai lokacin Kiki ta k’araso ta ceci Police man d’in da k’yar wanda tuni jini ya soma zubowa daga goshinsa Sabida k’arafan da Safeenah ta dinga rabza masa.
A haka suka nufi gidan Safeenah na sakin huci tana duban fad’in gidan da kalan cin amanar da mijinta Mu’azzam yai mata.. Gidanta ne amma wata ‘yar iska ce ciki har yana kiranta da matarsa.
Suna isa ta shiga bugun k’ofar parlorn da iyaka k’arfinta.
Sadiya da har lokacin tak’ure take waje guda tana kukan rashin sanin ina ahalinta suke kaman daga sama taji ana bugun k’ofar.. A d’ari ta mik’e ta nufi k’ofar dan a zatonta Mu’azzam ne ya dawo mata da labari mai dad’i ta bud’e tana fad’in “Have you found them already..!” Cak ta tsaya ganin ba Mu’azzam bane wasu ‘yanmata ne guda biyu.. Take ta juya tana kallon hoton auren Safeenah da Mu’azzam, nan ta fahimci matarsa ce wannan.. D’ayar kuma taso ganeta ta rasa a ina ne.. Lokaci guda ta tuna Sune ‘yanmatan da suka tab’a had’uwa dasu a Police Headquarters har suka take mata k’afar Umma da tayar Mota.
Sud’inma dubanta suke suna son d’ago ina suka tab’a ganinta.. Meema ce ta soma d’ago hannu tana nunata alamun ta ganeta.
“Addah Feenah itace.. Itace wacce muka bugesu a k’ofar police headquarters last two weeks itada wata mata.. Ta saba binsa har wajen aiki..!”
Ai Meema bata kai aya ba Safeenah dake tsananin huci tana duban Sadiya ta yunk’ura takai mata wata jahilar mari.. Saidai Sadiya bata bari marin ya sauk’a a fuskarta ba Ta rik’e hannun Feenah tana sakin huci itama.. Tin kafin Feenah takai hannunta k’asa Sadiya Ta maida mata Martanin marinta tasss..! Lokaci guda take nunata da yatsa tana fad’in “Wannan shine sakamakon take mun k’afar mahaifiya da kikayi da Mota..!”
Kan uban can.! Safeenah tai tsaye tana dubanta dafe da k’uncinta. Meema ma kame baki tai tana duban Sadiya data kashe Safeenah da mari mai lafiya har cikin gidanta..
“Idan ban kasheki yau ba sunana ba Safeenah Marwan Gamji ba.. Sai nayi ajalinki shegiya Karuwa..!”
Tana ida fad’in haka ta shiga kokawan janyo Sadiya sabida k’afarta dake da ciwo yasa batai nasaran capketa ba takai mata duka da sandar hannunta Ta kauce.. Lokaci guda Safeenah ke fad’i da Meema “Tare mun shegiya Meema kar ki barta ta fice..!”
Daidai lokacin Kiki ta shigo Safeenah tace su toshe mata Sadiya..
Sarkin yawa yafi Sarkin k’arfi aiko Meema dake duk Ta fisu jiki dama tuni ta k’arasa ta had’e Sadiya jikin garu ta matseta sosai Safeenah na fad’iwa Kiki Ta taimakawa Meema.. Kiki ta k’araso ta saka ma Meema hannu suka danne Sadiya a k’asa. Safeenah na huci ta b’arke ledar ultra d’in ta shiga turawa bakin Sadiya tana fad’in “Sai kin cinye yau tas dan uwarki.. Shegiya Karuwa sauran kwalta mai bin mazan mutane.. Yau sai kinyi nadaman sanin mijina da kikai har kika yarda ya kawoki gidana ya ajiye..”
Sadiya tana kiciniyar k’watan kanta fa Safeenah na tura mata sanitary pad cikin bakinta.. Kiki Ta sunkuya saitin kunnen Sadiyar ta rad’a mata a hankali “Zan sakeki kiyi k’ok’ari ki tura Meema batada wani balance sai ki gudu..”
Safeenah ta kamo sumar Kiki tana fad’in “Mai kike fad’a mata munafuka..!”
Daidai lokacin Kiki ta saki Sadiya ta taimaka mata suka hankad’a Meema ta fad’i gefe tana sakin k’ara.. A guje Sadiya ta nufi upstairs ya maida k’ofa ta rufe..
Safeenah tayo kan Kiki zata jibga wayar Meema ya soma ringing dan dik tashin hankali da Meema zata shiga bata rabo da wayarta.. Kiki ce ta k’arasa ta d’auka dan Meema kam ta kasa tashi tana nan zube wajen tana ihun k’afarta.
Ganin Aunty Shemau ce mai kira ya sanya Kiki Saurin d’agawa..
Cikin rawar murya Kiki ke fad’in “How’s Daddy doing Aunty Shema..? Alright gamu nan zuwa..!”
Ta juyo tana duban ‘yanuwan nata sai kuma ta fashe da kuka tana fad’in “Daddy ne.. Daddy babu lafiya.. Aunty Shemau ce ta kira tace maza muje gida yanzun nan..”
Babu shiri Safeenah ta finciki wayar tai jifa dashi “Babu yanda zamuje sai na kashe shegiyar nan..!”
Meema ta mik’e da k’yar tana fad’in “Toh wllhi saidai kiyi ke kad’ai Addah Feenah.. What if Daddy ya mutu muna tsaye a nan.. Kiki shige muje I want to see Daddy..!” Ta k’arashe tana kamo Kikin cikin d’ingishi.
Safeenah ta d’aga ido tana duban upstairs d’in “This is far from over..! Zan dawo dan Ubanki.. Kuma sai na kashe ki..!” Daga haka ta janyo crutches d’inta ta nufo bayansu.. Saidai suna fitowa sukaga d’akin karnukan a bud’e. Aiko nan karnukan suka soma haushi.. A d’ari suka arce suka nufo gate a guje suna ihu.. Harta Safeenah watsar da Crutches d’inta tai ta fito a guje.. har suna bangaje police d’in dake gate.. Dik gudun nan basu san k’ofar d’akin karnukan bane kawai a bud’e amma suna d’aure da chain d’insu.
Police d’in ya tattaro sandunan Safeenah ya mik’a masu cikin Mota yace a sauk’a lafiya.. Aka barsa da kumburarren goshi yanda Safeenah ta jibgesa da sanda.
**
CID
Bayan wayar tai chaji suka soma binkicen k’wak’waf cikin wayar. Suka soma Retrieving dik wani sak’o ko kira da aka fitar daga kan wayar. Lamba d’aya suka samu cikin wayar da kuma kan SIM card din, sannan wannan lambar ita kad’ai aka tab’a contacting da SIM card d’in.. Sannan sak’o d’aya ce aka tura da wayar kuma ma lamba d’aya tak aka tura sak’on.. Sak’on Address ne aka tura da wayar. Location d’in da aka sami gawar Ikram da Sagir.
Mu’azzam idanunsa sukai jazir yana karanta sak’on. Lokaci guda Assad ke fad’in “Let’s see idan zamu iya tracking lambar da aka aika ma sak’on..!”
Bai Kai aya ba Mu’azzam da gumi ke tsartsafo masa yace ya basa wayar. Babu musu Assad ya mik’a masa duk suka zuba masa idanu.
K’ura ma lambar da aka turama sak’on ido yai yana duban digits d’in yana karantsrsu one by one.. He’s familiar with number, for sure yasan wannan lambar... D’aukan lambar yai cikin wayarsa ya soma dialing yana jin bugun zuciyarsa na ninkuwa.
Sunan da ya fito masa b’oro b’oro saman screen d’insa shine ya sanyasa tsayawa Cak yana duban fuskar wayar tasa, lokaci guda yana jin duniyar na juya masa.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*31*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ji yai k’afafunsa suna barazanar kasa d’aukarsa, lokaci guda zuciyarsa na barazanar tarwatsewa.
Assad Yusuf harma da Maleeka mik’ewa sukai suna dubansa cikin tsananin kad’uwa da tashin hankali. Zasu iya cewa yanayin da suka gansa ciki basu tab’a ganinsa cikin irin yanayin a baya ba.
Assad ya matso yana jijjiga Mu’azzam wanda ya koma tamkar mutum mutumi “Mu’azzam.. Mu’azzam lafiya.. What’s wrong Mu’azzam..?!”
Mu’azzam bai iya amsa Sa ba sai zuba masa rinannun idanunsa da yai yana dubansa har lokacin takara bashi a duniyar haka yake jinsa.
Wayar hannunsa Assad ya amsa nan yaga sunan Safeenah ya bayyana saman wayar. Yusuf da Maleeka suka dubi juna bayan sunga sunan da fuskar wayar Mu’azzam ya nuna.
Lokaci guda Yusuf yai alamawa Maleeka da idanu cewa su fice. Babu musu Maleeka tabi umarnin Yusuf suka fice daga d’akin.
Gijif haka Mu’azzam ya zauna saman kujera idanunsa na k’ok’arin kawo ruwa . Cikin wane irin murya mai gauraye da tashin hankali had’ida rud’ani yake furta “It’s Safeenah’s phone number Assad..! That text message...was sent to her.!”
Ya d’ago yana duban Assad wanda tsananin shock shima ya nuna a fuskarsa, lokaci guda Mu’azzam yaci gaba da fad’in “But Assad how’s this possible..? I mean.. Safeenah is my blood.. And Ikram... Ikram was like a sister to her...!” Ya mik’e yana girgiza kai yana duban Assad d’in yake damk’e wayar Sagir cikin hannunsa, lokaci guda yake jijjiga wayar yana fad’in “Assad lambar matata.. Matata Assad, sak’on ma ita aka tura.. She couldn’t have killed my sister right..?!” Yanda yake maganar zaka fahimci yana cikin tsananin rud’ani ne da tashin hankali.
Kamo kafad’unsa Assad yai ya zaunarsa saman kujera yana k’ok’arin calming nasa “Please try to calm down Mu’azzam.”
D’ago idanu yai yana duban Assad d’in wanda gaba d’aya shima ya zama lost and confused.
Kauda Kai gefe kad’an Mu’azzam yai yana tinanin abubuwan da suka faru tun bayan rasa Ikram, lokaci guda yana dunk’ule hannayesa yana murzasu.
Assad ya d’an shafi kansa kad’an yana duban Mu’azzam d’in cikeda tausayawa. Fuzar da fuci yai kafin ya isa jikin window cikin rashin sanin abinda zai fad’iwa abokin nasa.. Tabbas Mu’azzam yana cikin yanayi mai matuk’ar wahala. Ace kana bincike kwatsam sai ka samu Matarka itace prime suspect na binciken da kake.. Kuma k’anwarka ce aka kashe sannan matarka ‘yaruwarka ta zamto Prime suspect.. Tabbas al’amarin akwai matuk’ar tashin hankali.
K’ok’arin saita kanta Assad yai kafin ya nufo Mu’azzam d’in wanda har lokaci ke zaune ya k’ura ma waje guda rinannun idanunsa.
Lokaci guda Mu’azzam d’in ke furta “All this while.. The killer’s right in front of me. Makashiyar tana nan a gabana.. Ina can inata neman makashin ba tareda sanin tana nan tare dani ba.. Claiming to be my wife.. wacce tafi kowa kusanci a gareni bayan mahaifiyata..”
Ya d’ago idonsa wanda siririn hawaye ke gangarowa daga ciki yana duban Assad. Lokaci guda yaci gaba da furta “She killed my sister Assad, and then she acts innocent.. Like she was also grieving for Ikram’s death.. She made me look like a complete idiot. Ina can inata bincike kaman wani wawa.. Tanata toshe duk wani hanyar da zanbi na samu gaskiya.. Assad she insulted my profession, you know.!”
Saurin dafasa Assad yai yana fad’in “Try to calm down first.. please Mu’azzam..”