Sashe 40
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuzar da huci Assad yai yace “Baka aikata komai ba Mu’azzam, amma kana shirin aikatawa, ka d’auko mutumin nan ba bisa k’aida ba kana interrogating nasa, and not only that. you’re forcing him to admit to the crime he’s not committed. Bayan cewa koda ya aikata laifin yanada damar da zai k’i yin magana har sai an barsa ya gana da lawyer d’insa..Anya Mu’azzam ka d’auko hanyar da zai b’ulle.. Don’t allow your anger to consume you.. Kabi komai a sannu.. I’m positive mutumin nan Iyakacin gaskiyarsa yake fad’i babu abinda ya Sani. Kaman yanda na fad’a maka he’s caught in the middle ne sabida auren yarinyar da ya tassama yi, Toh haka d’in ne.. Instead mu tsaya muna b’ata lokacinka kan tuhumarsa da neman mutanen da suka tassama kidnapping d’insa mukai.. Dan na tabbata babu abinda zamu samu wajen mutumin nan..”
Mu’azzam ya d’ago fuskarsa data rine zuwa ja sabida tsananin tashin hankali, lokaci guda ya shafi goshinsa da hannunsa guda kafin yace “Kai baka tunanin mutumin nan had’a baki sukai da mutanen da suka tassama sacesa.. Baka tunanin hakan na iya kasancewa cikin plan d’in Danger.. Danger is a very dangerous person Assad, he’s capable of everything.”
Assad ya jinjina kai yace “Na sani Danger is Dangerous, amma tambayar da zan maka a nan shine idan bakinsa d’aya da Danger Maiyasa zai sacesa.. Sannan idan bakinsa d’aya da Danger bazasu amshe kud’ad’en dake hannunsa ba..”
Mu’azzam ya zuba masa idanu kaman mai nazarin sai kuma ya murmusa yace “Kana magana as if you can’t read criminal minds and how smart they can act.. Yanzu dashi da Danger duk zasu iya shirya haka dan su karkatar da hankalin jami’an tsaro dan kawai abun yayi kaman Su d’in suna bibiyar Alhaji Isyaku ne sabida Auren Sadiya da yake yunk’urin yi.. I believe ka amince zasu aikata fiyeda haka.”
Assad ya nusa yace “Everything is possible in a situation like this saidai hanyar da ka d’auko zai iya sakamu cikin matsala gaba d’aya.. Maimakon muyi solving case d’in zamu iya b’ata komai da wannan hanyar daka biyo ba bisa k’a’ida ba..” Shiru Assad ya d’anyi yana mai tsaresa da idanu kafin yace “But wait, idan har kana tinanin Danger da mutumin nan bakinsu d’aya ne Maiyasa ka hana mutumin auren yarinyar..? Sannan Maiyasa kai ka aureta.. Kana tunanin zasu iya cutar da ita ne..?”
Shiru Mu’azzam bai basa amsa ba sai mugun kallon da yake aika masa. Lokaci guda Assad yaci gaba da jinjina kai yana fad’in “Now I get it.. Ka aureta ne to give her protection..!”
“O C’mon just shut up Assad..!”
Assad yaci gaba da fad’in “Yes gaskiya ne Mu’azzam dan ka bata kariya daga sharrin su Danger ka aureta.. Because she’s there target.. Ko baka fahimci hakan yanzu ba I’m positive gaba zaka fahimci haka.”
Da mugun mamaki Mu’azzam ke kallonsa yanaji yanda yake k’ok’arin k’irk’iro wani zance, kan mai zai bama wannan yarinyar protection Iyakacin abinda ya Sani shine he still needs her for his mission ne. Gajeren tsaki yai yana mai girgiza kai yake furta “You are not serious Assad. Bansan ya akai kake aiki k’ark’ashin NPF ba. You should be a clown and not a police officer..” Yana ida fad’in haka yasa kai ya koma cikin building d’in yanda Alhaji Isyaku ke zaune.
Assad ya take masa baya yana mai girgiza kai kad’an.
Suna k’arasowa Mu’azzam ya dubi Alhaji Isyaku yace “Alhaji zamu k’yaleka ka tafi.. Zamu maidaka Gida.. Motarka tana nan a waje wad’annan abokan aikin nawa sun taho maka da Ita nan.. Amma still idan kanaso zaka iya reporting ‘yanta’addan nan da suka tasamma saceka suka kuma sace maka kud’ad’enka.”
Alhaji Iskyaku Yai saurin girgiza kai yana mai zaro idanu yace “Ni wllhi bana fatan abinda zai had’ani da ‘‘yanta’addan nan, yo a k’asa irin wannan da aka maida satan mutum kaman an d’auke ‘ya’yan kaji ai abun na gode ma Allah ne da bai k’addari zan sha wahala hannun mutanen nan ba.. Kuma tinda na tsira Alhamdulillah.. Sannan wannan yarinya ko a k’afa aka d’aura mun ita zan kwance na gudu dan na kula tsautsayi da bala’i ke bibiyarsu.. Ban tab’a jin k’aran harbe harbe ba saida nace zan aureta.. Na gode maku matuk’a da ceton rayuwata da kukai..”
Assad ya mik’a masa hannu sukai musabaha kafin yace “Kar ka damu Alhaji, hakan aikinmu ne.. Kula da al’umman k’asa tsare masu rayuwarsu lafiyarsu harmada dukiyarsu.. Kuma kar ka damu da izinin Allah zamu gano mutanen da suka maka wannan aika aika and they will answer to the law. Ku daina karyar ma jami’an tsaron k’asar nan da fad’in cewa sun gaza Gwabnati ma sun gaza.. NPF tana iya k’ok’arinta a kullum domin taga Ta kawo k’arshen ta’addanci da rashin tsaron da ya addabi k’asar nan..A koda yaushe ku saka a ranku cewa mu ‘yansanda abokanku ne ba mak’iyanku ba.. Dukda cewa da yawa sun mana shaida cewa akasarin mu gurb’atattu ne ba haka abin yake ba domin kuwa akwai na k’warai a cikinmu.. Kaman dai ko wacce irin Sana’a akwai gurb’atattu akwai na K’warai..”
Alhaji Isyaku ya jinjina kai a hankali yana duban matashin D’ansandan. Lokaci guda ya kuma masu godiya kafin suka nufo waje gaba d’aya.
Suna fitowa waje Alhaji Isyaku ya kasa key ma Mota, jikinsa dik sai rawa yake.. Gani yake kaman ‘yantaddan zasu kuma dawowa.
Ya lek’o da kansa ta glass yana fad’in “Rankaidad’e ko zaku taimaka min dan Allah.. Wllhi ban iya tuk’a motar.”
Assad ya dubesa kafin ya dubi su Mu’azzam sai kuma yace da Alhaji Isyaku “I’ll drive you home Alhaji.”
Alhaji Isyaku cikeda jin dad’i yake godiya wa Assad “Na gode matuk’a yallab’ai, aikam bazan iya tuk’a mota ba dan har yanzu tsoro bai sakeni ba.. Gani nake kaman idan ina tafiya ‘Yantaddan nan zasu dawo.. Na gode na gode k’warai.”
Assad ya dubi Mu’azzam yai masa alama da hannu kan cewa zai kai Alhaji Isyaku gida. Jinjina masa kai kurum Mu’azzam yai kafin suka soma fitowa tareda su Yusuf suka nufi motocinsu suna basa update abinda ke faruwa a CID.
Shiru Mu’azzam yai yana nazarin abducting Alhaji Isyaku da aka tasamma Yi wanda baida haufi idan har Alhaji Isyaku baida wani connection da Danger Toh ko shakka babu masu bibiyan yarinyar ne suka kuskuresa. A fili ya furta “Danger..! Zan kamaka dik yanda ka shiga ka fita.. Da k’udurar Ubangiji.!”
K’aran shigowar sak’o cikin wayarsa da yaji ne ya sanyasa ciro wayar aljihu yana dubawa. Lamba ce Babu suna, sannan abinda kawai aka rubuta jikin sak’on shine _BAD_
Ya nanata alphabets d’in a hankali “BAD” sai kuma ya fad’a in word “Bad..!” Ya nanata yafi sau UKU. Lokaci guda ya yanke shawarin kiran lambar.. Kafin yakai ga kiran lambar wani sak’on ya sake shigo masa. Wannan karon ga abinda aka rubuta.
_BAD is your enemy_
A hankali ya kuma furtawa “Bad is your enemy”. Yai shiru yana kuma duba. What does this mean.?
Saurin sake danna kira yai amma wayar bata shiga, a kashe take.
Take wata sak’on Ta kuma shigo masa da wata lamba ta daban
_BAD is ruining your home._
Dafe kansa yai kad’an yana duban lambobin da aka turo masa wad’annan sak’on dasu wanda ko shakka babu wasa da hankalinsa mai turo sak’on yake shiyasa yake turo masa da lambobi barkatai dan kar yayi tunanin tracing lambobin.
Bai ida tinanin ba wani sak’on ya kuma shigowa da wani lamba daban duk dai akan BAD.
_BAD is very BAD_
A hankali ya fuzar da fuci yana duban lambobin kusan guda uku.
Cikin natsuwa ya nufi motarsa lokacin ana kiraye kirayen sallar magrib. Tinanin Bad bai daina Yawo a kwanyarsa ba. Yana driving yana nanata kalmar Bad.
Wata sak’on ta sake shigo masa da wata lamba daban duk dai akan bad
_You need to find BAD_
A fili Mu’azzam ya furta “Who are you BAD..?!”
**
A gidansu Sadiya kaw tana k’udundune a d’aki cikin bargo sai rawa jikinta yake alamun zazzab’i ya kuma rufeta, ko kukan ma ta kasa yi yanzu kam. Tabbas da ace zatai kukan da taji sa’ida cikin zuciyarta. Tana nan kwance tana kar karkarwa tana iya sauraro muryoyinsu daga tsakar gidan yanda yanda Malam Liman da Ummanta da shaidu guda uku suka had’u suna warware bashin da Tabawa ke binsu Wanda Wai mutumin da ya aureta ya biya masu.. Kuma Wai ba kowa bane wannan mutumin face d’asandan nan da Ta tabbata da zai iya samun daman harbeta da zai aikata hakan.. Ta yaya za’ace wannan mutumin shine mijinta.. Ta yaya za’ace an mata aure haka bagatatan saikace wata ‘yar tsana.. Shin talauci hauka ne kokuwa dai rashin mahaifinta ne yasa akai mata haka.. Allah sarki yau Ta kuma yarda cewa mahaifi Katanga ne mai k’arfi kan iyalansa duk talaucinsa da babunsa kuwa.. Ta tabbata da ace Abba yana nan sam bazai zuba idanu ai mata irin wannan auren ba.. Tabbas maraici akwai ciwo cikinsa.. Tabbas wanda bai d’and’ani d’acin maraici ba baisan rashi a rayuwa ba.. Yau taga ranan mahaifinta sannan taji ciwon rashin sa a gareta.. Gashi nan a aurar da ita saikace wata taguwar da aka ciwo a yak’i wacce batada wani daraja.. Wasu hawaye masu tsananin zafi suka zubo mata. Tana jin sanda Tabawa ke gud’a tana fad’in ta yarda k’wallan mangoro ta huta da k’uda.
Saida su Malam Liman da shaidu suka fara ficewa kafin Tabawa ta mak’ale kud’ad’enta ta fice.
A zauren gidan Tabawa Malam Liman da D’an Rakiyarsa Munkaila kuka tsaya suna jiran Tabawar.
Tabawa tana shigowa tai wani birki tana bada balance dan bataga alamun mutane ba da shike dare ne.
Rawanin Malam Liman ta hango ta gane sune.
“Ahh Haba Malam yo ai sai ka razanen.!”
Malam Liman ya Washe baki yace “Yo banda abinki Tabawa ai su kud’i ‘yan sirri ne..”
Tabawa tace “Haka ne..” Lokaci guda ta juya ta basu baya Liman sai nad’e carbi yake cikin hannunsa yana gyara rawani yana ‘yan lek’e lek’e irinta marassa gaskiya.
Tabawa ta k’irgo dubu biyar ta mik’awa Malam Liman.
Mu’azzam ya d’ago fuskarsa data rine zuwa ja sabida tsananin tashin hankali, lokaci guda ya shafi goshinsa da hannunsa guda kafin yace “Kai baka tunanin mutumin nan had’a baki sukai da mutanen da suka tassama sacesa.. Baka tunanin hakan na iya kasancewa cikin plan d’in Danger.. Danger is a very dangerous person Assad, he’s capable of everything.”
Assad ya jinjina kai yace “Na sani Danger is Dangerous, amma tambayar da zan maka a nan shine idan bakinsa d’aya da Danger Maiyasa zai sacesa.. Sannan idan bakinsa d’aya da Danger bazasu amshe kud’ad’en dake hannunsa ba..”
Mu’azzam ya zuba masa idanu kaman mai nazarin sai kuma ya murmusa yace “Kana magana as if you can’t read criminal minds and how smart they can act.. Yanzu dashi da Danger duk zasu iya shirya haka dan su karkatar da hankalin jami’an tsaro dan kawai abun yayi kaman Su d’in suna bibiyar Alhaji Isyaku ne sabida Auren Sadiya da yake yunk’urin yi.. I believe ka amince zasu aikata fiyeda haka.”
Assad ya nusa yace “Everything is possible in a situation like this saidai hanyar da ka d’auko zai iya sakamu cikin matsala gaba d’aya.. Maimakon muyi solving case d’in zamu iya b’ata komai da wannan hanyar daka biyo ba bisa k’a’ida ba..” Shiru Assad ya d’anyi yana mai tsaresa da idanu kafin yace “But wait, idan har kana tinanin Danger da mutumin nan bakinsu d’aya ne Maiyasa ka hana mutumin auren yarinyar..? Sannan Maiyasa kai ka aureta.. Kana tunanin zasu iya cutar da ita ne..?”
Shiru Mu’azzam bai basa amsa ba sai mugun kallon da yake aika masa. Lokaci guda Assad yaci gaba da jinjina kai yana fad’in “Now I get it.. Ka aureta ne to give her protection..!”
“O C’mon just shut up Assad..!”
Assad yaci gaba da fad’in “Yes gaskiya ne Mu’azzam dan ka bata kariya daga sharrin su Danger ka aureta.. Because she’s there target.. Ko baka fahimci hakan yanzu ba I’m positive gaba zaka fahimci haka.”
Da mugun mamaki Mu’azzam ke kallonsa yanaji yanda yake k’ok’arin k’irk’iro wani zance, kan mai zai bama wannan yarinyar protection Iyakacin abinda ya Sani shine he still needs her for his mission ne. Gajeren tsaki yai yana mai girgiza kai yake furta “You are not serious Assad. Bansan ya akai kake aiki k’ark’ashin NPF ba. You should be a clown and not a police officer..” Yana ida fad’in haka yasa kai ya koma cikin building d’in yanda Alhaji Isyaku ke zaune.
Assad ya take masa baya yana mai girgiza kai kad’an.
Suna k’arasowa Mu’azzam ya dubi Alhaji Isyaku yace “Alhaji zamu k’yaleka ka tafi.. Zamu maidaka Gida.. Motarka tana nan a waje wad’annan abokan aikin nawa sun taho maka da Ita nan.. Amma still idan kanaso zaka iya reporting ‘yanta’addan nan da suka tasamma saceka suka kuma sace maka kud’ad’enka.”
Alhaji Iskyaku Yai saurin girgiza kai yana mai zaro idanu yace “Ni wllhi bana fatan abinda zai had’ani da ‘‘yanta’addan nan, yo a k’asa irin wannan da aka maida satan mutum kaman an d’auke ‘ya’yan kaji ai abun na gode ma Allah ne da bai k’addari zan sha wahala hannun mutanen nan ba.. Kuma tinda na tsira Alhamdulillah.. Sannan wannan yarinya ko a k’afa aka d’aura mun ita zan kwance na gudu dan na kula tsautsayi da bala’i ke bibiyarsu.. Ban tab’a jin k’aran harbe harbe ba saida nace zan aureta.. Na gode maku matuk’a da ceton rayuwata da kukai..”
Assad ya mik’a masa hannu sukai musabaha kafin yace “Kar ka damu Alhaji, hakan aikinmu ne.. Kula da al’umman k’asa tsare masu rayuwarsu lafiyarsu harmada dukiyarsu.. Kuma kar ka damu da izinin Allah zamu gano mutanen da suka maka wannan aika aika and they will answer to the law. Ku daina karyar ma jami’an tsaron k’asar nan da fad’in cewa sun gaza Gwabnati ma sun gaza.. NPF tana iya k’ok’arinta a kullum domin taga Ta kawo k’arshen ta’addanci da rashin tsaron da ya addabi k’asar nan..A koda yaushe ku saka a ranku cewa mu ‘yansanda abokanku ne ba mak’iyanku ba.. Dukda cewa da yawa sun mana shaida cewa akasarin mu gurb’atattu ne ba haka abin yake ba domin kuwa akwai na k’warai a cikinmu.. Kaman dai ko wacce irin Sana’a akwai gurb’atattu akwai na K’warai..”
Alhaji Isyaku ya jinjina kai a hankali yana duban matashin D’ansandan. Lokaci guda ya kuma masu godiya kafin suka nufo waje gaba d’aya.
Suna fitowa waje Alhaji Isyaku ya kasa key ma Mota, jikinsa dik sai rawa yake.. Gani yake kaman ‘yantaddan zasu kuma dawowa.
Ya lek’o da kansa ta glass yana fad’in “Rankaidad’e ko zaku taimaka min dan Allah.. Wllhi ban iya tuk’a motar.”
Assad ya dubesa kafin ya dubi su Mu’azzam sai kuma yace da Alhaji Isyaku “I’ll drive you home Alhaji.”
Alhaji Isyaku cikeda jin dad’i yake godiya wa Assad “Na gode matuk’a yallab’ai, aikam bazan iya tuk’a mota ba dan har yanzu tsoro bai sakeni ba.. Gani nake kaman idan ina tafiya ‘Yantaddan nan zasu dawo.. Na gode na gode k’warai.”
Assad ya dubi Mu’azzam yai masa alama da hannu kan cewa zai kai Alhaji Isyaku gida. Jinjina masa kai kurum Mu’azzam yai kafin suka soma fitowa tareda su Yusuf suka nufi motocinsu suna basa update abinda ke faruwa a CID.
Shiru Mu’azzam yai yana nazarin abducting Alhaji Isyaku da aka tasamma Yi wanda baida haufi idan har Alhaji Isyaku baida wani connection da Danger Toh ko shakka babu masu bibiyan yarinyar ne suka kuskuresa. A fili ya furta “Danger..! Zan kamaka dik yanda ka shiga ka fita.. Da k’udurar Ubangiji.!”
K’aran shigowar sak’o cikin wayarsa da yaji ne ya sanyasa ciro wayar aljihu yana dubawa. Lamba ce Babu suna, sannan abinda kawai aka rubuta jikin sak’on shine _BAD_
Ya nanata alphabets d’in a hankali “BAD” sai kuma ya fad’a in word “Bad..!” Ya nanata yafi sau UKU. Lokaci guda ya yanke shawarin kiran lambar.. Kafin yakai ga kiran lambar wani sak’on ya sake shigo masa. Wannan karon ga abinda aka rubuta.
_BAD is your enemy_
A hankali ya kuma furtawa “Bad is your enemy”. Yai shiru yana kuma duba. What does this mean.?
Saurin sake danna kira yai amma wayar bata shiga, a kashe take.
Take wata sak’on Ta kuma shigo masa da wata lamba ta daban
_BAD is ruining your home._
Dafe kansa yai kad’an yana duban lambobin da aka turo masa wad’annan sak’on dasu wanda ko shakka babu wasa da hankalinsa mai turo sak’on yake shiyasa yake turo masa da lambobi barkatai dan kar yayi tunanin tracing lambobin.
Bai ida tinanin ba wani sak’on ya kuma shigowa da wani lamba daban duk dai akan BAD.
_BAD is very BAD_
A hankali ya fuzar da fuci yana duban lambobin kusan guda uku.
Cikin natsuwa ya nufi motarsa lokacin ana kiraye kirayen sallar magrib. Tinanin Bad bai daina Yawo a kwanyarsa ba. Yana driving yana nanata kalmar Bad.
Wata sak’on ta sake shigo masa da wata lamba daban duk dai akan bad
_You need to find BAD_
A fili Mu’azzam ya furta “Who are you BAD..?!”
**
A gidansu Sadiya kaw tana k’udundune a d’aki cikin bargo sai rawa jikinta yake alamun zazzab’i ya kuma rufeta, ko kukan ma ta kasa yi yanzu kam. Tabbas da ace zatai kukan da taji sa’ida cikin zuciyarta. Tana nan kwance tana kar karkarwa tana iya sauraro muryoyinsu daga tsakar gidan yanda yanda Malam Liman da Ummanta da shaidu guda uku suka had’u suna warware bashin da Tabawa ke binsu Wanda Wai mutumin da ya aureta ya biya masu.. Kuma Wai ba kowa bane wannan mutumin face d’asandan nan da Ta tabbata da zai iya samun daman harbeta da zai aikata hakan.. Ta yaya za’ace wannan mutumin shine mijinta.. Ta yaya za’ace an mata aure haka bagatatan saikace wata ‘yar tsana.. Shin talauci hauka ne kokuwa dai rashin mahaifinta ne yasa akai mata haka.. Allah sarki yau Ta kuma yarda cewa mahaifi Katanga ne mai k’arfi kan iyalansa duk talaucinsa da babunsa kuwa.. Ta tabbata da ace Abba yana nan sam bazai zuba idanu ai mata irin wannan auren ba.. Tabbas maraici akwai ciwo cikinsa.. Tabbas wanda bai d’and’ani d’acin maraici ba baisan rashi a rayuwa ba.. Yau taga ranan mahaifinta sannan taji ciwon rashin sa a gareta.. Gashi nan a aurar da ita saikace wata taguwar da aka ciwo a yak’i wacce batada wani daraja.. Wasu hawaye masu tsananin zafi suka zubo mata. Tana jin sanda Tabawa ke gud’a tana fad’in ta yarda k’wallan mangoro ta huta da k’uda.
Saida su Malam Liman da shaidu suka fara ficewa kafin Tabawa ta mak’ale kud’ad’enta ta fice.
A zauren gidan Tabawa Malam Liman da D’an Rakiyarsa Munkaila kuka tsaya suna jiran Tabawar.
Tabawa tana shigowa tai wani birki tana bada balance dan bataga alamun mutane ba da shike dare ne.
Rawanin Malam Liman ta hango ta gane sune.
“Ahh Haba Malam yo ai sai ka razanen.!”
Malam Liman ya Washe baki yace “Yo banda abinki Tabawa ai su kud’i ‘yan sirri ne..”
Tabawa tace “Haka ne..” Lokaci guda ta juya ta basu baya Liman sai nad’e carbi yake cikin hannunsa yana gyara rawani yana ‘yan lek’e lek’e irinta marassa gaskiya.
Tabawa ta k’irgo dubu biyar ta mik’awa Malam Liman.