Sashe 119
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya furzar da huci kad’an yana shafe fuskarsa kafin ya duk’a nan gabanta suna fuskantar juna. Cikin yanayin kwantar da murya yake fad’in “Feenah ki nastu ki daina wann obsession d’in.. Ki tuna you are carrying a child in your womb now.. Abinda kikeyi can affect the child.. Look if you need a therapist zan nemo miki..”
Katsesa tai da fad’in “Aw bayan obsession da kake fad’i yanzu kuma mahaukaciya ka d’aukeni.. Well idan akan soyayyarka ne kana iya kirana komai.. Har abinda yafi mahaukaciya.”
Ya kuma furzar da huci kad’an yana mai duban wani b’angaren dan yanzu abin Safeenah ya daina basa mamaki, yafi danganta abin da rashin lafiya.. Idan bai bita a hankali ba za’a iya rasa abinda ke cikinta.
“Ba mahaukaciya na d’aukeki ba.. Ki kwantar da hankalinki kinji.. Idan na dawo zamuyi magana a natse. Kinga Dr yace high risk pregnancy kike d’auke dashi.. And shiga damuwa ko tashin hankali won’t do any good for the Baby.. Kuma kema Nasan baki son abinda zai samu Babyn right.?” Yanda yake maganar tamkar mai lallashin k’aramin yaro maras cikakken hankali haka yake mata.
Ta saki murmushi a hankali tana jinjina masa kai hannunta guda dafe da cikin nata.
Murmushi ya sakar mata shima kafin yace “Good.. Yanzu ki kwanta ki huta.. And idan kina son wani just tell me right away kinji koh..”
Ta jinjina masa kai a hankali kafin tace “Idan ka tafi zaka dawo ka dubamu..?I mean nida Babynmu..” Tana maganar tana shafa cikinta murmushi gauraye da hawaye saman fuskarta.
Jinjina mata kai yai yace “Of course zan dawo.. Just get some rest now kinji koh..” Ya k’arashe yana mai mik’ewa tsaye ya isa ya gyara mata pillow da tai matashi dashi yace “Zo ki kwanta ki huta..”
Ta mike tana murmushi ta iso ta zauna a kujeran. Ya sakar mata murmushi kad’an kafin yace “I’ll be goin now..”
Ta sakar masa murmushi tace “Ka sayo min roasted corn.”
Ya jinjina kai yace “Akwai wani abinda kike so kuma.?”
Ta girgiza kai kad’an “No gasashiyar masarar yayi.”
Ya jinjina kai kafin ya sakar mata murmushi kad’an ya fice zuciyarsa fal tausayinta.
Safeenah tabi bayansa da kallo tana murmushi “Sannu a hankali Mu’azzam.. Zaka mai dani gidana kafin na haife abinda ke cikina..” Ta k’arashe zancen zucin nata tana mai gyara kwanciyar ta.
Mommy dake lab’e taji dik yanda sukai. Murmushi ta saki kafin ta furta a fili “Greatest weakness d’inka shine wann cikin Mu’azzam.. Na maka alk’awari ni kuma sai nayi amfani da wann cikin na tarwatsa ka.. Ba’a cin bashi na a wanye lafiya ni Hajara.!” Tana ida fad’in haka ta juya ta bar wajen.
Tana shiga d’aki ta tadda wayarta na ruri. Lamba ce Babu suna.. Ta yatsina fuska kafin ta d’aga kiran tana fad’in “Hello hello wake magana.. Hello ba service.. Wrong number... Shuuuuuu..!” Mommy tace tana Yawo da wayar a iska.
Muryar Shemau ta sinkayo daga d’aya b’angaren tana fad’in “Kar ki kuskura Hajara..!”
Mommy tai tsaye tana sauraronta yayinda Shemau taci gaba da fad’in “Wllhi idan kika kashe mun waya yau kam sai na tona miki asiri. Na Sani sarai mijinki na nan Fufore yazo duba matarsa.. Yau kusan sati kenan Ina kiranki da different lines kina raina mun hankali, da kin d’aga ki wani fara hello hello ba network.. Toh ko uban Network ne Babu yau kam kika katse mun waya wllhi sai na kwance miki zani a kasuwa. Naji labarin Alhaji Marwan Gamji na gari tin shekaran jiya.. I can go straight to him na sanar dashi komai duk abinda kika aikata wa matarsa.”
Mommy tai ‘yar bazawarar dariya kafin tace “Shemau kenan.. Yo ce maki akai barazanarki zai bani tsoro.. Ince atata kice mun had’a baki nida ke mun d’auko wa Nuratu mai gani na bogi..” Ta mik’e tsaye tana zagaye d’akin, still waya manne kunnenta. Muguwar murmushi saman fuskarta take fad’in “Barin tambayeki Shemau, tsakanin ni da ke wacece Kyallu ta sani..?”
Shemau tai shiru batace komai ba jin Mommy zata juya teburin zuwa kanta.
Mommy tai murmushin cin nasara kafin taci gaba da fad’in “Ko nuna ni akaima Kyallu nayi imani bata sanni ba, bata tab’a gani na ba.. Wa ta sani..? Wacece Ta d’auko ta matsayin mai magani..? Kece Shemau.. Ke kikai kid’anki kuma kikai rawarki.. Ke da kanki zaki kama kanki.. Kuma na miki imani da Allah yanda yanzu baki tareda Salman Gamji tsaf Mu’azzam zai turaku kurkuku ne keda Kyallu..” Ta murmusa kad’an kafin tace “Kin zata bani da hankali ne..? Kin zata ni shahshasha ce.. Shemau nasan yanda nake buga wasanni na.. Ce miki akai bansan amfani kike so kiyi dani ba.? Nasan dole Kema akwai abinda kike nema wajena Watak’ila nan gaba kad’an ki bijiro min da abinda kike nema shisa kike taimakona.. Toh ni ba mahaukaciya bace Shemau.. Nasan sarai mai nakeyi.. Bakida wata dalili ko hujja akaina.. Idan kuwa kikai gangancin sanar da Marwan Gamji kin d’auko wa matarsa ‘Yar damfara matsayin mai magani ba ke kad’ai ba harta mijinki sai Mu’azzam ya bincika.. Kinga kuwa a banza Salman zai kuma tsananki..”
Shemau ta saki baki da hanci tana jin tuggun da Mommy ke fad’i, Wato ashe itace babban Shashahsha da tai komai ita kad’ai ba tareda tayi involving Mommy ba tinda Mommy tana Abuja ne.. Ita dai Shemaun ita ake aike.
Cikin tsananin k’unan rai Shemau ke fad’in “Amma Hajara Bakida kirki.. Bakida imani.. Juya min baya zakiyi..?”
Mommy ta dara tace “Iya ruwa ke fidda kai.. Kowa ya biya allonsa sai ya wanke.”
“Ban gama dake ba Hajara. Akwai last card d’ina da zanyi amfani dashi akanki.. ‘Yarki Safeenah..!”
Mommy ta tsaya Cak tana sauraron Shemau. Yayinda Shemaun taci gaba da fad’in “Zan tona mata asiri wajen Mu’azzam cewa itace Ta bani umarni na kawo wa matarsa Sadiya kwarto.”
Katseta Mommy tai cikin k’yalk’yalewa da dariya “Amma kin tabbata shashasha Shemau. Yo a d’akin waye aka kama Kwarto. D’akin Mijinki ne ko kuwa D’akin matar Mu’azzam.?”
Shiru Shemau bata bata amsa ba sai hawaye dake k’ok’arin ciko idanunta.
Mommy ta kuma murmusawa kafin tace “Bakida wata hujja akanmu daga ni har ‘yata.. Babu wanda zai yarda dake Shemau b’ata ma kanki lokaci kawai kike..” Ta kuma murmusawa kafin tace “Sai ki tattari k’wararen da aka kawoki dasu maza a koma ruga.. Dan idan ban mance ba da k’waraye uku kawai aka kawoki, na wayar dake na gogar dake na nuna miki duniya shine bari ki min tijara har ni kike ma barazana.. Go ahead Shemau.. Kije ki fad’a ma duk wanda zaki fad’i kiga ko akwai mai yarda dake..” Daga haka D’if Mommy ta kashe wayar.
Aka bar Shemau rik’e da waya tana jinjina lamarin duniya. Wato duk tarayyar da ba’a ginata dan Allah ba da tsiya take watsewa.. Wasu irin k’walla ne na nadama Shemau taji suna ciko idanunta.. Shin dama ita rayuwar duniya haka take..? Shin dama da gaske ne hausar nan da ake cewa idan ka so wa mutane alkhairi kaima ka tsammaci alkhairi a matsayin tukwicin duniya.. Haka idan Kaso wa mutane sharri kaima sai ka tsammaci sharri a matsayin tukwicin duniya.. Bata ida tunanin nata na ta sinkayo muryar mijin Boddo daga parlor yana ci gaba da sababi “Ni gaskiya ta fice ta bar mun gida.. Ba yanda za’a yi matar nan ta k’ara kwana a gidan nan.. Wllhi kinji na rantse miki idan baki sallami bak’uwarki a gidan nan ba zan had’a harda ke na sallameku dan ni babu masauk’inta a gidana.. Matar da labari ya gama karad’e gari cewa maza take kaiwa cikin gidan mijinta.. Ke barin fad’a miki.. Daga yau.. Daga rana mai kamar ta yau na yanke alak’arki da ita.. Babu ita Babu ke kinji na fad’a miki.”
Boddo ta marairaice fuska tace “Haba Abban Huzaifa Shemau batada majingini ne dan Allah ka tausaya mata.. Wllhi akasi aka samu amma ba halinta bane biye biyen maza.. Ni zanyi wann shaidar.”
Banda uwar harara baya aikata mata komai “Wann kuma matsalarku ce can abinda naji a gari dashi zanyi amfani. Ko mutuwa kai shaidar da aka maka shi zai bika dan haka wann watsattsiyar batada masauk’i gidana.. Toh ma Wai batada iyaye ne.. Ubanta ne ni da za’a koreta Ta kwaso k’afa tazo mun gida.. Ki fice a idanuna fah Boddo..” Ya k’arashe yana nunata da yatsa.
Boddo ya sauk’e ajiyan zuciya Ta mik’e Jiki babu k’wari.
Shemau dake rakub’e d’aki tana sauraron tattaunawar mijin Boddo da Boddon sai taji wasu k’wallan na kuma ciko idanunta “Na shiga uku ni Shemau Ina zan saka kaina..!” Ta k’arashe tana d’aura hannayenta biyu aka.
A haka Boddo ta shigo ta taddata.
Shemau na hawaye take fad’in “Baddo naji komai. Kuma wllhi nasan Kinyi iya k’ok’arinki.. Na gode matuk’a K’awata... Zan tafi dan bazanso Kema na lalata miki naki auren ba.. Kaman yanda na lalata nawa..”
Boddo ta k’araso ta dafa Shemau tace “Kiyi hak’uri Shemau wllhi babu yanda na iya ne.. Tinda Abban Huzaifa yace haka nasan bazai kuma sauk’owa ba.. Amma da ace zaiyi hak’uri ya barki ki zauna a nan wllhi da bazan bari ki tafi ba.. Kiyi hak’uri k’awata.”
Rungumeta Shemau tai tana kuka tana girgiza kai “Dole na tafi Boddo dan kar Kema na jaza miki.. Abinda na shuka ne Tabbas nake girba.. Duniya makaranta ce dama.. Yau ta kuma biya mun wani karatu.. Mutanen da nayi tarayya dasu wajen aikata muggan laifuka duk sun juya mun baya.. Sun barni a rana tsaka babu rumfa babu majingini.. Ga Salman har umarni yai ma securities na Companyn su cewa ko mai kamannina suka sake gani k’ofar wajen Su koreta..” Ta saka bayan hannunta tana goge hawayenta kafin taci gaba da jinjina kai tana fad’in “Banida zab’i da ya wuce na koma ruga can wajen su Inna Fini da Baffah.. Boddo zan koma rayuwar da na baro a baya.. Rayuwar da Allah ya cireni a ciki ni kuma nayi butulci... Na butulce wa Rahamar Ubangijina... Bani da zab’i da ya wuce na fuskanci wann rayuwar a halin yanzu..” Ta k’arashe tana mai kuma fashewa da kuka.
Katsesa tai da fad’in “Aw bayan obsession da kake fad’i yanzu kuma mahaukaciya ka d’aukeni.. Well idan akan soyayyarka ne kana iya kirana komai.. Har abinda yafi mahaukaciya.”
Ya kuma furzar da huci kad’an yana mai duban wani b’angaren dan yanzu abin Safeenah ya daina basa mamaki, yafi danganta abin da rashin lafiya.. Idan bai bita a hankali ba za’a iya rasa abinda ke cikinta.
“Ba mahaukaciya na d’aukeki ba.. Ki kwantar da hankalinki kinji.. Idan na dawo zamuyi magana a natse. Kinga Dr yace high risk pregnancy kike d’auke dashi.. And shiga damuwa ko tashin hankali won’t do any good for the Baby.. Kuma kema Nasan baki son abinda zai samu Babyn right.?” Yanda yake maganar tamkar mai lallashin k’aramin yaro maras cikakken hankali haka yake mata.
Ta saki murmushi a hankali tana jinjina masa kai hannunta guda dafe da cikin nata.
Murmushi ya sakar mata shima kafin yace “Good.. Yanzu ki kwanta ki huta.. And idan kina son wani just tell me right away kinji koh..”
Ta jinjina masa kai a hankali kafin tace “Idan ka tafi zaka dawo ka dubamu..?I mean nida Babynmu..” Tana maganar tana shafa cikinta murmushi gauraye da hawaye saman fuskarta.
Jinjina mata kai yai yace “Of course zan dawo.. Just get some rest now kinji koh..” Ya k’arashe yana mai mik’ewa tsaye ya isa ya gyara mata pillow da tai matashi dashi yace “Zo ki kwanta ki huta..”
Ta mike tana murmushi ta iso ta zauna a kujeran. Ya sakar mata murmushi kad’an kafin yace “I’ll be goin now..”
Ta sakar masa murmushi tace “Ka sayo min roasted corn.”
Ya jinjina kai yace “Akwai wani abinda kike so kuma.?”
Ta girgiza kai kad’an “No gasashiyar masarar yayi.”
Ya jinjina kai kafin ya sakar mata murmushi kad’an ya fice zuciyarsa fal tausayinta.
Safeenah tabi bayansa da kallo tana murmushi “Sannu a hankali Mu’azzam.. Zaka mai dani gidana kafin na haife abinda ke cikina..” Ta k’arashe zancen zucin nata tana mai gyara kwanciyar ta.
Mommy dake lab’e taji dik yanda sukai. Murmushi ta saki kafin ta furta a fili “Greatest weakness d’inka shine wann cikin Mu’azzam.. Na maka alk’awari ni kuma sai nayi amfani da wann cikin na tarwatsa ka.. Ba’a cin bashi na a wanye lafiya ni Hajara.!” Tana ida fad’in haka ta juya ta bar wajen.
Tana shiga d’aki ta tadda wayarta na ruri. Lamba ce Babu suna.. Ta yatsina fuska kafin ta d’aga kiran tana fad’in “Hello hello wake magana.. Hello ba service.. Wrong number... Shuuuuuu..!” Mommy tace tana Yawo da wayar a iska.
Muryar Shemau ta sinkayo daga d’aya b’angaren tana fad’in “Kar ki kuskura Hajara..!”
Mommy tai tsaye tana sauraronta yayinda Shemau taci gaba da fad’in “Wllhi idan kika kashe mun waya yau kam sai na tona miki asiri. Na Sani sarai mijinki na nan Fufore yazo duba matarsa.. Yau kusan sati kenan Ina kiranki da different lines kina raina mun hankali, da kin d’aga ki wani fara hello hello ba network.. Toh ko uban Network ne Babu yau kam kika katse mun waya wllhi sai na kwance miki zani a kasuwa. Naji labarin Alhaji Marwan Gamji na gari tin shekaran jiya.. I can go straight to him na sanar dashi komai duk abinda kika aikata wa matarsa.”
Mommy tai ‘yar bazawarar dariya kafin tace “Shemau kenan.. Yo ce maki akai barazanarki zai bani tsoro.. Ince atata kice mun had’a baki nida ke mun d’auko wa Nuratu mai gani na bogi..” Ta mik’e tsaye tana zagaye d’akin, still waya manne kunnenta. Muguwar murmushi saman fuskarta take fad’in “Barin tambayeki Shemau, tsakanin ni da ke wacece Kyallu ta sani..?”
Shemau tai shiru batace komai ba jin Mommy zata juya teburin zuwa kanta.
Mommy tai murmushin cin nasara kafin taci gaba da fad’in “Ko nuna ni akaima Kyallu nayi imani bata sanni ba, bata tab’a gani na ba.. Wa ta sani..? Wacece Ta d’auko ta matsayin mai magani..? Kece Shemau.. Ke kikai kid’anki kuma kikai rawarki.. Ke da kanki zaki kama kanki.. Kuma na miki imani da Allah yanda yanzu baki tareda Salman Gamji tsaf Mu’azzam zai turaku kurkuku ne keda Kyallu..” Ta murmusa kad’an kafin tace “Kin zata bani da hankali ne..? Kin zata ni shahshasha ce.. Shemau nasan yanda nake buga wasanni na.. Ce miki akai bansan amfani kike so kiyi dani ba.? Nasan dole Kema akwai abinda kike nema wajena Watak’ila nan gaba kad’an ki bijiro min da abinda kike nema shisa kike taimakona.. Toh ni ba mahaukaciya bace Shemau.. Nasan sarai mai nakeyi.. Bakida wata dalili ko hujja akaina.. Idan kuwa kikai gangancin sanar da Marwan Gamji kin d’auko wa matarsa ‘Yar damfara matsayin mai magani ba ke kad’ai ba harta mijinki sai Mu’azzam ya bincika.. Kinga kuwa a banza Salman zai kuma tsananki..”
Shemau ta saki baki da hanci tana jin tuggun da Mommy ke fad’i, Wato ashe itace babban Shashahsha da tai komai ita kad’ai ba tareda tayi involving Mommy ba tinda Mommy tana Abuja ne.. Ita dai Shemaun ita ake aike.
Cikin tsananin k’unan rai Shemau ke fad’in “Amma Hajara Bakida kirki.. Bakida imani.. Juya min baya zakiyi..?”
Mommy ta dara tace “Iya ruwa ke fidda kai.. Kowa ya biya allonsa sai ya wanke.”
“Ban gama dake ba Hajara. Akwai last card d’ina da zanyi amfani dashi akanki.. ‘Yarki Safeenah..!”
Mommy ta tsaya Cak tana sauraron Shemau. Yayinda Shemaun taci gaba da fad’in “Zan tona mata asiri wajen Mu’azzam cewa itace Ta bani umarni na kawo wa matarsa Sadiya kwarto.”
Katseta Mommy tai cikin k’yalk’yalewa da dariya “Amma kin tabbata shashasha Shemau. Yo a d’akin waye aka kama Kwarto. D’akin Mijinki ne ko kuwa D’akin matar Mu’azzam.?”
Shiru Shemau bata bata amsa ba sai hawaye dake k’ok’arin ciko idanunta.
Mommy ta kuma murmusawa kafin tace “Bakida wata hujja akanmu daga ni har ‘yata.. Babu wanda zai yarda dake Shemau b’ata ma kanki lokaci kawai kike..” Ta kuma murmusawa kafin tace “Sai ki tattari k’wararen da aka kawoki dasu maza a koma ruga.. Dan idan ban mance ba da k’waraye uku kawai aka kawoki, na wayar dake na gogar dake na nuna miki duniya shine bari ki min tijara har ni kike ma barazana.. Go ahead Shemau.. Kije ki fad’a ma duk wanda zaki fad’i kiga ko akwai mai yarda dake..” Daga haka D’if Mommy ta kashe wayar.
Aka bar Shemau rik’e da waya tana jinjina lamarin duniya. Wato duk tarayyar da ba’a ginata dan Allah ba da tsiya take watsewa.. Wasu irin k’walla ne na nadama Shemau taji suna ciko idanunta.. Shin dama ita rayuwar duniya haka take..? Shin dama da gaske ne hausar nan da ake cewa idan ka so wa mutane alkhairi kaima ka tsammaci alkhairi a matsayin tukwicin duniya.. Haka idan Kaso wa mutane sharri kaima sai ka tsammaci sharri a matsayin tukwicin duniya.. Bata ida tunanin nata na ta sinkayo muryar mijin Boddo daga parlor yana ci gaba da sababi “Ni gaskiya ta fice ta bar mun gida.. Ba yanda za’a yi matar nan ta k’ara kwana a gidan nan.. Wllhi kinji na rantse miki idan baki sallami bak’uwarki a gidan nan ba zan had’a harda ke na sallameku dan ni babu masauk’inta a gidana.. Matar da labari ya gama karad’e gari cewa maza take kaiwa cikin gidan mijinta.. Ke barin fad’a miki.. Daga yau.. Daga rana mai kamar ta yau na yanke alak’arki da ita.. Babu ita Babu ke kinji na fad’a miki.”
Boddo ta marairaice fuska tace “Haba Abban Huzaifa Shemau batada majingini ne dan Allah ka tausaya mata.. Wllhi akasi aka samu amma ba halinta bane biye biyen maza.. Ni zanyi wann shaidar.”
Banda uwar harara baya aikata mata komai “Wann kuma matsalarku ce can abinda naji a gari dashi zanyi amfani. Ko mutuwa kai shaidar da aka maka shi zai bika dan haka wann watsattsiyar batada masauk’i gidana.. Toh ma Wai batada iyaye ne.. Ubanta ne ni da za’a koreta Ta kwaso k’afa tazo mun gida.. Ki fice a idanuna fah Boddo..” Ya k’arashe yana nunata da yatsa.
Boddo ya sauk’e ajiyan zuciya Ta mik’e Jiki babu k’wari.
Shemau dake rakub’e d’aki tana sauraron tattaunawar mijin Boddo da Boddon sai taji wasu k’wallan na kuma ciko idanunta “Na shiga uku ni Shemau Ina zan saka kaina..!” Ta k’arashe tana d’aura hannayenta biyu aka.
A haka Boddo ta shigo ta taddata.
Shemau na hawaye take fad’in “Baddo naji komai. Kuma wllhi nasan Kinyi iya k’ok’arinki.. Na gode matuk’a K’awata... Zan tafi dan bazanso Kema na lalata miki naki auren ba.. Kaman yanda na lalata nawa..”
Boddo ta k’araso ta dafa Shemau tace “Kiyi hak’uri Shemau wllhi babu yanda na iya ne.. Tinda Abban Huzaifa yace haka nasan bazai kuma sauk’owa ba.. Amma da ace zaiyi hak’uri ya barki ki zauna a nan wllhi da bazan bari ki tafi ba.. Kiyi hak’uri k’awata.”
Rungumeta Shemau tai tana kuka tana girgiza kai “Dole na tafi Boddo dan kar Kema na jaza miki.. Abinda na shuka ne Tabbas nake girba.. Duniya makaranta ce dama.. Yau ta kuma biya mun wani karatu.. Mutanen da nayi tarayya dasu wajen aikata muggan laifuka duk sun juya mun baya.. Sun barni a rana tsaka babu rumfa babu majingini.. Ga Salman har umarni yai ma securities na Companyn su cewa ko mai kamannina suka sake gani k’ofar wajen Su koreta..” Ta saka bayan hannunta tana goge hawayenta kafin taci gaba da jinjina kai tana fad’in “Banida zab’i da ya wuce na koma ruga can wajen su Inna Fini da Baffah.. Boddo zan koma rayuwar da na baro a baya.. Rayuwar da Allah ya cireni a ciki ni kuma nayi butulci... Na butulce wa Rahamar Ubangijina... Bani da zab’i da ya wuce na fuskanci wann rayuwar a halin yanzu..” Ta k’arashe tana mai kuma fashewa da kuka.