Sashe 73
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daidai lokacin Chief ya shigo sanda suketa shiri cikin sauri babu kaman Mu’azzam wanda gani yake kaman bazai isa wajen ba, alla alla kawai yake ya ceceta ya kuma damk’o Danger da hannayensa.
Chief yai tsaye yana dubansu yanda kowa ke sauri cikinsu sai shirya alburusai suke cikin bindigoginsu. Yusuf na sanar dasu wani tsohon building ne Danger yake can wajen gari.
Assad ya sarawa Chief yana fad’in “We were able to trace Danger’s location, Sir.”
Dikda Zuciyar Chief Ta yanke hakan bai hanasa nuna Farin cikinsa a fili ba.. Yana tafe hannayensa yake fad’in “Then what are we waiting for Detectives.. Move it, faster.. Let’s catch Danger.!” Ya fad’i yana tafe hannayensa alamun Su k’ara sauri.
A haka suka dinga ficewa har dai Mu’azzam yazo ficewa, suka tsaya suna duban juna shida Chief.
Murmushi Chief ya sakar masa kafin yace “Well done Inspector Gamji.. I must congratulate you and your team..”
Murmushi da gefen bakin Mu’azzam ya sakar masa yana Soka bindigarsa jikin belt d’insa kafin yace “Tukunna ma Sir.. Sai kaga Danger da accomplices d’insa behind bars.” Yana ida fad’in haka ya sarawa Chief kafin yasa kai ya shige.
Chief yabi bayansa da mugun kallo yana huci, lokaci guda yake duban allon binciken nasu nan yaga an zana circle an rubuta B.A.T a sama ga kuma question mark cikin circle d’in.. Anyi linking circle d’in da hoton Danger. Zuciyr Chief yai wani irin bugawa.. Gumi ya shiga ketowa Chief tako Ta ina.. Kar dai Maleeka ta sanar da Mu’azzam wani abu akan BAT.. Lallai Maleeka tana wasa da rayuwarta. Ya lura komai zatayi akan Mu’azzam.
Cikin tsananin fushi mai gauraye da tashin hankali Chief ya daki garu kafin yasa kai ya fice daga ofishin.
Kallon da Chief yaiwa Maleeka tasan cewa akwai matsala, tasa kai Ta shige cikin sauri zuciyarta na yankewa.
Mu’azzam ne ya rarraba masu bulletproof vests ko wannensu ya aza saman rigarsa, gaba d’ayansu motar Office suka shiga. Assad ke driving Mu’azzam na gefensa Yusuf da Maleeka suna mazaunin baya.
Saidai suna isa sukaji an soma kaima motarsu attack da harbi alamun su Danger Sun riga sun San da zuwansu an sanar dasu. Take sukai holding positions d’insu Mu’azzam na fad’in”No one shoot.. My wife is in there..”
Suka jinjina kai suna fad’in copy. Su Danger suka ci gaba da harbi kafin daga bisani wutan ya tsagaita.
Mu’azzam ne yai masu alama da hannu da ido kan su soma matsowa kusa suna nufan ginin cikin kwanton b’auna. Haka kuwa akai a hankali suka dinga matsawa kusa cikin bin umarnin Mu’azzam har suka isa ginin..
Wani mutumi sanye da bak’ak’en tufafi fuskarsa rufe da bak’in mask shine yai saitin Mu’azzam zai harbesa ba tareda Mu’azzam d’in ya gansa ba Maleeka ta k’arasa da sauri ta tare wa Mu’azzam harsashin tana kiran sunansa dan ita taga mutumin.. Take harsashin ya sameta a hannunta.. Gaba d’aya suka juyo suna duban Maleeka da ta karb’ewa Mu’azzam harsashi ta duk’a wajen tana cije lab’e rik’e da hannuta yanda harsashi ya huda jini na zuba.. Yusuf da Assad suka k’araso a guje suna ambato sunan Maleeka yayinda Mu’azzam yai Chasing mutumin a guje.. Gini ne upstairs mai tsawo irin abandon gini d’in nan wanda zallan Kango ne.. Haka mutumin ya dinga haurawa sama a guje yana sakowa Mu’azzam harsashai Mu’azzam na kaucewa yana kuma chasing d’insa dan a raye yake son capke Sa. Saida ya bari Mu’azzam ya isa sama saura kad’an ya kamasa kafin ya dirk’o yana kuma kai masa harbi.. Mu’azzam ya kama jikin bargwajajjen staircase din kenan zai dirk’o yabi bayansa yaji kaman kukan mutum cikin wani d’aki dake rufe .. Cikin sauri ya juyo yana duban d’akin ya daina chasing mutumin..
A hankali ya furta “Sadee.!”
Da k’afarsa ya daki k’ofar saida ya b’allata.. Can ya hangota d’aure saman kujera idanunta a rufe haka ma bakinta.. Jikinsa har rawa yake ya isa a guje ya cire blindfold d’in da aka rufe mata ido dashi..
Suna had’a ido taji wani irin kuka yazo mata.. Lokaci guda yaci gaba da kwanceta yana fad’in “It’s okay.. You’re safe now..!” Ya k’arashe yana mai rungumarta cikin jikinsa.
Wani kukan Ta kuma fashewa dashi jikinta sai rawa yake alamun bak’ar azaba yunwa da galabaita had’ida tsananin tsoro da tashin hankalin da Ta tsinci kanta ciki.
Kaman wacce ta tuna wani abu tai k’ok’arin cire jikinta daga nasa ta shiga girgiza kai tana k’ok’arin matsawa da baya take fad’in “No no no.. Don’t touch me.. Kar ka tab’a ni kar kazo kusana..”
“How do I save you idan ban tab’a ki ba.!” Yai maganar cikin daka tsawa..
Juyawan da zai yaji kaman abu na reading ashe bomb ne a gefe Danger ya aje ma Sadiya da niyyan k’onata.
Mu’azzam bai kuma sauraronta ba ya shiga girgiza kai yana furta “Oh shit..! Come here now..” Ya sunkuceta tamkar Baby ya soma gudu da ita tana cikin hannunsa sai had’e stirs yake yana tsallakewa gudun kar bomb d’in Ta tashi dasu suna cikin ginin.
A can waje kuwa Maleeka dai tana fama da hannunta da aka harba Assad da Yusuf ne sukai chasing mutumi mai bak’in kayan bayan ya samu fitowa daga building d’in.. Suna guje suna bata kashi tsakaninsu.. Nan harsashi ya samu Assad gefen wuyarsa kusan kafad’arsa yanda Bulletproof vest d’in bai rufe ba.. Ya duk’a a wajen yana kame wuyarsa da tuni jini ya soma kwarara..
Yusuf ya dakata da chasing mai bak’in kaya ya duk’a yana duba Assad dake cikin pain yana k’ok’arin taimakawa d’anuwansa.
A can building d’in kaw wata jahilar tsalle Mu’azzam yai still tana rik’e cikin hannunsa daidai sanda Bomb d’in tai exploding..
Haka ya kwanta kan Sadiya ya rufeta ruf sand bomb d’in ta tashi dan ma kar wani abu ya sameta.
Maleeka ma ta juyar da fuskarta tana mai kwanciya flat a k’asa sanda bomb d’in tai exploding.
A hankali komai ke lafawa. Mu’azzam ya mik’e da k’yar yana jijjiga Sadiya dake kwance k’asar sa wacce ta koma tamkar bata numfashi.
Maleeka ta bud’e idanunta da k’yar tana duban Mu’azzam dake ci gaba da jijjiga Sadiya yana fad’in Ta bud’e idanunta.
Lokaci guda yaci gaba da jijjigata yana fad’in “No.. No.. Stubborn head.. Not now.. Please wake up.. Wake up.. wake up now..!” Yana maganar yana jijjigata.
Dukda rad’ad’in ciwon dake jikin Maleeka bai hanata zuba idanu tana dubansu kaman Ta samu TV.. Tinda take bata tab’a ganin Mu’azzam ya birkice kan wata mace ba sai wannan yarinyar.. For the first time da zata iya cewa taga Mu’azzam Gamji dumu dumu cikin kogin soyayya..
Haka ya dinga jijjiga Sadiya yana fad’in Ta tashi.. K’arshe bakinsa ya d’aura saman nata yana hura mata iska..
Maleeka kaw ji tai wani abu ya tokare mata mak’oshi sanda tanga Mu’azzam ya saka bakinsa saman na Sadiya. Tai saurin rintse idanunta had’ida ciza labb’anta.. Shekara da shekaru tana kwad’ayin irin haka ya kasance tsakaninsu sai gashi yau d’in tanaji tana gani a gabanta yake saka bakinsa cikin na wata.. Ji tai zafin ciwon da taji dominsa na k’aruwa.. Ta kuma rintse idanunta da k’arfin gaske hawaye mai zafi na gangaro mata.
Wani dogon numfashi Sadiya taja had’ida bud’e idanunta. Bai wata wata ba ya mak’aleta tsam cikin jikinsa kaman mai tsoron kar wani abu ya kuma raba tsakaninsu.
Daidai lokacin Su Assad da Yusuf suka k’araso. Yusuf na tallafe da Assad wanda jini ke zuba sosai daga jikinsa. Cikin sauri Mu’azzam ya bud’e mota ya zaunar da Sadiya ciki kafin ya k’araso wajen abokansa. Assad ko iya bud’e idanunsa bayayi dan sosai harsashin ta shigesa gashi a waje mai had’ari harsashin ya samesa.
Sai wannan lokacin Chief ya taho wajen da backup harda ambulance dan tinda aka harbi Maleeka dama suka nemi taimakon ambulance.
Kan kace mai an soma basu taimako na gaggawa.
Assad aka fara baiwa taimako dan yafi kowa buk’atan taimakon.
Mu’azzam ya k’araso da sauri lokacin da aka d’aura Assad saman doguwar gadon tura marassa lafiya. Hannun Assad ya kama yana fad’in “Zaka samu lafiya brother.. In sha Allah..!”
Cikin jin jiki Assad ya bud’e idanunsa da k’yar kafin ya murmusa ya jinjina ma Mu’azzam kai yace “Ina Sadiya.. Did you save her..?”
Mu’azzam ya jinjina masa kai yace “She’s dafe now..” Ya d’aga masa babban yatsarsa alamun jinjina yana mai sakar masa murmushi da k’yar.
Lokaci guda aka tura Assad cikin ambulance kafin aka saka masa na’uran oxygen.
Yusuf ya dubi Mu’azzam yace “Zan kula da Assad.. Just go to your wife.” Yai masa nuni da ido zuwa cikin motar yanda Sadiya ke tak’ure waje guda.
Jinjina kai Mu’azzam yai kafin ya d’an dafa kafad’an Yusuf alamun godiya.
Lokaci guda Yusuf ya shige cikin ambulance d’in..
**
Safeenah da taga Mommy bazata d’auki wayarta ba sai ta yanke shawarin kiran Aunty Shemau. Da kuka ta soma ma Aunty Shemau tana fad’in Mommy tana fushi da ita bata d’aga wayarta.
Aunty Shemau ta tab’e baki kad’an tace “Safeenah ni fah na baro gidanku tin daren jiya.. Your Uncle came ya d’aukeni mun taho masauk’insa tare.”
Safeenah tace “Aunty Toh ni yanzu ya zanyi da Mu’azzam ne.. Wllhi Aunty ko kallo fah ban ishesa ba dan Allah kizo ki yanzu..” Ta k’arashe wasu hawayen na gangaro mata.
Aunty Shemau Ta dubi mijinta dake zaune gefe kafin ta d’an sauk’e ajiyan zuciya tace “Shikenan Safeenah zan tambayi Uncle d’in naku idan ya barni zaki ganni..”
Cikin kuka Safeenah tace “Aunty idan Uncle Salman d’in na kusa put him through zan tambayesa da kaina.”
Aunty Shemau ta murmusa kafin tace “Kar Safeenah ina nan zuwa kinji koh.. Kiyi hak’uri. Yauwa sai nazo..” Daga haka katse kiran tai tana duban mijinta da ya kafeta da idanu.
“Mai wannan shashashar kuma take buk’ata..?” Ya tambaya yana duban Shemau.
“Banda akan Mu’azzam.. Kasan ita wannan batada tinani batada hankali sam indai akan Mu’azzam ne.. So take naje gidan nata ta rasa abinyi..”
Uncle Salman ya jinjina kai kafin yace “A tak’aice dai zuwanki garin nan baiyi amfani ba Shemau.. Kin kasa d’auko min wad’annan Documents d’in.. Wad’anda idan na mallakesu tamkar na mallaki kaso na dukiyar Mu’azzam ne da d’anuwana ya handame..”
Chief yai tsaye yana dubansu yanda kowa ke sauri cikinsu sai shirya alburusai suke cikin bindigoginsu. Yusuf na sanar dasu wani tsohon building ne Danger yake can wajen gari.
Assad ya sarawa Chief yana fad’in “We were able to trace Danger’s location, Sir.”
Dikda Zuciyar Chief Ta yanke hakan bai hanasa nuna Farin cikinsa a fili ba.. Yana tafe hannayensa yake fad’in “Then what are we waiting for Detectives.. Move it, faster.. Let’s catch Danger.!” Ya fad’i yana tafe hannayensa alamun Su k’ara sauri.
A haka suka dinga ficewa har dai Mu’azzam yazo ficewa, suka tsaya suna duban juna shida Chief.
Murmushi Chief ya sakar masa kafin yace “Well done Inspector Gamji.. I must congratulate you and your team..”
Murmushi da gefen bakin Mu’azzam ya sakar masa yana Soka bindigarsa jikin belt d’insa kafin yace “Tukunna ma Sir.. Sai kaga Danger da accomplices d’insa behind bars.” Yana ida fad’in haka ya sarawa Chief kafin yasa kai ya shige.
Chief yabi bayansa da mugun kallo yana huci, lokaci guda yake duban allon binciken nasu nan yaga an zana circle an rubuta B.A.T a sama ga kuma question mark cikin circle d’in.. Anyi linking circle d’in da hoton Danger. Zuciyr Chief yai wani irin bugawa.. Gumi ya shiga ketowa Chief tako Ta ina.. Kar dai Maleeka ta sanar da Mu’azzam wani abu akan BAT.. Lallai Maleeka tana wasa da rayuwarta. Ya lura komai zatayi akan Mu’azzam.
Cikin tsananin fushi mai gauraye da tashin hankali Chief ya daki garu kafin yasa kai ya fice daga ofishin.
Kallon da Chief yaiwa Maleeka tasan cewa akwai matsala, tasa kai Ta shige cikin sauri zuciyarta na yankewa.
Mu’azzam ne ya rarraba masu bulletproof vests ko wannensu ya aza saman rigarsa, gaba d’ayansu motar Office suka shiga. Assad ke driving Mu’azzam na gefensa Yusuf da Maleeka suna mazaunin baya.
Saidai suna isa sukaji an soma kaima motarsu attack da harbi alamun su Danger Sun riga sun San da zuwansu an sanar dasu. Take sukai holding positions d’insu Mu’azzam na fad’in”No one shoot.. My wife is in there..”
Suka jinjina kai suna fad’in copy. Su Danger suka ci gaba da harbi kafin daga bisani wutan ya tsagaita.
Mu’azzam ne yai masu alama da hannu da ido kan su soma matsowa kusa suna nufan ginin cikin kwanton b’auna. Haka kuwa akai a hankali suka dinga matsawa kusa cikin bin umarnin Mu’azzam har suka isa ginin..
Wani mutumi sanye da bak’ak’en tufafi fuskarsa rufe da bak’in mask shine yai saitin Mu’azzam zai harbesa ba tareda Mu’azzam d’in ya gansa ba Maleeka ta k’arasa da sauri ta tare wa Mu’azzam harsashin tana kiran sunansa dan ita taga mutumin.. Take harsashin ya sameta a hannunta.. Gaba d’aya suka juyo suna duban Maleeka da ta karb’ewa Mu’azzam harsashi ta duk’a wajen tana cije lab’e rik’e da hannuta yanda harsashi ya huda jini na zuba.. Yusuf da Assad suka k’araso a guje suna ambato sunan Maleeka yayinda Mu’azzam yai Chasing mutumin a guje.. Gini ne upstairs mai tsawo irin abandon gini d’in nan wanda zallan Kango ne.. Haka mutumin ya dinga haurawa sama a guje yana sakowa Mu’azzam harsashai Mu’azzam na kaucewa yana kuma chasing d’insa dan a raye yake son capke Sa. Saida ya bari Mu’azzam ya isa sama saura kad’an ya kamasa kafin ya dirk’o yana kuma kai masa harbi.. Mu’azzam ya kama jikin bargwajajjen staircase din kenan zai dirk’o yabi bayansa yaji kaman kukan mutum cikin wani d’aki dake rufe .. Cikin sauri ya juyo yana duban d’akin ya daina chasing mutumin..
A hankali ya furta “Sadee.!”
Da k’afarsa ya daki k’ofar saida ya b’allata.. Can ya hangota d’aure saman kujera idanunta a rufe haka ma bakinta.. Jikinsa har rawa yake ya isa a guje ya cire blindfold d’in da aka rufe mata ido dashi..
Suna had’a ido taji wani irin kuka yazo mata.. Lokaci guda yaci gaba da kwanceta yana fad’in “It’s okay.. You’re safe now..!” Ya k’arashe yana mai rungumarta cikin jikinsa.
Wani kukan Ta kuma fashewa dashi jikinta sai rawa yake alamun bak’ar azaba yunwa da galabaita had’ida tsananin tsoro da tashin hankalin da Ta tsinci kanta ciki.
Kaman wacce ta tuna wani abu tai k’ok’arin cire jikinta daga nasa ta shiga girgiza kai tana k’ok’arin matsawa da baya take fad’in “No no no.. Don’t touch me.. Kar ka tab’a ni kar kazo kusana..”
“How do I save you idan ban tab’a ki ba.!” Yai maganar cikin daka tsawa..
Juyawan da zai yaji kaman abu na reading ashe bomb ne a gefe Danger ya aje ma Sadiya da niyyan k’onata.
Mu’azzam bai kuma sauraronta ba ya shiga girgiza kai yana furta “Oh shit..! Come here now..” Ya sunkuceta tamkar Baby ya soma gudu da ita tana cikin hannunsa sai had’e stirs yake yana tsallakewa gudun kar bomb d’in Ta tashi dasu suna cikin ginin.
A can waje kuwa Maleeka dai tana fama da hannunta da aka harba Assad da Yusuf ne sukai chasing mutumi mai bak’in kayan bayan ya samu fitowa daga building d’in.. Suna guje suna bata kashi tsakaninsu.. Nan harsashi ya samu Assad gefen wuyarsa kusan kafad’arsa yanda Bulletproof vest d’in bai rufe ba.. Ya duk’a a wajen yana kame wuyarsa da tuni jini ya soma kwarara..
Yusuf ya dakata da chasing mai bak’in kaya ya duk’a yana duba Assad dake cikin pain yana k’ok’arin taimakawa d’anuwansa.
A can building d’in kaw wata jahilar tsalle Mu’azzam yai still tana rik’e cikin hannunsa daidai sanda Bomb d’in tai exploding..
Haka ya kwanta kan Sadiya ya rufeta ruf sand bomb d’in ta tashi dan ma kar wani abu ya sameta.
Maleeka ma ta juyar da fuskarta tana mai kwanciya flat a k’asa sanda bomb d’in tai exploding.
A hankali komai ke lafawa. Mu’azzam ya mik’e da k’yar yana jijjiga Sadiya dake kwance k’asar sa wacce ta koma tamkar bata numfashi.
Maleeka ta bud’e idanunta da k’yar tana duban Mu’azzam dake ci gaba da jijjiga Sadiya yana fad’in Ta bud’e idanunta.
Lokaci guda yaci gaba da jijjigata yana fad’in “No.. No.. Stubborn head.. Not now.. Please wake up.. Wake up.. wake up now..!” Yana maganar yana jijjigata.
Dukda rad’ad’in ciwon dake jikin Maleeka bai hanata zuba idanu tana dubansu kaman Ta samu TV.. Tinda take bata tab’a ganin Mu’azzam ya birkice kan wata mace ba sai wannan yarinyar.. For the first time da zata iya cewa taga Mu’azzam Gamji dumu dumu cikin kogin soyayya..
Haka ya dinga jijjiga Sadiya yana fad’in Ta tashi.. K’arshe bakinsa ya d’aura saman nata yana hura mata iska..
Maleeka kaw ji tai wani abu ya tokare mata mak’oshi sanda tanga Mu’azzam ya saka bakinsa saman na Sadiya. Tai saurin rintse idanunta had’ida ciza labb’anta.. Shekara da shekaru tana kwad’ayin irin haka ya kasance tsakaninsu sai gashi yau d’in tanaji tana gani a gabanta yake saka bakinsa cikin na wata.. Ji tai zafin ciwon da taji dominsa na k’aruwa.. Ta kuma rintse idanunta da k’arfin gaske hawaye mai zafi na gangaro mata.
Wani dogon numfashi Sadiya taja had’ida bud’e idanunta. Bai wata wata ba ya mak’aleta tsam cikin jikinsa kaman mai tsoron kar wani abu ya kuma raba tsakaninsu.
Daidai lokacin Su Assad da Yusuf suka k’araso. Yusuf na tallafe da Assad wanda jini ke zuba sosai daga jikinsa. Cikin sauri Mu’azzam ya bud’e mota ya zaunar da Sadiya ciki kafin ya k’araso wajen abokansa. Assad ko iya bud’e idanunsa bayayi dan sosai harsashin ta shigesa gashi a waje mai had’ari harsashin ya samesa.
Sai wannan lokacin Chief ya taho wajen da backup harda ambulance dan tinda aka harbi Maleeka dama suka nemi taimakon ambulance.
Kan kace mai an soma basu taimako na gaggawa.
Assad aka fara baiwa taimako dan yafi kowa buk’atan taimakon.
Mu’azzam ya k’araso da sauri lokacin da aka d’aura Assad saman doguwar gadon tura marassa lafiya. Hannun Assad ya kama yana fad’in “Zaka samu lafiya brother.. In sha Allah..!”
Cikin jin jiki Assad ya bud’e idanunsa da k’yar kafin ya murmusa ya jinjina ma Mu’azzam kai yace “Ina Sadiya.. Did you save her..?”
Mu’azzam ya jinjina masa kai yace “She’s dafe now..” Ya d’aga masa babban yatsarsa alamun jinjina yana mai sakar masa murmushi da k’yar.
Lokaci guda aka tura Assad cikin ambulance kafin aka saka masa na’uran oxygen.
Yusuf ya dubi Mu’azzam yace “Zan kula da Assad.. Just go to your wife.” Yai masa nuni da ido zuwa cikin motar yanda Sadiya ke tak’ure waje guda.
Jinjina kai Mu’azzam yai kafin ya d’an dafa kafad’an Yusuf alamun godiya.
Lokaci guda Yusuf ya shige cikin ambulance d’in..
**
Safeenah da taga Mommy bazata d’auki wayarta ba sai ta yanke shawarin kiran Aunty Shemau. Da kuka ta soma ma Aunty Shemau tana fad’in Mommy tana fushi da ita bata d’aga wayarta.
Aunty Shemau ta tab’e baki kad’an tace “Safeenah ni fah na baro gidanku tin daren jiya.. Your Uncle came ya d’aukeni mun taho masauk’insa tare.”
Safeenah tace “Aunty Toh ni yanzu ya zanyi da Mu’azzam ne.. Wllhi Aunty ko kallo fah ban ishesa ba dan Allah kizo ki yanzu..” Ta k’arashe wasu hawayen na gangaro mata.
Aunty Shemau Ta dubi mijinta dake zaune gefe kafin ta d’an sauk’e ajiyan zuciya tace “Shikenan Safeenah zan tambayi Uncle d’in naku idan ya barni zaki ganni..”
Cikin kuka Safeenah tace “Aunty idan Uncle Salman d’in na kusa put him through zan tambayesa da kaina.”
Aunty Shemau ta murmusa kafin tace “Kar Safeenah ina nan zuwa kinji koh.. Kiyi hak’uri. Yauwa sai nazo..” Daga haka katse kiran tai tana duban mijinta da ya kafeta da idanu.
“Mai wannan shashashar kuma take buk’ata..?” Ya tambaya yana duban Shemau.
“Banda akan Mu’azzam.. Kasan ita wannan batada tinani batada hankali sam indai akan Mu’azzam ne.. So take naje gidan nata ta rasa abinyi..”
Uncle Salman ya jinjina kai kafin yace “A tak’aice dai zuwanki garin nan baiyi amfani ba Shemau.. Kin kasa d’auko min wad’annan Documents d’in.. Wad’anda idan na mallakesu tamkar na mallaki kaso na dukiyar Mu’azzam ne da d’anuwana ya handame..”