Sashe 105
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin sauri Safeenah har tana girgiza kai take fad’in “A’a ni bance ki kasheta ba Aunty.. Kawai ki illata shegiya yanda bazata samu damar dawowa ba yanda ma bazata kuma amfanarsa ba. Ki karya mun k’afar munafuka ko ki lak’a mata wani babban sharri.. Ki tura namiji d’akinta kiyi kururuwa ki had’a mata jama’a nayi imani idan Mu’azzam yaji haka ya rabu da Ita kenan rabuwa ta har abada..”
Shemau ta numfasa kad’an cikin zuciyarta tana ayyana cewa Wato anama Safeenah kallon shashasha idan akan D’ansandan nan ne tsaf zatai tunanin makirci iri daban daban dan burinta ya cika.
Ta d’an nusa tace “Feenah Kinsan had’arin abinda kike fad’i kuwa.. Idan plan d’in yai backfiring fah ba ke kad’ai ba harta ni zan sami matsala bada Uncle d’inku kawai ba harta da Inne sai na sami matsala dan na tabbata ko Mu’azzam bai kulle ni a cell ba Inne zata koreni.. Ta inama zan gayyato mata kwarto cikin gidan gonar nan..? Bayan Kinsan kalan tsaron dake cikin gidan gonar.
Safeenah ta d’an rausayar da idanunta cikeda k’osawa tace “Aunty bamuda wani zab’i kawai kisan yanda zakiyi ki lak’a mata wann sharrin shi kad’ai ne zaisa Mu’azzam yaji ya washeta bai ko k’aunar jin mai irin sunanta balle ya ganta.. Haba Aunty Shema ki tausaya min na karkato da akalar hankalin mijina gareni..”
Aunty Shemau ta nusa tace “But Safeenah kinsan fah komai a rayuwar nan yanada price..”
Safeenah Ta jinjina kai tace “K’warai kuwa na sani Aunty.. Wllhi idan kika mun haka.. Idan kika taimakeni tsinanniyar nan Ta fice daga rayuwar Mu’azzam ni kuma zan miki komai ko mai kika umarceni na miki zan miki shi without giving it a thought.. I’ll do whatever it takes dan na tabbata Karuwar nan Ta b’ace b’at daga rayuwar my Halal.. Please Aunty Shemau ki taimakeni Kimin wann..”
Aunty Shemau ta jinjina kai dan ta tabbata yanda Safeenah tace d’in zatayi komai “Toh shikenan Safeenah.. Zan taimakeki zan gayyato mata kwarto har cikin d’akinta yazo mana da sauk’i tinda a d’akin uwar Mu’azzam take kwana, Kinga idan Ta fice sai mu turosa ya shiga da safe tana dawowa a kamata dashi a d’akin. Ni kuma zan tara mata jama’a.. Kinga tun kafin labari ya isa ga Mu’azzam jarabebbiyar Kakarku zata kori shegiya dangin mayu..”
Safeenah ta sauk’e ajiyan zuciya cikeda jin dad’i tana mai sakin murmushi “Aunty kin gama mun komai nan gidan duniya idan har kika mun wann.. Ki fad’a ko me kike so daga wajena kin same shi babu tantama.”
Shemau ta murmusa cikeda jin dad’i tace “Zan fad’a miki abinda nake so ki mun.. But for now bari mu cire Sadiya cikin hoton..”
Suka shek’e da dariya a tare kafin sukai sallama.
Cikin sand’a Musaddiq ya bar wajen yana nanata iyaka abubuwan da yaji suna fita daga Bakin Aunty Shemau. Ya fahimci sunaso Su k’ulla wa matar Mu’azzam sharri ne itada ‘yar uwarsa Safeenah. Ya girgiza kai kad’an ba tareda yace komai ba. Zama yai saman kujera ya d’aura hab’arsa saman hannayensa da ya dunk’ulesu waje guda tinani fal zuciyarsa.
Aunty Shemau kaw suna ida waya da Safeenah ta nufi sashen Sadiya.
A k’ofa suka had’u da Sadiya zata shashen Inne.
Ta sakar mata murmushi tana dubanta “A’a Amarya kar dai fita zakiyi..?”
Sadiya ta murmusa kad’an kafin ta d’an risina ta gaida Aunty Shemau.
“Dama sashen Inne na nufa Aunty..”
Aunty Shemau ta murmusa kafin tace “Koda yake ma ina kika sani a garin nan balle ki fita.. Kuma dai ya kamata ki d’an fita kiga gari kafin ki gama hutunki ko yaya Kikace..?”
Murmusawa ta d’anyi kad’an tana gyara zaman mayafinta ba tareda tace komai ba. Sai kuma tace “Aunty Mu shiga ciki ki sha ruwa na barki tsaye.”
Aunty Shemau ta murmusa tace “Aiko ba a k’in tayin shan ruwan gidan Amarya.. Ruwan gidan Amarya zak’i ne dashi..” Ta k’arashe cikeda barkwanci.
Sadiya dai sai murmushi kurum take. Lokaci guda ta juya ta bud’e masu k’ofa suka shige Parlorn.
Aunty Shemau Ta soma bin parlorn da kallo sai kace ranan ta soma shiga. Tai zaune saman kujera k’afafu d’aya bisa d’aya ta d’aga kai sama tana ‘yan kalle kalle “Wai! Dank’ari lallai an kashe Kud’i a parlorn nan.. Kaga kaya kaman order d’insu akai daga waje.. Gidan Amarya dai dik yanda yake akwai santi. Sai ya tuna min lokacin da na raka Aunty Hajara mukai sayayyan kayan auren Safeenah a Dubai da Qatar.. Ni wasu abubuwan ma sunmin kama da na Safeenah..” Ta k’arashe tana kuma dube dube.
Jikin Sadiya ya d’anyi sanyi dai dai lokacin da take aje drinks gaban Aunty Shemau.
Shemau taci gaba da fad’in “Ai iyaye gaskiya suna k’ok’arin kashe Kud’i wajen aurar da yaransu mata. Duk dukiyar nan da ake kashewa wani sa’in sai kiga aure bai kya ba.. Shiyasa ni bana goyon bayan kashe kud’i da gidan mata suke a aure.. Ka gama kashe kud’i ka sai ma d’iyarka kayan d’aki na gani a fad’i ba shi zai hana namiji ya faskara mata rashin mutunci ba. Dai dai da warmers na zuba masa abinci sai an saya.. Yana cin abincin yana danna wa ubanta ashar.. Namiji kenan k’anin ajali..” Ta k’arashe tana kurb’an drink d’in.
Ta d’anyi gyaran murya kad’an kafin tace “Ai ke kinada sa’a da naki iyayen basu wahala kan namiji ba.. Duk wann kayan alatun danginsa suka zuba abinsu.. Ai naga tulin kud’ad’en da Inne tasa aka fitar sanda za’a gyarawa Mu’azzam wann b’angaren da shike lokacin da sunan Safeenah aka gyara sashen nan.. Da yanzu komai nata ne a nan.. Saidai kana Naka ne Allah na nashi.. Na Allah shine daidai dama ya tsaga rabonki ne.. Yo ba dole ma a shak’e gidan nan da kaya masu kyau da tsada ba sabida ansan Safeenah da son k’yale k’yale da gayu..” Tai maganar tana kurb’ar drink.
Jikin Sadiya yai matuk’ar yin sanyi da jin irin abubuwan da Aunty Shemaubke fad’i.. Ta sadda kanta k’asa d’ago sai tanaji kaman ita d’in ta tauye hakkokin Safeenah da yawa. Na farko Ta soma tarewa gidan Safeenar tin a can Abuja kafin Safeenah Ta shiga gidan yanzu gashi gidan da aka gina ma da sunar Safeenar ya zama nata.. Anya wann ba rashin adalci bane..? Bata kaiga nemo amsa ba ta sinkayo muryar Aunty Shemau naci gaba da fad’in “Kinga randa ya tasamma maki halin nasu na maza abin bazai ma iyayenki ciwo sosai ba..”
Gaba d’aya jikin Sadiya a sanyaye yake, kanta a k’asa tana sakin murmushin da daga gani kasan na yak’e ne.
Aunty Shemau taci gaba da fad’in “K’ila al’adarku ce maza ke yin kayan d’aki..?”
Sadiya ta d’an girgiza kai cikin rashin sakewa tace “A’a Aunty Al’ada iri guda mukeda shi.. Gidan mata keyin kayan d’aki.. Nawa iyayen ne basu da hali..Kuma ni marainiya ce banida kowa sai mahaifiyata da k’annena..”
Aunty Shemau tai rau rau da idanu ta taso da sauri ta dafa Sadiya tana fad’in “Allah sarki ‘yar nan.. Kiyi hak’uri Bansan haka abin yake ba.. Kiyi hak’uri kinji.. Allah sarki ashe dai ked’in marainiya ce.. Allah sarki bansan haka ba..”
Sadiya ta murmusa kad’an Wanda yafi kama da yak’e tace “Babu komai Aunty.. Ki daina bani hak’uri dan Allah..”
Aunty Shemau tace “Yo dole na baki hak’uri Amarya am.. Bansan ke marainiya bace.. Amma a halin yanzu ke ba marainiya bace dan tinda kika shigo ahali irin wann maraici ya k’are miki..”
Ta murmusa kad’an tana sadda kai.
Aunty Shemau ta tsareta da idanu cikin zuciyarta tana fad’in ‘kaji munafuka yanda take wane sanne kai’
A fili kuwa gyaran murya ta kumayi tana d’an dafa Sadiyar “Amma naji kince Bakida kowa..Sai mahaifiyarki da ‘yanuwanki. Toh ina ahalinki suke.. Dangin mahaifiya ko na mahaifi..?”
Zuciyar Sadiya yai wani irin yankewa dan batasan Ta yanda zata soma sanar da Aunty Shemau Dangin mahaifinta sun gujesu tun kafin a haifeta sabida zab’an mahaifiyarta da yayi a matsayin wacce zata zamto abokiyar rayuwarsa. ko kuma dangin mahaifiyarta da batasan duniyar da suke ba.. Bata kai ga bata amsa ba sallamar Mama Hindu ya katse su.
Hamdala tai cikin zuciyarta dan zuwan Hindu ya ceceta daga amsa tambayar Aunty Shemau.
Mama Hindu Ta sanar da Ita Inne ke kiranta. Cikin sauri kaman wacce take jira Ta mik’e tana amsawa.
Aunty Shemau ta d’auki sauran drink d’in da Sadiya ta had’a ta kawo mata tana sha tana fad’in zata Zo a koya mata irin wann drink d’in dan ta lurar hannun amaryar tasu nada albarka. Sai santin drink d’in take.
Sadiya tace “Aunty bari akai miki dama na had’a maku ne dasu Inne.. An kai na Inne tintinin dama na k’ofarki ne ban kai ba nace sai zuwa anjima zan kai..”
Aunty Shemau ta d’auka tana fad’in “Allah Sarki Amarya mai ruwan zak’i.. Toh bara na hutasarki na tafi dashi, ai kaw Uncle Salman na son irin wad’ann fresh drinks d’in da babu wani chemicals ciki babu preservatives..”
Mama Hindu ta amsa jug d’in daga hannun Aunty Shemau tana fad’in bari ta kai mata.
A tare suka jera suka nufo sashen Inne da Shemau da Sadiyar.
Suka gaida Inne gaba d’ayansu dan a parlor suka taddata.
Inne Ta dubi Shemau tace “Wai har yanzu ‘Yan biyu basu ida hutun nasu bane bazasu dawo haka nan ba.”
Shemau ta murmusa cikeda jin dad’in Inne na kewar jikokinta “Dama satin dama za’a d’aukosu Inne..”
Jinjina Kai Inne tai tace “Allah ya kaimu.. Ai gwara su dawo haka nan.. Da k’iriniyar tasu a waje yafi.. K’aramin k’afa a waje da dad’i..”
Shemau sai murmusawa take cikeda jin dad’i tana fad’in “Za’a d’auko Su Inne..”
Inne Ta dubi Sadiya tace “Kinyi magana da mijin naki ne..?”
Sadiya ta girgiza kai kad’an tana sadda kai k’asa “A’a Inne bamuyi magana yau ba..”
Inne Ta jinjina kai tace “Taw, nasan zai kiraki ya sanar dake... Adnan yana hanya yau.. Zuwa gobe in sha Allah zai d’aukeki zaku koma.. Sai ki fara shiri ko..”
Shemau ta numfasa kad’an cikin zuciyarta tana ayyana cewa Wato anama Safeenah kallon shashasha idan akan D’ansandan nan ne tsaf zatai tunanin makirci iri daban daban dan burinta ya cika.
Ta d’an nusa tace “Feenah Kinsan had’arin abinda kike fad’i kuwa.. Idan plan d’in yai backfiring fah ba ke kad’ai ba harta ni zan sami matsala bada Uncle d’inku kawai ba harta da Inne sai na sami matsala dan na tabbata ko Mu’azzam bai kulle ni a cell ba Inne zata koreni.. Ta inama zan gayyato mata kwarto cikin gidan gonar nan..? Bayan Kinsan kalan tsaron dake cikin gidan gonar.
Safeenah ta d’an rausayar da idanunta cikeda k’osawa tace “Aunty bamuda wani zab’i kawai kisan yanda zakiyi ki lak’a mata wann sharrin shi kad’ai ne zaisa Mu’azzam yaji ya washeta bai ko k’aunar jin mai irin sunanta balle ya ganta.. Haba Aunty Shema ki tausaya min na karkato da akalar hankalin mijina gareni..”
Aunty Shemau ta nusa tace “But Safeenah kinsan fah komai a rayuwar nan yanada price..”
Safeenah Ta jinjina kai tace “K’warai kuwa na sani Aunty.. Wllhi idan kika mun haka.. Idan kika taimakeni tsinanniyar nan Ta fice daga rayuwar Mu’azzam ni kuma zan miki komai ko mai kika umarceni na miki zan miki shi without giving it a thought.. I’ll do whatever it takes dan na tabbata Karuwar nan Ta b’ace b’at daga rayuwar my Halal.. Please Aunty Shemau ki taimakeni Kimin wann..”
Aunty Shemau ta jinjina kai dan ta tabbata yanda Safeenah tace d’in zatayi komai “Toh shikenan Safeenah.. Zan taimakeki zan gayyato mata kwarto har cikin d’akinta yazo mana da sauk’i tinda a d’akin uwar Mu’azzam take kwana, Kinga idan Ta fice sai mu turosa ya shiga da safe tana dawowa a kamata dashi a d’akin. Ni kuma zan tara mata jama’a.. Kinga tun kafin labari ya isa ga Mu’azzam jarabebbiyar Kakarku zata kori shegiya dangin mayu..”
Safeenah ta sauk’e ajiyan zuciya cikeda jin dad’i tana mai sakin murmushi “Aunty kin gama mun komai nan gidan duniya idan har kika mun wann.. Ki fad’a ko me kike so daga wajena kin same shi babu tantama.”
Shemau ta murmusa cikeda jin dad’i tace “Zan fad’a miki abinda nake so ki mun.. But for now bari mu cire Sadiya cikin hoton..”
Suka shek’e da dariya a tare kafin sukai sallama.
Cikin sand’a Musaddiq ya bar wajen yana nanata iyaka abubuwan da yaji suna fita daga Bakin Aunty Shemau. Ya fahimci sunaso Su k’ulla wa matar Mu’azzam sharri ne itada ‘yar uwarsa Safeenah. Ya girgiza kai kad’an ba tareda yace komai ba. Zama yai saman kujera ya d’aura hab’arsa saman hannayensa da ya dunk’ulesu waje guda tinani fal zuciyarsa.
Aunty Shemau kaw suna ida waya da Safeenah ta nufi sashen Sadiya.
A k’ofa suka had’u da Sadiya zata shashen Inne.
Ta sakar mata murmushi tana dubanta “A’a Amarya kar dai fita zakiyi..?”
Sadiya ta murmusa kad’an kafin ta d’an risina ta gaida Aunty Shemau.
“Dama sashen Inne na nufa Aunty..”
Aunty Shemau ta murmusa kafin tace “Koda yake ma ina kika sani a garin nan balle ki fita.. Kuma dai ya kamata ki d’an fita kiga gari kafin ki gama hutunki ko yaya Kikace..?”
Murmusawa ta d’anyi kad’an tana gyara zaman mayafinta ba tareda tace komai ba. Sai kuma tace “Aunty Mu shiga ciki ki sha ruwa na barki tsaye.”
Aunty Shemau ta murmusa tace “Aiko ba a k’in tayin shan ruwan gidan Amarya.. Ruwan gidan Amarya zak’i ne dashi..” Ta k’arashe cikeda barkwanci.
Sadiya dai sai murmushi kurum take. Lokaci guda ta juya ta bud’e masu k’ofa suka shige Parlorn.
Aunty Shemau Ta soma bin parlorn da kallo sai kace ranan ta soma shiga. Tai zaune saman kujera k’afafu d’aya bisa d’aya ta d’aga kai sama tana ‘yan kalle kalle “Wai! Dank’ari lallai an kashe Kud’i a parlorn nan.. Kaga kaya kaman order d’insu akai daga waje.. Gidan Amarya dai dik yanda yake akwai santi. Sai ya tuna min lokacin da na raka Aunty Hajara mukai sayayyan kayan auren Safeenah a Dubai da Qatar.. Ni wasu abubuwan ma sunmin kama da na Safeenah..” Ta k’arashe tana kuma dube dube.
Jikin Sadiya ya d’anyi sanyi dai dai lokacin da take aje drinks gaban Aunty Shemau.
Shemau taci gaba da fad’in “Ai iyaye gaskiya suna k’ok’arin kashe Kud’i wajen aurar da yaransu mata. Duk dukiyar nan da ake kashewa wani sa’in sai kiga aure bai kya ba.. Shiyasa ni bana goyon bayan kashe kud’i da gidan mata suke a aure.. Ka gama kashe kud’i ka sai ma d’iyarka kayan d’aki na gani a fad’i ba shi zai hana namiji ya faskara mata rashin mutunci ba. Dai dai da warmers na zuba masa abinci sai an saya.. Yana cin abincin yana danna wa ubanta ashar.. Namiji kenan k’anin ajali..” Ta k’arashe tana kurb’an drink d’in.
Ta d’anyi gyaran murya kad’an kafin tace “Ai ke kinada sa’a da naki iyayen basu wahala kan namiji ba.. Duk wann kayan alatun danginsa suka zuba abinsu.. Ai naga tulin kud’ad’en da Inne tasa aka fitar sanda za’a gyarawa Mu’azzam wann b’angaren da shike lokacin da sunan Safeenah aka gyara sashen nan.. Da yanzu komai nata ne a nan.. Saidai kana Naka ne Allah na nashi.. Na Allah shine daidai dama ya tsaga rabonki ne.. Yo ba dole ma a shak’e gidan nan da kaya masu kyau da tsada ba sabida ansan Safeenah da son k’yale k’yale da gayu..” Tai maganar tana kurb’ar drink.
Jikin Sadiya yai matuk’ar yin sanyi da jin irin abubuwan da Aunty Shemaubke fad’i.. Ta sadda kanta k’asa d’ago sai tanaji kaman ita d’in ta tauye hakkokin Safeenah da yawa. Na farko Ta soma tarewa gidan Safeenar tin a can Abuja kafin Safeenah Ta shiga gidan yanzu gashi gidan da aka gina ma da sunar Safeenar ya zama nata.. Anya wann ba rashin adalci bane..? Bata kaiga nemo amsa ba ta sinkayo muryar Aunty Shemau naci gaba da fad’in “Kinga randa ya tasamma maki halin nasu na maza abin bazai ma iyayenki ciwo sosai ba..”
Gaba d’aya jikin Sadiya a sanyaye yake, kanta a k’asa tana sakin murmushin da daga gani kasan na yak’e ne.
Aunty Shemau taci gaba da fad’in “K’ila al’adarku ce maza ke yin kayan d’aki..?”
Sadiya ta d’an girgiza kai cikin rashin sakewa tace “A’a Aunty Al’ada iri guda mukeda shi.. Gidan mata keyin kayan d’aki.. Nawa iyayen ne basu da hali..Kuma ni marainiya ce banida kowa sai mahaifiyata da k’annena..”
Aunty Shemau tai rau rau da idanu ta taso da sauri ta dafa Sadiya tana fad’in “Allah sarki ‘yar nan.. Kiyi hak’uri Bansan haka abin yake ba.. Kiyi hak’uri kinji.. Allah sarki ashe dai ked’in marainiya ce.. Allah sarki bansan haka ba..”
Sadiya ta murmusa kad’an Wanda yafi kama da yak’e tace “Babu komai Aunty.. Ki daina bani hak’uri dan Allah..”
Aunty Shemau tace “Yo dole na baki hak’uri Amarya am.. Bansan ke marainiya bace.. Amma a halin yanzu ke ba marainiya bace dan tinda kika shigo ahali irin wann maraici ya k’are miki..”
Ta murmusa kad’an tana sadda kai.
Aunty Shemau ta tsareta da idanu cikin zuciyarta tana fad’in ‘kaji munafuka yanda take wane sanne kai’
A fili kuwa gyaran murya ta kumayi tana d’an dafa Sadiyar “Amma naji kince Bakida kowa..Sai mahaifiyarki da ‘yanuwanki. Toh ina ahalinki suke.. Dangin mahaifiya ko na mahaifi..?”
Zuciyar Sadiya yai wani irin yankewa dan batasan Ta yanda zata soma sanar da Aunty Shemau Dangin mahaifinta sun gujesu tun kafin a haifeta sabida zab’an mahaifiyarta da yayi a matsayin wacce zata zamto abokiyar rayuwarsa. ko kuma dangin mahaifiyarta da batasan duniyar da suke ba.. Bata kai ga bata amsa ba sallamar Mama Hindu ya katse su.
Hamdala tai cikin zuciyarta dan zuwan Hindu ya ceceta daga amsa tambayar Aunty Shemau.
Mama Hindu Ta sanar da Ita Inne ke kiranta. Cikin sauri kaman wacce take jira Ta mik’e tana amsawa.
Aunty Shemau ta d’auki sauran drink d’in da Sadiya ta had’a ta kawo mata tana sha tana fad’in zata Zo a koya mata irin wann drink d’in dan ta lurar hannun amaryar tasu nada albarka. Sai santin drink d’in take.
Sadiya tace “Aunty bari akai miki dama na had’a maku ne dasu Inne.. An kai na Inne tintinin dama na k’ofarki ne ban kai ba nace sai zuwa anjima zan kai..”
Aunty Shemau ta d’auka tana fad’in “Allah Sarki Amarya mai ruwan zak’i.. Toh bara na hutasarki na tafi dashi, ai kaw Uncle Salman na son irin wad’ann fresh drinks d’in da babu wani chemicals ciki babu preservatives..”
Mama Hindu ta amsa jug d’in daga hannun Aunty Shemau tana fad’in bari ta kai mata.
A tare suka jera suka nufo sashen Inne da Shemau da Sadiyar.
Suka gaida Inne gaba d’ayansu dan a parlor suka taddata.
Inne Ta dubi Shemau tace “Wai har yanzu ‘Yan biyu basu ida hutun nasu bane bazasu dawo haka nan ba.”
Shemau ta murmusa cikeda jin dad’in Inne na kewar jikokinta “Dama satin dama za’a d’aukosu Inne..”
Jinjina Kai Inne tai tace “Allah ya kaimu.. Ai gwara su dawo haka nan.. Da k’iriniyar tasu a waje yafi.. K’aramin k’afa a waje da dad’i..”
Shemau sai murmusawa take cikeda jin dad’i tana fad’in “Za’a d’auko Su Inne..”
Inne Ta dubi Sadiya tace “Kinyi magana da mijin naki ne..?”
Sadiya ta girgiza kai kad’an tana sadda kai k’asa “A’a Inne bamuyi magana yau ba..”
Inne Ta jinjina kai tace “Taw, nasan zai kiraki ya sanar dake... Adnan yana hanya yau.. Zuwa gobe in sha Allah zai d’aukeki zaku koma.. Sai ki fara shiri ko..”