Sashe 25
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shafa kansa Umma tai tace ya kan naka. Ya daina ciwo.?”
Ya jinjina mata kai yana bud’e ledar biscuit d’in dake d’aya hannunsa.
Umma ta Shafa kansa tace “Tashi ka shiga ciki koh ka bamu waje.”
Ya mik’e yana jinjina kai.. Yana shigewa Sadiya ta fuzge tarkacen da ya shigo dashi tai watsi dasu.
Kuka ya shigayi yana bori yana fad’in Maiyasa ta yar masa abinsa.. Ko takan kukan Ashir batabi ba ta shige d’aki zuciyarta na mata d’aci.
Umma da Alhaji Isyaku dik sunji abinda ya faru a kunnuwarsu..
Dikda jikin Alhaji Isyakun ya d’anyi sanyi bai fasa sanar da Umma buk’atarsa na son auren Sadiya ba..
Umma Ta murmusa cikeda takaici “Alhaji da ka daina wannan wahalan dan hukunci dai mun riga mun gama yankewa daga ni har Sadiya.. Kaje mun gode da niyyan taimako.”
Alhaji Isyaku yace “Baki fahimta ba Umma..”
“A’a ni dan Allah ka kirani da Uwani menene wani Umma.. Kaga Alhaji Takaba nake ba don tashin hankalin da muke ciki ba Ko barinka ka shigo gidan nan bazanyi ba.. Mun gode da kai Ashiru asibiti da kai dan Allah ina rok’onka ka tashi ka tattari kayyakinka ka tafi bamu buk’ata kuma kar ka sake dawo mana.”
Alhaji Isyaku ya murmusa kad’an yace “Umma kenan.. Barin fad’a miki kuna buk’ata na..”
Da mamaki Umma ke dubansa.
Alhaji Isyaku ya murmusa yana mai jinjina kai “ K’warai kuna buk’atana Umma.. Ya kamata ki sake tunani akan wannan al’amari.. Ki tuna makomar rayuwarku musamman yanzu da babu mahaifin yaranki.. Ki tuna halin rayuwa da zaku fuskanta.. Shin kina tunanin Sadiya zata samu miji ne bayan duk abubuwan da suka faru..? Kindai ji da kunnuwanki irin maganganun da mutanen unguwa keyi akan d’iyarki.. Kina tunanin akwai wanda zaizo ya aureta a haka..?” Ya kuma kannare idanu yana kuma duk’ar da kansa yace “Amma ni zan biya maku bashinku sannan zan auri d’iyarki na d’auketa daga garin nan, zan kaita can da nisa yanda babu wanda ya santa, gaba d’aynku ma zaku bar nan zaku koma sabon waje ku soma sabuwar rayuwa a can yanda babu tashin hankali babu komai..”
Umma da hawaye ke gangaro mata kafin takai ga furta wani kalma suka jiyo sallama daga waje.. Babu shiri Ta mik’e dan ba muryar kowa bane face Aminu dillalin da ya basu hayan gidan da suke ciki..
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kawai Umma ke nanatawa cikin zuciyarta.. Ta d’aga idanu tana duban glasses na window da Tabawa da ‘yandabanta suka fasa..
Umma murya na rawa take fad’i da Aminu “Malam Aminu Barka da Safiya..”
“Uwani ba wannan ya kawoni ba.. Zuwa nai dan na tabbata Kun fice daga gidan nan. Bazan d’auki asara irin haka ba.. Zamanku a gidan nan babu alkhairi dama baku biya kud’in hayan bara ba ga na bana.. Sabida mutuwar mijinki yasa na d’an d’aga maku k’afa. Nayi niyyan maku mutunci na barku ku zauna har ki ida takabanki kafin na sallameku amma Tunda abun ya zama haka gaskiya zaku tattara ku fice a gidan nan dan amana Alhaji ya bani.. Tinda nake masa dillancin gidajen hayansa a unguwar nan bamu tab’a samun matsala ba.. Bazan fara akanku ba, na kula masifa da tashin hankali bibiyarku suke Dan haka kawai ku biya kud’in hayanku ku k’ara gaba tin kafin Alhaji Sadi yaji wannan batu..”
Cikin rawar murya Umma ke fad’in “Malam Aminu dan Allah kai hak’uri ka taimakemu.. Ka rufa mana asiri yanda Allah ya rufa maka.. Idan muka tashi a nan bansan Ina zamuje ba.. Dan Allah kaji tausayinmu.. Ka bari Ko Takaban ne na gama.. Inada yara Malam Aminu bansan ina zan kaisu ba idan muka tashi a nan..”
Girgiza kai Malam Aminu yai yana duban wani gefen dan karma Ta basa tausayi “A’a Uwani.. Gaskiya bazan iya ba.. Gidan nan nima amana ce a hannuna, kawai ki daina rok’ona dan bazai yuwu kuci gaba da zama a nan ba.. Maganar gaskiya kenan..!” Ya k’arashe yana mai jaddada maganar tasa..
Alhaji Isyaku dake gefe gyaran murya yai yace “Aminu kayi hak’uri kar ka tashesu.. Ni zan baka kud’ed’en da ake binsu zan kuma biya damages d’in da Tabawa tayi ma gidan.. Mu k’arasa gidana ka amshi kud’ad’en..”
Umma baki sake take duban Alhaji Isyaku, Ta rasa wanne zatayi dan batada bakin maganar a halin yanzu.. Tana ganin Alhaji Isyaku da Aminu suka wuce Aminu yana fad’in “Wllhi ba don kai ba Alhaji saidai su bar gidan nan a yau dan na lura tsautsayi ke bin ahalin..”
Juyowan da Umma zatai taga Sadiya na tsaye bayanta hawaye na bin fuskarta.. Su duka biyun babu wanda ya iya cewa komai sai rungume juna da sukai had’i da sakin kuka mai ban tausayi..
**
Hindu ce taima Ajidde iso zuwa parlorn Aunty Nuratu. A nan suka tadda Inne harmada Aunty Shamau.
Ajidde ta risina ta gaishesu sai kalle kallen kayan alatu take wanda aka k’awata d’akin dasu. Tab lallai da ace zata iya kwashe wannan kaya takaima Kyallu da ta gama saye zuciyar Kyallu da imaninta..
Yanda take kalle kalle tana d’aga kai yasa Shemau zuba mata idanu fuska a yatsine “Ke.!! kiyi abinda ya kawoki ki tafi kin tsaya sai faman kalle kalle kike..”
Tsawan da Shemau ta daka mata saida ya sanyata zabura Ta k’ame waje guda.
Inna kaw a hasale Ta katse Shemau da fad’in “Haba Shemau ki bita a hankali mana.. Meye abun fad’a a nan inyi. Baki ganin yarinya ce..”
Shemau Ta d’an sassauta murya tace “Inne babu wani yarinta muguwar k’auyanci ne kawai..”
“K’auyanci.? Ked’in yaushe ne kika waye..! Koda wasa ni Kinsan bana d’aukan wulak’anta d’an Adam.. Ki k’yale yarinya tayi aikinta a natse, Zo ki fice ma bansan zaman mai kike a nan ba..”
Shemau ta d’an b’ata fuska ta fice ranta baiso ba Inne naci gaba da sababi..
Ajidde taima Shemau gwalo cikeda jin dad’in bayanta da Inne tabi...
Mamaki ya cika Shemau dan taga sanda Ajidde ta mata gwalo harda kashe mata ido guda.. A ranta tace lallai wannan yarinya sai ta gyara mata zama.
Tana ficewa Ajidde ta saci kallon Inne saidai itama Inne ita take duba murmushi saman fuskarta.
“Taho muje.” Inne tace sanda ta mik’e ta nufi k’ofar d’akin da Aunty Nuratu ke kwance.
Ajidde tabi bayanta rungume da jakar maganinta still sai kalle kalle take tana k’are ma gidan kallo.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*16*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Suna ficewa daga lungun Alhaji Isyaku ya mik’a ma Aminu hannu saka tafa yana sakin muguwar dariya.
“Kai Aminu naji dad’in yanda ka masu barazana, na tabbata yanzu basuda yanda zasuyi face su amince dani.”
Aminu ya dafe kud’ad’ensa yana k’irgasu yake fad’in “Toh kai d’in ai bana wasa bane Alhaji. Na gode K’warai. Idan kanaso na koma gobe ma zan koma na kuma masu barazana.”
Alhaji Iskyaku ya kuma aza babbar riga yana sakin dariya “Aminu Aminu.. Ai bayan abinda ya faru yanzu dole zasu amince dani dan idan ba haka ba basuda mahalli, kaga basuda sauran zab’in da ya wuce su amince dani.”
Suka kuma k’ek’yata dariya Aminu na kuma godiya, nan yai sallama da Alhaji Isyaku ya wuce.
**
Tinda Inne ta tura k’ofar d’akin gaban Ajidde ke yankewa, batasan mai zata gani cikin d’akin ba amma kam zuciyarta ya tsananta bugawa. Bugun zuciyarta ya k’aru sanda Ta hango matar dake kwance saman gado idanunta a lumshe. Sumarta da yake tamkar na Indians ya rufe b’angaren fuskarta. Fuskar nata yayi fayau irinta marassa lafiya. Dan koda gani ba wata fara bace can tsananin Jinya ne ya sanya fuskar nata yin fari. Saidai ga dukkan alamu tanada Yalwan suma irin mai tsananin tsantsin nan.. Ajidde taci gaba da takowa a hankali tana jin zuciyarta na wani irin fuzga tana duban matar. Kyallu tasha kwantar da majinyata a gidanta tana masu magani da rawan Bori wanda akasari mutuwa suke amma ko kusa bata tab’a karo da matar da ganinta ya mugun raunana zuciyarta irin wannan matar ba. Taci gaba da takowa zuwa gadon da matar ke kwance bisa.
Inne na hankalce da ita har ta k’araso.
Ganin ta zubawa Aunty Nuratu idanu Ta kasa janye idanunta yasa Inne gyaran murya ta soma fad’in “Shekaru goma sha biyar kenan tana kwance haka. An gwada magunguna da dama, anje k’asashe da dama amma babu wani abinda yake canzawa haka za’a hak’ura a dawo da Ita.. Mun yanke shawarin dawowa gida ko Allah zaisa a dace.”
Ajidde tasa hannu Ta share hawayen da taji na ziraro mata.
Inne ta kuma dubanta tace “Ban tambayeki ba. Ya sunanki.?”
Ajidde ta d’ago tana duban Inne “Suanana Ajidde.”
“Ajidde.” Inne ta nanata, sai kuma ta saki murmushi tace “Ina fata maganinki ya mana aiki Ajidde.. Ina fata Ubangiji yasa mu dace da maganinki.. Allah ya nufa maganin Nuratu na cikin tafin hannunki.”
Ajidde Ta d’ago manyan idanunta da suke farare k’al masu gauraye da hawaye tana duban Inne dasu. Bata iya furta komai ba Sai duk’awa da tai gaban gadon tana k’ok’arin bud’e jakan maganinta.
“Amm Hajiya ko zan d’an sami k’aramar kwano.?” Ajidde ta tambaya tana duban Inne.
Murmushi Inne Ta sakar mata Tace “Ki kirani da Inne kinji koh..”
Ajidde ta maida mata martanin murmushin tana mai jinjina kai tace “Toh Inne..”
Inne ta kuma murmusawa kafin ta bud’e murya tana kiran Hindu.
Hindu ta shigo cikeda risinawa tana fad’in “Gani Inne.”
“Kije ki kawo mata kwano k’arama.”
“Toh Inne.” Hindu ta amsa tana mai ficewa.
Ya jinjina mata kai yana bud’e ledar biscuit d’in dake d’aya hannunsa.
Umma ta Shafa kansa tace “Tashi ka shiga ciki koh ka bamu waje.”
Ya mik’e yana jinjina kai.. Yana shigewa Sadiya ta fuzge tarkacen da ya shigo dashi tai watsi dasu.
Kuka ya shigayi yana bori yana fad’in Maiyasa ta yar masa abinsa.. Ko takan kukan Ashir batabi ba ta shige d’aki zuciyarta na mata d’aci.
Umma da Alhaji Isyaku dik sunji abinda ya faru a kunnuwarsu..
Dikda jikin Alhaji Isyakun ya d’anyi sanyi bai fasa sanar da Umma buk’atarsa na son auren Sadiya ba..
Umma Ta murmusa cikeda takaici “Alhaji da ka daina wannan wahalan dan hukunci dai mun riga mun gama yankewa daga ni har Sadiya.. Kaje mun gode da niyyan taimako.”
Alhaji Isyaku yace “Baki fahimta ba Umma..”
“A’a ni dan Allah ka kirani da Uwani menene wani Umma.. Kaga Alhaji Takaba nake ba don tashin hankalin da muke ciki ba Ko barinka ka shigo gidan nan bazanyi ba.. Mun gode da kai Ashiru asibiti da kai dan Allah ina rok’onka ka tashi ka tattari kayyakinka ka tafi bamu buk’ata kuma kar ka sake dawo mana.”
Alhaji Isyaku ya murmusa kad’an yace “Umma kenan.. Barin fad’a miki kuna buk’ata na..”
Da mamaki Umma ke dubansa.
Alhaji Isyaku ya murmusa yana mai jinjina kai “ K’warai kuna buk’atana Umma.. Ya kamata ki sake tunani akan wannan al’amari.. Ki tuna makomar rayuwarku musamman yanzu da babu mahaifin yaranki.. Ki tuna halin rayuwa da zaku fuskanta.. Shin kina tunanin Sadiya zata samu miji ne bayan duk abubuwan da suka faru..? Kindai ji da kunnuwanki irin maganganun da mutanen unguwa keyi akan d’iyarki.. Kina tunanin akwai wanda zaizo ya aureta a haka..?” Ya kuma kannare idanu yana kuma duk’ar da kansa yace “Amma ni zan biya maku bashinku sannan zan auri d’iyarki na d’auketa daga garin nan, zan kaita can da nisa yanda babu wanda ya santa, gaba d’aynku ma zaku bar nan zaku koma sabon waje ku soma sabuwar rayuwa a can yanda babu tashin hankali babu komai..”
Umma da hawaye ke gangaro mata kafin takai ga furta wani kalma suka jiyo sallama daga waje.. Babu shiri Ta mik’e dan ba muryar kowa bane face Aminu dillalin da ya basu hayan gidan da suke ciki..
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un kawai Umma ke nanatawa cikin zuciyarta.. Ta d’aga idanu tana duban glasses na window da Tabawa da ‘yandabanta suka fasa..
Umma murya na rawa take fad’i da Aminu “Malam Aminu Barka da Safiya..”
“Uwani ba wannan ya kawoni ba.. Zuwa nai dan na tabbata Kun fice daga gidan nan. Bazan d’auki asara irin haka ba.. Zamanku a gidan nan babu alkhairi dama baku biya kud’in hayan bara ba ga na bana.. Sabida mutuwar mijinki yasa na d’an d’aga maku k’afa. Nayi niyyan maku mutunci na barku ku zauna har ki ida takabanki kafin na sallameku amma Tunda abun ya zama haka gaskiya zaku tattara ku fice a gidan nan dan amana Alhaji ya bani.. Tinda nake masa dillancin gidajen hayansa a unguwar nan bamu tab’a samun matsala ba.. Bazan fara akanku ba, na kula masifa da tashin hankali bibiyarku suke Dan haka kawai ku biya kud’in hayanku ku k’ara gaba tin kafin Alhaji Sadi yaji wannan batu..”
Cikin rawar murya Umma ke fad’in “Malam Aminu dan Allah kai hak’uri ka taimakemu.. Ka rufa mana asiri yanda Allah ya rufa maka.. Idan muka tashi a nan bansan Ina zamuje ba.. Dan Allah kaji tausayinmu.. Ka bari Ko Takaban ne na gama.. Inada yara Malam Aminu bansan ina zan kaisu ba idan muka tashi a nan..”
Girgiza kai Malam Aminu yai yana duban wani gefen dan karma Ta basa tausayi “A’a Uwani.. Gaskiya bazan iya ba.. Gidan nan nima amana ce a hannuna, kawai ki daina rok’ona dan bazai yuwu kuci gaba da zama a nan ba.. Maganar gaskiya kenan..!” Ya k’arashe yana mai jaddada maganar tasa..
Alhaji Isyaku dake gefe gyaran murya yai yace “Aminu kayi hak’uri kar ka tashesu.. Ni zan baka kud’ed’en da ake binsu zan kuma biya damages d’in da Tabawa tayi ma gidan.. Mu k’arasa gidana ka amshi kud’ad’en..”
Umma baki sake take duban Alhaji Isyaku, Ta rasa wanne zatayi dan batada bakin maganar a halin yanzu.. Tana ganin Alhaji Isyaku da Aminu suka wuce Aminu yana fad’in “Wllhi ba don kai ba Alhaji saidai su bar gidan nan a yau dan na lura tsautsayi ke bin ahalin..”
Juyowan da Umma zatai taga Sadiya na tsaye bayanta hawaye na bin fuskarta.. Su duka biyun babu wanda ya iya cewa komai sai rungume juna da sukai had’i da sakin kuka mai ban tausayi..
**
Hindu ce taima Ajidde iso zuwa parlorn Aunty Nuratu. A nan suka tadda Inne harmada Aunty Shamau.
Ajidde ta risina ta gaishesu sai kalle kallen kayan alatu take wanda aka k’awata d’akin dasu. Tab lallai da ace zata iya kwashe wannan kaya takaima Kyallu da ta gama saye zuciyar Kyallu da imaninta..
Yanda take kalle kalle tana d’aga kai yasa Shemau zuba mata idanu fuska a yatsine “Ke.!! kiyi abinda ya kawoki ki tafi kin tsaya sai faman kalle kalle kike..”
Tsawan da Shemau ta daka mata saida ya sanyata zabura Ta k’ame waje guda.
Inna kaw a hasale Ta katse Shemau da fad’in “Haba Shemau ki bita a hankali mana.. Meye abun fad’a a nan inyi. Baki ganin yarinya ce..”
Shemau Ta d’an sassauta murya tace “Inne babu wani yarinta muguwar k’auyanci ne kawai..”
“K’auyanci.? Ked’in yaushe ne kika waye..! Koda wasa ni Kinsan bana d’aukan wulak’anta d’an Adam.. Ki k’yale yarinya tayi aikinta a natse, Zo ki fice ma bansan zaman mai kike a nan ba..”
Shemau ta d’an b’ata fuska ta fice ranta baiso ba Inne naci gaba da sababi..
Ajidde taima Shemau gwalo cikeda jin dad’in bayanta da Inne tabi...
Mamaki ya cika Shemau dan taga sanda Ajidde ta mata gwalo harda kashe mata ido guda.. A ranta tace lallai wannan yarinya sai ta gyara mata zama.
Tana ficewa Ajidde ta saci kallon Inne saidai itama Inne ita take duba murmushi saman fuskarta.
“Taho muje.” Inne tace sanda ta mik’e ta nufi k’ofar d’akin da Aunty Nuratu ke kwance.
Ajidde tabi bayanta rungume da jakar maganinta still sai kalle kalle take tana k’are ma gidan kallo.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*16*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Suna ficewa daga lungun Alhaji Isyaku ya mik’a ma Aminu hannu saka tafa yana sakin muguwar dariya.
“Kai Aminu naji dad’in yanda ka masu barazana, na tabbata yanzu basuda yanda zasuyi face su amince dani.”
Aminu ya dafe kud’ad’ensa yana k’irgasu yake fad’in “Toh kai d’in ai bana wasa bane Alhaji. Na gode K’warai. Idan kanaso na koma gobe ma zan koma na kuma masu barazana.”
Alhaji Iskyaku ya kuma aza babbar riga yana sakin dariya “Aminu Aminu.. Ai bayan abinda ya faru yanzu dole zasu amince dani dan idan ba haka ba basuda mahalli, kaga basuda sauran zab’in da ya wuce su amince dani.”
Suka kuma k’ek’yata dariya Aminu na kuma godiya, nan yai sallama da Alhaji Isyaku ya wuce.
**
Tinda Inne ta tura k’ofar d’akin gaban Ajidde ke yankewa, batasan mai zata gani cikin d’akin ba amma kam zuciyarta ya tsananta bugawa. Bugun zuciyarta ya k’aru sanda Ta hango matar dake kwance saman gado idanunta a lumshe. Sumarta da yake tamkar na Indians ya rufe b’angaren fuskarta. Fuskar nata yayi fayau irinta marassa lafiya. Dan koda gani ba wata fara bace can tsananin Jinya ne ya sanya fuskar nata yin fari. Saidai ga dukkan alamu tanada Yalwan suma irin mai tsananin tsantsin nan.. Ajidde taci gaba da takowa a hankali tana jin zuciyarta na wani irin fuzga tana duban matar. Kyallu tasha kwantar da majinyata a gidanta tana masu magani da rawan Bori wanda akasari mutuwa suke amma ko kusa bata tab’a karo da matar da ganinta ya mugun raunana zuciyarta irin wannan matar ba. Taci gaba da takowa zuwa gadon da matar ke kwance bisa.
Inne na hankalce da ita har ta k’araso.
Ganin ta zubawa Aunty Nuratu idanu Ta kasa janye idanunta yasa Inne gyaran murya ta soma fad’in “Shekaru goma sha biyar kenan tana kwance haka. An gwada magunguna da dama, anje k’asashe da dama amma babu wani abinda yake canzawa haka za’a hak’ura a dawo da Ita.. Mun yanke shawarin dawowa gida ko Allah zaisa a dace.”
Ajidde tasa hannu Ta share hawayen da taji na ziraro mata.
Inne ta kuma dubanta tace “Ban tambayeki ba. Ya sunanki.?”
Ajidde ta d’ago tana duban Inne “Suanana Ajidde.”
“Ajidde.” Inne ta nanata, sai kuma ta saki murmushi tace “Ina fata maganinki ya mana aiki Ajidde.. Ina fata Ubangiji yasa mu dace da maganinki.. Allah ya nufa maganin Nuratu na cikin tafin hannunki.”
Ajidde Ta d’ago manyan idanunta da suke farare k’al masu gauraye da hawaye tana duban Inne dasu. Bata iya furta komai ba Sai duk’awa da tai gaban gadon tana k’ok’arin bud’e jakan maganinta.
“Amm Hajiya ko zan d’an sami k’aramar kwano.?” Ajidde ta tambaya tana duban Inne.
Murmushi Inne Ta sakar mata Tace “Ki kirani da Inne kinji koh..”
Ajidde ta maida mata martanin murmushin tana mai jinjina kai tace “Toh Inne..”
Inne ta kuma murmusawa kafin ta bud’e murya tana kiran Hindu.
Hindu ta shigo cikeda risinawa tana fad’in “Gani Inne.”
“Kije ki kawo mata kwano k’arama.”
“Toh Inne.” Hindu ta amsa tana mai ficewa.