Sashe 91
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta dara kad’an kafin tace “Now you are talking detective..” Gyara tsayuwarta tai kafin ta soma fad’in “I know you don’t want this videos and pictures to go viral on social media.. Na tabbata bazakaso sunanka ya b’aci ba.. Na tabbata bazaka so ka rasa aikinka da ahalinka ba.. Harma da d’iyarka wacce take hannun matarka da kaketa fafutukan k’watota daga hannun matar taka a kotu.. Assad idan Kotu sukaga pictures da videos d’in nan Alk’ali bazai baka rik’on d’iyarka ba kaman yanda kake so.. Wait Idan ban mance ba kace mahaifiyarta Wato tsohuwar matarka batada kamun kai batada tarbiya hasalima ka kamata da kwarto ne shiyasa kuka rabu.. Kana son amso d’iyarka daga hannunta sabida zata lalata maka d’iya shiyasa kake so Kotu ta karb’ar maka rik’on d’iyarka ya dawo hannun mahaifiyarka.. Toh ina mai tabbatar maka idan Kotu sukaga wann shaida kaida d’iyarka har abada.. Sannan ita kanta mahaifiyarka zata gujeka.. Kai k’arshe ni kaina zan k’ulla maka sharrin da bazaka iya fidda kanka ba.. Dama NPF kam ka saka ma ranka an koreka an gama bayan tuggun da zan k’ulla maka.. Kai bama kora kad’ai ba zaka k’are a kurkuku..!”
Duban Maleeka kurum yake yana mamakin Ta yaya mutum zai zama mugu irin haka.. Mai ya mata da tsanani da zata shirya masa irin wann gadar zare..
Girgiza kai ya soma yana fad’in “Maleeka why.. Mai na miki..?!” Yai maganar cikin rawar murya yana nuni da k’irjinsa.
Maleeka ta tsefe idanu tana dubansa “Baka mun komai ba Assad.. Laifinka d’aya shine zama aminin Mu’azzam da kai.. Dole ce ta saka ni na aikata maka haka..”
Ya girgiza kai hawaye na gangarowa daga idanunsa guda “Maleeka don’t do this please.. Na rok’eki.. Kar ki aikata mun haka.. Ki dubi girman Allah ki dubi girman sharrin da kike k’ok’arin k’ulla ma ran da bata San hawa ba batasan sauk’a ba.. Kar ki cutar da ran da baki da iko akanta..!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya.
Maleeka ta murmusa kafin tace “Babu kalaman da zakayi amfani dasu wad’anda zasu sa na fasa k’udirina Assad.. Babu gudu babu jada baya.. Wanna shine kad’ai hanyar da zan wanke kaina daga zargin da abokinka yake mun.. Ka saka ma ranka kalan taka k’addaran kenan..!”
Ya girgiza kai yace “Ban fahimceki ba.. Mai hakan yake nufi.. Mai kike so nayi..?”
Ta murmusa kafin tace “Inspector Gamji your best friend, your only confidant.. Ya bani Assignment cewa na nemo masa wanda yake masa zagon k’asa a CID.. Nasan kanada masaniya akan binciken da yake gameda B.A.T. Ta yuwu ma tare kukeyi tinda yanzu aikin team d’inma kuna classifying nashi.. Dan haka Ina so ka amsa laifin cewa kai kake wa Mu’azzam zagon k’asa.. Ya bani sati biyu kafin ya dawo daga tafiyar da yai na kawo masa wanene B.A.T... A cewarsa B.A.T shine Spy d’in Danger a cikin CID.. Zaka amsa laifin cewa kai kake aiki da Danger sann duk tsawon lokacin nan kai ne kake masa zagon k’asa.. Wato dai zaka amsa cewa kai ne B.A.T..”
Lumshe idanunsa Assad yai hawaye masu zafi suka gangaro masa.
“Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!” Abinda harshensa ya iya furtawa kenan.. Fatan bakinsa suka bud’e da k’yar..
Muryarta ya kuma sinkayo tana fad’in “Zab’i ya rage Naka Assad.. Kodai ka amsa laifin ka rufawa Kanka da mutuncinka asiri ka tsare mutuncin ahalinka, harma da d’iyarka da mahaifiyarka.. Ko kuma kak’i amsa laifin na yad’a wad’ann hotuna a kafafen sada zumunta mutuncinka ya zube.. Sannan ka rasa Farin cikinka Wato d’iyarka... Sannan ka shafawa zuri’arka harma da d’iyarka bak’in fenti wanda bazai tab’a gogewa ba a tarihin rayuwa..”
Daga haka Sa kai tai zata wuce.. Har Ta kai k’ofa ta dawo da baya ta aje masa wayarsa saman kujera, kafin Ta dubesa yanda yai zaune ya k’ura ma waje guda idanu, hab’arsa d’aure saman hannayensa biyu.
Maleeka tace “You have 2 good weeks to decide Detective.. Kodai ka zab’i kasancewa da Abokinka ka rasa mutuncinka da d’iyarka harma da ahalinka.. Ko kuma kai confessing wa Mu’azzam cewa kai ne ke masa zagon k’asa ka tsira da mutuncinka.. Zab’i ya rage naka..!” Tana ida fad’in haka tasa kai zata Shige.
Kukan kura Assad yai ya fuzgo wayarta yana k’ok’arin goge hotunan.
Dariya ta fashe dashi kafin tace “Kayi a banza.. Kana abu kaman kana mance cewa inada tunani irin naka.. Profession d’aya ke garemu.. Assad nayi saving d’insu a multiple files inada su a wajaje daban daban.. Zab’i ya rage Naka... Kar ka mance kana da lokaci kafin Mu’azzam ya dawo..!” Tana ida fad’in haka ta funciki wayarta kafin ta fice zuciyarta Wasai..
Tana ficewa ta kirawo wayan Chief tana sanar dashi yanda abu ya kasance.
Chief ya murmusa Cikeda k’asaita “Na fad’a miki.. Ni nasan bazaki bamu kunya ba. Yanzu bamuda sauran damuwa akan Inspector Gamji da Assad.. Shikenan mun tarwatsa abotansu.. Ina mai tabbatar miki yanzu Mu’azzam zai zamto baida tudun dafawa a CID tinda amininsa mafi kusanci dashi zai tafi gidan Kaso... Daga wann lokaci case d’in zai fice daga Zuciyar Mu’azzam idan har abokinsa mafi kusanci dashi zai zamto suspect na gaba.. Kinga cikin Sauk’i za’a k’arasa wanann jarabben case da ya tsaya mana a mak’oshi ya mana banga banga..” Ya kuma murmusawa yana fad’in “Good job Officer.. Kinsan aikinki.. Dole BAT ya baki kyauta na musamman bisa jajircewa da kikai..”
Ta murmusa kad’an kafin tace “Na gode da yabo Sir.. Amma Sir Ina son sanin wanene asalin BAT.. Shin menene had’insa da case din nan..?”
Murmusawa Chief yai kafin yace “Zai fi miki idan kika tsaya a nan ba tareda Kin kuma kutsawa ciki ba..”
Maleeka ta d’an girgiza kai kad’an kafin tace “Har yanzu baku gama yarda dani bane.. Chief ina son sanin Wanene BAT.. Ina son sanin ma wa nake aiki..?”
Chief ya murmusa kafin yace “Har yanzu dai zan k’ara shawartanki kar ki nemi sanin wanene Jemage domin kuwa bakinksa baya banbance abu mai kyau da najasa, komai ta baki yake. harta najasa ta baki yake fitarwa.. Jemage baida gaba sai baya..!” Ya k’arashe cikin tsoratarwa.
Maleeka ta d’anyi jim kafin tace “Chief kana nufin BAT wai Jemage kake nufi ba abbreviation na sunan wani bane..?”
Murmusawa Chief yai kafin yace “You love asking crucial questions Maleeka and you never give up akan bincike.. Ked’in material ce Babba.. Zakiyi amfani ma CID sosai da ace zaki zamto mutumiyar k’warai...” Daga haka katse kiran yai ya barta tana tinani.. Ta fuzar da fuci kad’an tana nanata kalmar Jemage.
**
FUFORE..
Su Inne dasu Aunty Shemau gaba d’aya suka fito tarbansu, duk wanda ke cikin gidan ma saida Inne ta sanyasa fitowa domin a tarbi kishiyarta amaryar Mu’azzam d’inta.
Ajidde ce kawai bata a wajen amma har su Mama Hindu duk sun fito.
Gaban Sadiya Sai fad’uwa yake sanda suka soma fitowa daga motar. Ita da Mu’azzam ne a baya sai ko Musaddiq da driver a gaba.
Tana fitowa ta hango Dattijuwar sai sakin murmushi take idanunta tarau akanta sauran mutanen na lale lale.
A hankali Sadiya ta sadda idanunta k’asa sanda taji hannun Mu’azzam saman nata. Tai k’ok’arin zame hannunta amma yak’i saki.. Ta d’an d’ago idanunta ta dubesa kaman mai shirin kuka alamun ya sakar mata hannu.. Bai sakar matan ba sai ma d’auke kansa da yai alamun ta daina b’atawa kanta lokaci dan bazai cire hannunta cikin nasa ba.
Babu yanda ta iya ta maida kanta k’asa.
Musaddiq ya tafi da sauri ya rungume Dattijuwan yana fad’in yayi kewarta wanda Sadiya keda tabbacin cewa itace Inne.
Inne ta d’an dunguri k’eyarsa tana fad’in “Toh maza kayar dani sai kaji dad’i.. Fitananne..”
Musaddiq ya d’an shafi kansa yace “Haba mana Inne tarban da zaki min kenan..”
Ta tsaresa da idanu tana karantar k’wayan idanunsa ko da ya tafi Abuja ya koma shan wasu abubuwan.. “Shige ka jirani zanzo na bincike ka..” Ta fad’i tana turasa kad’an.
Daidai lokacin Mu’azzam da Sadiya suka k’araso.. Mu’azzam ya bawa Inne light hug yana fad’in “Nayi kewarki Inne na..” Murmushi itama tai kafin ta d’an turasa tana fad’in “Ka dank’aro mun kishiyoyi dole kace haka.. Bani waje na fara gaisawa da kishiyan tawa kafin kai.” Ta k’arashe tana mai nufo Sadiya.
Sadiya tai saurin duk’awa da niyyan gaida Inne.. Saidai Inne bata bari ta isa k’asa ba ta kamota tana fad’in “A’a na yafeki.. Tashi abinki ni k’awarki ce ba kishiya ba..” Tai maganar tana mai rungumar Sadiyar.
Ita kaw Sadiya daketa sakin murmushi sanne kanta tai da mayafinta jikin Inne dan kunya..
A haka Inne na rik’eda Ita suka nufi cikin gidan.
Shemau ta rakasu da idanu kafin ta jinjina kai tace a cikin zuciyarta. Tirk’ashi Lallai Safeenah kinada jan aiki.. Lokaci guda ta soma dialing layin Mommy tana mai barin wajen.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*47*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A d’akin Inne aka soma mata masauk’i a cewar Inne sai Washe gari su kaita b’angarenta suyi mata rakiya kaman yanda akeyi a al’ada. Ba haka Mu’azzam yaso ba, saidai babu yanda ya iya tinda haka Inne tace. Tai wanka nan band’akin Inne Ta kuma sauya shiga cikin tufafi masu sauk’i.. Sai nan da Ita Inne take, gaba d’aya Sadiya ta gaza sakewa Dikda cewa da Innen take ta saki jikinta gida take.
Mama Hindu ce ta shimfid’a mata abin sallah sanda ta ida shirin nata.. Nan Mama Hindu Ta nuna mata gabas, itama sai nan nan da ita take.
Sadiya tai mata godiya cikeda risinawa kafin ta tada sallar isha.
Ruwan sama na kuma b’arkewa kaman da bakin k’warya.
Mama Hindu ta fito ta nufi d’akin Aunty Nuratu tana fad’in yau Ajidde batai mata sallama ba ta tafi..
Kicib’is sukai da Ajidde ta fito daga waje ruwa ya jik’ata shakaf rungume da gwaiba cikin hijabinta.
Mama Hindu ta saki baki tana duban Ajidde da tsananin mamaki “Ke Ajidde Wai dama baki tafi gida ba.. Toh ina kika tsaya..? Jibi yanda ruwa ya miki lilis..” Tai shiru tana duban Ajidde dake rawan d’ari.. Sai kuma ta girgiza kai tana duban ‘ya’yan gwaiba data jido.
Mama Hindu Ta girgiza kai tace “Yanzu tsayawa tsinkar gwaiba kikayi a ruwan nan ga duhun dare Ajidde.. Kar dai ma bishiya kika d’ale a daren nan..?”
Duban Maleeka kurum yake yana mamakin Ta yaya mutum zai zama mugu irin haka.. Mai ya mata da tsanani da zata shirya masa irin wann gadar zare..
Girgiza kai ya soma yana fad’in “Maleeka why.. Mai na miki..?!” Yai maganar cikin rawar murya yana nuni da k’irjinsa.
Maleeka ta tsefe idanu tana dubansa “Baka mun komai ba Assad.. Laifinka d’aya shine zama aminin Mu’azzam da kai.. Dole ce ta saka ni na aikata maka haka..”
Ya girgiza kai hawaye na gangarowa daga idanunsa guda “Maleeka don’t do this please.. Na rok’eki.. Kar ki aikata mun haka.. Ki dubi girman Allah ki dubi girman sharrin da kike k’ok’arin k’ulla ma ran da bata San hawa ba batasan sauk’a ba.. Kar ki cutar da ran da baki da iko akanta..!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya.
Maleeka ta murmusa kafin tace “Babu kalaman da zakayi amfani dasu wad’anda zasu sa na fasa k’udirina Assad.. Babu gudu babu jada baya.. Wanna shine kad’ai hanyar da zan wanke kaina daga zargin da abokinka yake mun.. Ka saka ma ranka kalan taka k’addaran kenan..!”
Ya girgiza kai yace “Ban fahimceki ba.. Mai hakan yake nufi.. Mai kike so nayi..?”
Ta murmusa kafin tace “Inspector Gamji your best friend, your only confidant.. Ya bani Assignment cewa na nemo masa wanda yake masa zagon k’asa a CID.. Nasan kanada masaniya akan binciken da yake gameda B.A.T. Ta yuwu ma tare kukeyi tinda yanzu aikin team d’inma kuna classifying nashi.. Dan haka Ina so ka amsa laifin cewa kai kake wa Mu’azzam zagon k’asa.. Ya bani sati biyu kafin ya dawo daga tafiyar da yai na kawo masa wanene B.A.T... A cewarsa B.A.T shine Spy d’in Danger a cikin CID.. Zaka amsa laifin cewa kai kake aiki da Danger sann duk tsawon lokacin nan kai ne kake masa zagon k’asa.. Wato dai zaka amsa cewa kai ne B.A.T..”
Lumshe idanunsa Assad yai hawaye masu zafi suka gangaro masa.
“Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..!” Abinda harshensa ya iya furtawa kenan.. Fatan bakinsa suka bud’e da k’yar..
Muryarta ya kuma sinkayo tana fad’in “Zab’i ya rage Naka Assad.. Kodai ka amsa laifin ka rufawa Kanka da mutuncinka asiri ka tsare mutuncin ahalinka, harma da d’iyarka da mahaifiyarka.. Ko kuma kak’i amsa laifin na yad’a wad’ann hotuna a kafafen sada zumunta mutuncinka ya zube.. Sannan ka rasa Farin cikinka Wato d’iyarka... Sannan ka shafawa zuri’arka harma da d’iyarka bak’in fenti wanda bazai tab’a gogewa ba a tarihin rayuwa..”
Daga haka Sa kai tai zata wuce.. Har Ta kai k’ofa ta dawo da baya ta aje masa wayarsa saman kujera, kafin Ta dubesa yanda yai zaune ya k’ura ma waje guda idanu, hab’arsa d’aure saman hannayensa biyu.
Maleeka tace “You have 2 good weeks to decide Detective.. Kodai ka zab’i kasancewa da Abokinka ka rasa mutuncinka da d’iyarka harma da ahalinka.. Ko kuma kai confessing wa Mu’azzam cewa kai ne ke masa zagon k’asa ka tsira da mutuncinka.. Zab’i ya rage naka..!” Tana ida fad’in haka tasa kai zata Shige.
Kukan kura Assad yai ya fuzgo wayarta yana k’ok’arin goge hotunan.
Dariya ta fashe dashi kafin tace “Kayi a banza.. Kana abu kaman kana mance cewa inada tunani irin naka.. Profession d’aya ke garemu.. Assad nayi saving d’insu a multiple files inada su a wajaje daban daban.. Zab’i ya rage Naka... Kar ka mance kana da lokaci kafin Mu’azzam ya dawo..!” Tana ida fad’in haka ta funciki wayarta kafin ta fice zuciyarta Wasai..
Tana ficewa ta kirawo wayan Chief tana sanar dashi yanda abu ya kasance.
Chief ya murmusa Cikeda k’asaita “Na fad’a miki.. Ni nasan bazaki bamu kunya ba. Yanzu bamuda sauran damuwa akan Inspector Gamji da Assad.. Shikenan mun tarwatsa abotansu.. Ina mai tabbatar miki yanzu Mu’azzam zai zamto baida tudun dafawa a CID tinda amininsa mafi kusanci dashi zai tafi gidan Kaso... Daga wann lokaci case d’in zai fice daga Zuciyar Mu’azzam idan har abokinsa mafi kusanci dashi zai zamto suspect na gaba.. Kinga cikin Sauk’i za’a k’arasa wanann jarabben case da ya tsaya mana a mak’oshi ya mana banga banga..” Ya kuma murmusawa yana fad’in “Good job Officer.. Kinsan aikinki.. Dole BAT ya baki kyauta na musamman bisa jajircewa da kikai..”
Ta murmusa kad’an kafin tace “Na gode da yabo Sir.. Amma Sir Ina son sanin wanene asalin BAT.. Shin menene had’insa da case din nan..?”
Murmusawa Chief yai kafin yace “Zai fi miki idan kika tsaya a nan ba tareda Kin kuma kutsawa ciki ba..”
Maleeka ta d’an girgiza kai kad’an kafin tace “Har yanzu baku gama yarda dani bane.. Chief ina son sanin Wanene BAT.. Ina son sanin ma wa nake aiki..?”
Chief ya murmusa kafin yace “Har yanzu dai zan k’ara shawartanki kar ki nemi sanin wanene Jemage domin kuwa bakinksa baya banbance abu mai kyau da najasa, komai ta baki yake. harta najasa ta baki yake fitarwa.. Jemage baida gaba sai baya..!” Ya k’arashe cikin tsoratarwa.
Maleeka ta d’anyi jim kafin tace “Chief kana nufin BAT wai Jemage kake nufi ba abbreviation na sunan wani bane..?”
Murmusawa Chief yai kafin yace “You love asking crucial questions Maleeka and you never give up akan bincike.. Ked’in material ce Babba.. Zakiyi amfani ma CID sosai da ace zaki zamto mutumiyar k’warai...” Daga haka katse kiran yai ya barta tana tinani.. Ta fuzar da fuci kad’an tana nanata kalmar Jemage.
**
FUFORE..
Su Inne dasu Aunty Shemau gaba d’aya suka fito tarbansu, duk wanda ke cikin gidan ma saida Inne ta sanyasa fitowa domin a tarbi kishiyarta amaryar Mu’azzam d’inta.
Ajidde ce kawai bata a wajen amma har su Mama Hindu duk sun fito.
Gaban Sadiya Sai fad’uwa yake sanda suka soma fitowa daga motar. Ita da Mu’azzam ne a baya sai ko Musaddiq da driver a gaba.
Tana fitowa ta hango Dattijuwar sai sakin murmushi take idanunta tarau akanta sauran mutanen na lale lale.
A hankali Sadiya ta sadda idanunta k’asa sanda taji hannun Mu’azzam saman nata. Tai k’ok’arin zame hannunta amma yak’i saki.. Ta d’an d’ago idanunta ta dubesa kaman mai shirin kuka alamun ya sakar mata hannu.. Bai sakar matan ba sai ma d’auke kansa da yai alamun ta daina b’atawa kanta lokaci dan bazai cire hannunta cikin nasa ba.
Babu yanda ta iya ta maida kanta k’asa.
Musaddiq ya tafi da sauri ya rungume Dattijuwan yana fad’in yayi kewarta wanda Sadiya keda tabbacin cewa itace Inne.
Inne ta d’an dunguri k’eyarsa tana fad’in “Toh maza kayar dani sai kaji dad’i.. Fitananne..”
Musaddiq ya d’an shafi kansa yace “Haba mana Inne tarban da zaki min kenan..”
Ta tsaresa da idanu tana karantar k’wayan idanunsa ko da ya tafi Abuja ya koma shan wasu abubuwan.. “Shige ka jirani zanzo na bincike ka..” Ta fad’i tana turasa kad’an.
Daidai lokacin Mu’azzam da Sadiya suka k’araso.. Mu’azzam ya bawa Inne light hug yana fad’in “Nayi kewarki Inne na..” Murmushi itama tai kafin ta d’an turasa tana fad’in “Ka dank’aro mun kishiyoyi dole kace haka.. Bani waje na fara gaisawa da kishiyan tawa kafin kai.” Ta k’arashe tana mai nufo Sadiya.
Sadiya tai saurin duk’awa da niyyan gaida Inne.. Saidai Inne bata bari ta isa k’asa ba ta kamota tana fad’in “A’a na yafeki.. Tashi abinki ni k’awarki ce ba kishiya ba..” Tai maganar tana mai rungumar Sadiyar.
Ita kaw Sadiya daketa sakin murmushi sanne kanta tai da mayafinta jikin Inne dan kunya..
A haka Inne na rik’eda Ita suka nufi cikin gidan.
Shemau ta rakasu da idanu kafin ta jinjina kai tace a cikin zuciyarta. Tirk’ashi Lallai Safeenah kinada jan aiki.. Lokaci guda ta soma dialing layin Mommy tana mai barin wajen.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*47*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A d’akin Inne aka soma mata masauk’i a cewar Inne sai Washe gari su kaita b’angarenta suyi mata rakiya kaman yanda akeyi a al’ada. Ba haka Mu’azzam yaso ba, saidai babu yanda ya iya tinda haka Inne tace. Tai wanka nan band’akin Inne Ta kuma sauya shiga cikin tufafi masu sauk’i.. Sai nan da Ita Inne take, gaba d’aya Sadiya ta gaza sakewa Dikda cewa da Innen take ta saki jikinta gida take.
Mama Hindu ce ta shimfid’a mata abin sallah sanda ta ida shirin nata.. Nan Mama Hindu Ta nuna mata gabas, itama sai nan nan da ita take.
Sadiya tai mata godiya cikeda risinawa kafin ta tada sallar isha.
Ruwan sama na kuma b’arkewa kaman da bakin k’warya.
Mama Hindu ta fito ta nufi d’akin Aunty Nuratu tana fad’in yau Ajidde batai mata sallama ba ta tafi..
Kicib’is sukai da Ajidde ta fito daga waje ruwa ya jik’ata shakaf rungume da gwaiba cikin hijabinta.
Mama Hindu ta saki baki tana duban Ajidde da tsananin mamaki “Ke Ajidde Wai dama baki tafi gida ba.. Toh ina kika tsaya..? Jibi yanda ruwa ya miki lilis..” Tai shiru tana duban Ajidde dake rawan d’ari.. Sai kuma ta girgiza kai tana duban ‘ya’yan gwaiba data jido.
Mama Hindu Ta girgiza kai tace “Yanzu tsayawa tsinkar gwaiba kikayi a ruwan nan ga duhun dare Ajidde.. Kar dai ma bishiya kika d’ale a daren nan..?”