Sashe 63
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Assad ya shigo Coffee shop d’in yana mamakin kiran da Mu’azzam d’in yai masa yace Su had’u nan da sassafe irin haka.
Assad ya k’araso sukai musabaha still mamaki saman fuskarsa. Mu’azzam ya tambayesa abinda za’a kawo masa. Nan yace a kawo masa coffee d’in shima. Yai zaune yana duban Mu’azzam d’in yana jira yaji da mai zai fara. Bayan an kawo wa Assad nasa order d’in ya sinkayo muryar Mu’azzam na fad’in “Nasan ka tab’a aure zama baiyi dad’i ba Kun rabu da matar..”
Assad ya dubesa da mamaki jin yau kuma da wannan batun yazo, shi ya zaci ma wani ci gaba suka kuma samu daga binkicen da suke.
Assad ya jinjina kai yace “Haka ne.”
Mu’azzam ya kuma sipping hot coffee d’insa kafin yace “Kanada experience, kasan halittan mata kenan.”
Yanzu kam aje cup d’in dake hannunsa Assad yai yana duban abokin nasa da tsananin mamaki wanda a baya sam bai irin wad’ann zantukan.
Mu’azzam yaci gaba da fad’in “Inaso na maka tambaya a matsayinka na wanda yakeda experience.”
Assad ya jinjina kai yace “Umhum ina saurarenka.
“Idan mace ta gama yawonta da biye biyen maza, after some time ta jima batabi mazan ba tana koma sabuwa ce kaman dai budurwar da bata tab’a sanin wani d’a namiji ba.?”
Bagatatan Assad yaji zancen wanda har saida ya kusan fuzar da coffe d’in da ya shiga bakinsa sabida dariyan da yazo masa.. Da alama abokinsa ya shiga missed call.. Ya k’unshe bakinsa yana darawa a hankali dan Yanzu kam ya gama gane Ina tambayoyin Abokin nasa suka nufa.
Mu’azzam ya aika masa mugun kallo cikeda takaici “You are not serious, you know. Ya ina tambayarka abu kana wani dariya..”
“Toh kuka kake so nayi.. Abun ne abun dariya.. Budurci guda d’aya ne ai.. Halitta ne da Ubangiji ya Karrama ko wace d’iya mace dashi, wacce ta watsar da wannan karamci nata tin a titi bazata kuma samunsa ba, bazai dawo ba duk gyaran da za’ayi kuwa.. Bazata tab’a zama kaman wacce ta Martaba wannan karamci nata ta rik’esa da kyau ba.”
Mu’azzam ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali yana mai sipping coffee. Lokaci guda Assad yaci gaba da fad’in “Shiyasa shaidar zina dai takeda matakai daki daki..Ku guje ma mummunan zato ma bayin Allah.. So tari wanda ka munana masa zato shine na k’warai d’in. Sannan so tari wanda ka kyautata masa zato shine na banzan. Amma ko yaushe ana so mutum ya kasance mai kyautata zato.. Ku guje ma d’aukan maganganun mutane domin shi d’anadam a Kullum aibunka yake nema ya yad’a, Sai ya yad’a aibunka sau d’ari kafin ya fad’i alkhairinka guda d’aya.. Ga aibun a tattare da shi amma shi bazaiga nashi ba sai yaje yana hangen na wani.. Allah yasa mu gane ya kuma datar damu.”
Mu’azzam ya amsa da Ameen. Yana mai ci gaba da shan coffee d’insa. Time ya duba yaga Wai har tara na safe Ta d’an gauta ya kamata Su k’arasa Office.. A tare Suka mik’e Mu’azzam yai settling bill d’insu kafin suka nufo waje.
Babu b’ata lokaci suka nufo ofishinsu.
Suna isowa suka tadda Daddy a k’ofan Ofishin nasu. Assad ya dubi Mu’azzam “Wa nake gani kaman Daddy..? Allah sarki ni wllhi duk yafi bani tausayi a al’amarin nan.. Mutumin nan yana k’aunarka Mu’azzam, kaga yanda ya juya ma d’iyarsa baya yak’i ya bama k’arya goyon baya dukda cewa yanada halinda zai iya sakawa a kashe case d’in nan a rufe case d’in gaba d’aya sabida d’iyarsa amma baiyi haka ba.. Gaskiya na jima banga mutum mai dattako da kiman Daddy ba.”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “K’warai Daddy mutumin kirki ne.. Bai cancanci d’iya irin Safeenah ba.. Unfortunately bamu zab’en ahali, farkawa muke kawai mu ganmu tareda mutanen da Allah ya hukunta zasu zama ahalinmu.. Sannan ko wanne ahali sunada nasu k’alubalen da suke fuskanta.. Mu kuma irin namu k’alubalen kenan.. Mu k’arasa..”
Assad ya jinjina kai kafin suka nufo yanda Daddy ke zaune. Gaisawa sukai gaba d’aya kafin Assad ya Shige ya basu waje.
Daddy ya dubi Mu’azzam wanda jinkinsa ya d’anyi sanyi da ganin Daddyn.. Ko Babu komai Safeenah d’iyar Daddy ce jininsa ce dole zaiji wani abu can k’asan zuciyarsa dukda kuwa k’arfin halin da yai.
Mu’azzam yace “Are you here to see Safeenah.? Mu k’arasa sai a kira maka ita..”
Daddy ya girgiza kai yace “Ba Safeenah nazo gani ba Mu’azzam.. Kai nazo gani..”
Mu’azzam ya d’an gyara zamansa yana duban Daddyn.
Daddy yaci gaba da fad’in “Mu’azzam bazan hanaka hukunta Safeenah akan laifinta ba idan har an kamata da laifin.. Amma inada wata alfarma guda d’aya da nake son rok’a daga gareka.”
Mu’azzam ya d’an d’ago ya dubesa “Alfarma kuma Daddy.. Ai ka wuce alfarma a wajena Daddy.. Umarni kawai zaka bani..”
Daddy ya murmusa cikeda jin dad’i kafin ya jinjina kai yace “Allah ya maka albarka Mu’azzam.. Alfarmar da nake nema wajenka shine, dan Allah kar ka saki Safeenah har sai an gama bincike an sameta da laifi.. Kamin wannan alk’awarin cewa bazaka rabu da ita ba har sai an tabbata Tanada laifi.. This is the least I can do for my daughter bayan juya mata baya da nayi..” Ya k’arashe yana duban Mu’azzam d’in cikeda kulawa.
Cak Mu’azzam ya tsaya ba tareda ya iya amsa Daddy ba, saima sadda idanunsa k’asa da yai.
Daddy yai gyaran murya yaci gaba da fad’in “I know it’s not easy, ace kana shari’a da matarka.. But please do this for me.. For our family Mu’azzam.. Kar ka saki Safeenah until she’s proven guilty.. Ina rok’onka ne a matsayin mahaifin Safeenah.. Please Mu’azzam..!”
Ganin Daddy na k’ok’arin had’e hannayensa biyu waje guda alamun rok’o yasa Mu’azzam saurin kamo hannayen Daddy ya hanasa aikata hakan. Yana girgiza kai yake fad’in “Dani da Safeenah Kai Babanmu ne gaba d’aya Daddy.. Yanda zaka umarce Safeenah tai abu ko Musaddiq haka nima zaka mun.. Daddy bazan saketa ba kaman yanda kace.. Safeenah zataci gaba da zama matsayin matata..”
Daddy ya sakar masa murmushi yana k’ok’arin maida k’wallan dake k’ok’arin ciko idanunsa “Na gode Mu’azzam.. Thank you for this.. Allah Ubangiji ya maka albarka ya kuma maka jagora.”
Mu’azzam ya amsa da “Ameen Daddy..”
Daddy ya mik’e yace “Alk’ali ya sanar da Court Hearing d’in ne..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Muna sauraro tukuna Daddy.”
Daddy ya jinjina kai kafin yace “Ni zan wuce Company.. Sai na ganka a gida..”
Mu’azzam ya jinjina kai yana mai rakiyawa Daddyn har zuwa yanda motarsa ke ajiye driver na jira. Suka kuma yin sallama kafin Mu’azzam ya dawo cikin ofishin nasu.
Yana shigowa Assad ya K’araso yana fad’in “Barr Ameer Dikko, Safeenah’s lawyer is here.. Yana son ganawa da Safeenah..”
Sunan Ameer da Assad ya fad’i in full shine yai ringing a k’wak’walwar Mu’azzam. Barr Ameer Dikko.
Duban Assad yai kafin ya kuma duba Barr Ameer dake nufosu cikin takunsa na k’asaita.
Ya k’araso yana gaisar da Mu’azzam cikeda izgilanci irin yanda ya saba. Mu’azzam bai ce masa komai ba Sai aiaka masa muguwar kallo da yake yana nanata sunansa cikin zuciyarsa.
Assad ne yai masu jagoranci gaba d’aya zuwa interrogation yanda Safeenah ke zaune tana jira. A d’an Kwana guda da tai cikin Cell har kamanninta ya canza abinka da wacce bata saba da wahala ba. Farin fatar ta dik yayi wani irin jajaja alamun wahala da rashin sabo.
Ameer ne ya soma shiga suka gana kafin daga bisani Mu’azzam ya shigo. Safeenah na ganinsa ta fashe da kuka tana fad’in “My Halal I can’t believe you are doing this to me.. Please ka k’yaleni na tafi gida.. This place is hell..”
Ameer kaw takaici ya cikasa ganin yanda Safeenah ke shagwab’awa Mu’azzam tana wani kiransa her Halal.
Zama yai gefe yana mai aikawa Ameer mugun kallo. Bai amsa Safeenah ba still idanunsa na kan Ameer yake furta “Barrister Ameer Dikko is your enemy.!”
“Barr Ameer Dikko is ruining your home.!”
“Barr Ameer Dikko is very BAD”
“Barr Ameer Dikko you’re BAD”
Cikin rashin gane kalman nasa suke dubansa daga Ameer d’in har Safeenah.
Ameer ya girgiza kai yace “Ban fahimceka ba Inspector..?”
Murmushi Mu’azzam yai kafin yace “Ba Lallai ka fahimta ba amma Iyakacin abinda na sani YOU ARE BAD..”
Ameer ya kuma dubansa kai a k’ulle, lokaci guda Mu’azzam ya ciro wayarsa cikin aljihu yana nunawa Ameer sak’onnin BAD da akaita turo masa kwanakin baya. Ameer ya dubi sak’onnin da tsananin mamaki yana kuma duban Mu’azzam. Safeenah ma mamaki ne saman fuskarta cikin zuciyarta tana furta mai hakan yake nufi.
Mu’azzam yaci gaba da furta “Ko Wanene mai turo mun wad’ann sak’onnin gargad’i yake mun akanka BAD.. And that means yasan Kun jima kuna k’ulla wani abu kenan kaida Safeenah.. Let’s say Ikram Ta fahimci wani abu taakaninku da Safeenah.. And you two silenced her sabida kar ta sanar dani.. Am I right..?” Ya k’arashe yana dubansu su duka biyun.
Zuciyar Safeenah yai wani irin yankewa. Ta shiga girgiza kai tana fad’in “No.. Wllhi wlhi babu komai tsakanina da Ameer.. Wllhi bansan mai wannan sak’on ke nufi ba..”
“Ai dama bazaki sani ba. Amma shi wanda ya turo min wani clue yake so ya bani game da ku biyun..” Mu’azzam ya fad’i yana tsare Safeenar da idanu.
Ameer ya girgiza kai wannan karon yace “Excuse me Mr Office. Mai kake k’ok’arin fad’i.. What are you trying to accuse us of.? BAD everyone can be BAD.. You can also be BAD... Bad is just a word.. So don’t try to complicate things here..”
Murmushi Mu’azzam keyi wann karon yana duban Ameer d’in “We shall see.!”
Safeenah dake girgiza kai tana hawaye lokaci guda Ta soma fad’in “Wait Mu’azzam wllhi zan fad’i gaskiyar abinda ya faru.. Kar ka fara zargina da cin amanarka balle aurenmu ya lalace.. Wllhi zan fad’i komai koda bazaka yarda dani ba.”
Mu’azzam ya jinjina kai yana mai gyara zamansa lokaci guda yai alamawa Maleeka cewa ta shigo ta tattari bayanan Safeenah. Maleeka kaw kaman wacce take jira, nan take ta shigo.. Ameer sai aika mata mugun kallo yake a sace, yana tinanin idan ba Ita ba babu wanda zai tura ma Mu’azzam sak’on BAD dan yasan duk wanda ya tura sak’on so yake ya raba Mu’azzam d’in da Safeenah.. Maleeka ita kad’ai ce takeda wanann Motive d’in.
Assad ya k’araso sukai musabaha still mamaki saman fuskarsa. Mu’azzam ya tambayesa abinda za’a kawo masa. Nan yace a kawo masa coffee d’in shima. Yai zaune yana duban Mu’azzam d’in yana jira yaji da mai zai fara. Bayan an kawo wa Assad nasa order d’in ya sinkayo muryar Mu’azzam na fad’in “Nasan ka tab’a aure zama baiyi dad’i ba Kun rabu da matar..”
Assad ya dubesa da mamaki jin yau kuma da wannan batun yazo, shi ya zaci ma wani ci gaba suka kuma samu daga binkicen da suke.
Assad ya jinjina kai yace “Haka ne.”
Mu’azzam ya kuma sipping hot coffee d’insa kafin yace “Kanada experience, kasan halittan mata kenan.”
Yanzu kam aje cup d’in dake hannunsa Assad yai yana duban abokin nasa da tsananin mamaki wanda a baya sam bai irin wad’ann zantukan.
Mu’azzam yaci gaba da fad’in “Inaso na maka tambaya a matsayinka na wanda yakeda experience.”
Assad ya jinjina kai yace “Umhum ina saurarenka.
“Idan mace ta gama yawonta da biye biyen maza, after some time ta jima batabi mazan ba tana koma sabuwa ce kaman dai budurwar da bata tab’a sanin wani d’a namiji ba.?”
Bagatatan Assad yaji zancen wanda har saida ya kusan fuzar da coffe d’in da ya shiga bakinsa sabida dariyan da yazo masa.. Da alama abokinsa ya shiga missed call.. Ya k’unshe bakinsa yana darawa a hankali dan Yanzu kam ya gama gane Ina tambayoyin Abokin nasa suka nufa.
Mu’azzam ya aika masa mugun kallo cikeda takaici “You are not serious, you know. Ya ina tambayarka abu kana wani dariya..”
“Toh kuka kake so nayi.. Abun ne abun dariya.. Budurci guda d’aya ne ai.. Halitta ne da Ubangiji ya Karrama ko wace d’iya mace dashi, wacce ta watsar da wannan karamci nata tin a titi bazata kuma samunsa ba, bazai dawo ba duk gyaran da za’ayi kuwa.. Bazata tab’a zama kaman wacce ta Martaba wannan karamci nata ta rik’esa da kyau ba.”
Mu’azzam ya sauk’e ajiyan zuciya a hankali yana mai sipping coffee. Lokaci guda Assad yaci gaba da fad’in “Shiyasa shaidar zina dai takeda matakai daki daki..Ku guje ma mummunan zato ma bayin Allah.. So tari wanda ka munana masa zato shine na k’warai d’in. Sannan so tari wanda ka kyautata masa zato shine na banzan. Amma ko yaushe ana so mutum ya kasance mai kyautata zato.. Ku guje ma d’aukan maganganun mutane domin shi d’anadam a Kullum aibunka yake nema ya yad’a, Sai ya yad’a aibunka sau d’ari kafin ya fad’i alkhairinka guda d’aya.. Ga aibun a tattare da shi amma shi bazaiga nashi ba sai yaje yana hangen na wani.. Allah yasa mu gane ya kuma datar damu.”
Mu’azzam ya amsa da Ameen. Yana mai ci gaba da shan coffee d’insa. Time ya duba yaga Wai har tara na safe Ta d’an gauta ya kamata Su k’arasa Office.. A tare Suka mik’e Mu’azzam yai settling bill d’insu kafin suka nufo waje.
Babu b’ata lokaci suka nufo ofishinsu.
Suna isowa suka tadda Daddy a k’ofan Ofishin nasu. Assad ya dubi Mu’azzam “Wa nake gani kaman Daddy..? Allah sarki ni wllhi duk yafi bani tausayi a al’amarin nan.. Mutumin nan yana k’aunarka Mu’azzam, kaga yanda ya juya ma d’iyarsa baya yak’i ya bama k’arya goyon baya dukda cewa yanada halinda zai iya sakawa a kashe case d’in nan a rufe case d’in gaba d’aya sabida d’iyarsa amma baiyi haka ba.. Gaskiya na jima banga mutum mai dattako da kiman Daddy ba.”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “K’warai Daddy mutumin kirki ne.. Bai cancanci d’iya irin Safeenah ba.. Unfortunately bamu zab’en ahali, farkawa muke kawai mu ganmu tareda mutanen da Allah ya hukunta zasu zama ahalinmu.. Sannan ko wanne ahali sunada nasu k’alubalen da suke fuskanta.. Mu kuma irin namu k’alubalen kenan.. Mu k’arasa..”
Assad ya jinjina kai kafin suka nufo yanda Daddy ke zaune. Gaisawa sukai gaba d’aya kafin Assad ya Shige ya basu waje.
Daddy ya dubi Mu’azzam wanda jinkinsa ya d’anyi sanyi da ganin Daddyn.. Ko Babu komai Safeenah d’iyar Daddy ce jininsa ce dole zaiji wani abu can k’asan zuciyarsa dukda kuwa k’arfin halin da yai.
Mu’azzam yace “Are you here to see Safeenah.? Mu k’arasa sai a kira maka ita..”
Daddy ya girgiza kai yace “Ba Safeenah nazo gani ba Mu’azzam.. Kai nazo gani..”
Mu’azzam ya d’an gyara zamansa yana duban Daddyn.
Daddy yaci gaba da fad’in “Mu’azzam bazan hanaka hukunta Safeenah akan laifinta ba idan har an kamata da laifin.. Amma inada wata alfarma guda d’aya da nake son rok’a daga gareka.”
Mu’azzam ya d’an d’ago ya dubesa “Alfarma kuma Daddy.. Ai ka wuce alfarma a wajena Daddy.. Umarni kawai zaka bani..”
Daddy ya murmusa cikeda jin dad’i kafin ya jinjina kai yace “Allah ya maka albarka Mu’azzam.. Alfarmar da nake nema wajenka shine, dan Allah kar ka saki Safeenah har sai an gama bincike an sameta da laifi.. Kamin wannan alk’awarin cewa bazaka rabu da ita ba har sai an tabbata Tanada laifi.. This is the least I can do for my daughter bayan juya mata baya da nayi..” Ya k’arashe yana duban Mu’azzam d’in cikeda kulawa.
Cak Mu’azzam ya tsaya ba tareda ya iya amsa Daddy ba, saima sadda idanunsa k’asa da yai.
Daddy yai gyaran murya yaci gaba da fad’in “I know it’s not easy, ace kana shari’a da matarka.. But please do this for me.. For our family Mu’azzam.. Kar ka saki Safeenah until she’s proven guilty.. Ina rok’onka ne a matsayin mahaifin Safeenah.. Please Mu’azzam..!”
Ganin Daddy na k’ok’arin had’e hannayensa biyu waje guda alamun rok’o yasa Mu’azzam saurin kamo hannayen Daddy ya hanasa aikata hakan. Yana girgiza kai yake fad’in “Dani da Safeenah Kai Babanmu ne gaba d’aya Daddy.. Yanda zaka umarce Safeenah tai abu ko Musaddiq haka nima zaka mun.. Daddy bazan saketa ba kaman yanda kace.. Safeenah zataci gaba da zama matsayin matata..”
Daddy ya sakar masa murmushi yana k’ok’arin maida k’wallan dake k’ok’arin ciko idanunsa “Na gode Mu’azzam.. Thank you for this.. Allah Ubangiji ya maka albarka ya kuma maka jagora.”
Mu’azzam ya amsa da “Ameen Daddy..”
Daddy ya mik’e yace “Alk’ali ya sanar da Court Hearing d’in ne..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Muna sauraro tukuna Daddy.”
Daddy ya jinjina kai kafin yace “Ni zan wuce Company.. Sai na ganka a gida..”
Mu’azzam ya jinjina kai yana mai rakiyawa Daddyn har zuwa yanda motarsa ke ajiye driver na jira. Suka kuma yin sallama kafin Mu’azzam ya dawo cikin ofishin nasu.
Yana shigowa Assad ya K’araso yana fad’in “Barr Ameer Dikko, Safeenah’s lawyer is here.. Yana son ganawa da Safeenah..”
Sunan Ameer da Assad ya fad’i in full shine yai ringing a k’wak’walwar Mu’azzam. Barr Ameer Dikko.
Duban Assad yai kafin ya kuma duba Barr Ameer dake nufosu cikin takunsa na k’asaita.
Ya k’araso yana gaisar da Mu’azzam cikeda izgilanci irin yanda ya saba. Mu’azzam bai ce masa komai ba Sai aiaka masa muguwar kallo da yake yana nanata sunansa cikin zuciyarsa.
Assad ne yai masu jagoranci gaba d’aya zuwa interrogation yanda Safeenah ke zaune tana jira. A d’an Kwana guda da tai cikin Cell har kamanninta ya canza abinka da wacce bata saba da wahala ba. Farin fatar ta dik yayi wani irin jajaja alamun wahala da rashin sabo.
Ameer ne ya soma shiga suka gana kafin daga bisani Mu’azzam ya shigo. Safeenah na ganinsa ta fashe da kuka tana fad’in “My Halal I can’t believe you are doing this to me.. Please ka k’yaleni na tafi gida.. This place is hell..”
Ameer kaw takaici ya cikasa ganin yanda Safeenah ke shagwab’awa Mu’azzam tana wani kiransa her Halal.
Zama yai gefe yana mai aikawa Ameer mugun kallo. Bai amsa Safeenah ba still idanunsa na kan Ameer yake furta “Barrister Ameer Dikko is your enemy.!”
“Barr Ameer Dikko is ruining your home.!”
“Barr Ameer Dikko is very BAD”
“Barr Ameer Dikko you’re BAD”
Cikin rashin gane kalman nasa suke dubansa daga Ameer d’in har Safeenah.
Ameer ya girgiza kai yace “Ban fahimceka ba Inspector..?”
Murmushi Mu’azzam yai kafin yace “Ba Lallai ka fahimta ba amma Iyakacin abinda na sani YOU ARE BAD..”
Ameer ya kuma dubansa kai a k’ulle, lokaci guda Mu’azzam ya ciro wayarsa cikin aljihu yana nunawa Ameer sak’onnin BAD da akaita turo masa kwanakin baya. Ameer ya dubi sak’onnin da tsananin mamaki yana kuma duban Mu’azzam. Safeenah ma mamaki ne saman fuskarta cikin zuciyarta tana furta mai hakan yake nufi.
Mu’azzam yaci gaba da furta “Ko Wanene mai turo mun wad’ann sak’onnin gargad’i yake mun akanka BAD.. And that means yasan Kun jima kuna k’ulla wani abu kenan kaida Safeenah.. Let’s say Ikram Ta fahimci wani abu taakaninku da Safeenah.. And you two silenced her sabida kar ta sanar dani.. Am I right..?” Ya k’arashe yana dubansu su duka biyun.
Zuciyar Safeenah yai wani irin yankewa. Ta shiga girgiza kai tana fad’in “No.. Wllhi wlhi babu komai tsakanina da Ameer.. Wllhi bansan mai wannan sak’on ke nufi ba..”
“Ai dama bazaki sani ba. Amma shi wanda ya turo min wani clue yake so ya bani game da ku biyun..” Mu’azzam ya fad’i yana tsare Safeenar da idanu.
Ameer ya girgiza kai wannan karon yace “Excuse me Mr Office. Mai kake k’ok’arin fad’i.. What are you trying to accuse us of.? BAD everyone can be BAD.. You can also be BAD... Bad is just a word.. So don’t try to complicate things here..”
Murmushi Mu’azzam keyi wann karon yana duban Ameer d’in “We shall see.!”
Safeenah dake girgiza kai tana hawaye lokaci guda Ta soma fad’in “Wait Mu’azzam wllhi zan fad’i gaskiyar abinda ya faru.. Kar ka fara zargina da cin amanarka balle aurenmu ya lalace.. Wllhi zan fad’i komai koda bazaka yarda dani ba.”
Mu’azzam ya jinjina kai yana mai gyara zamansa lokaci guda yai alamawa Maleeka cewa ta shigo ta tattari bayanan Safeenah. Maleeka kaw kaman wacce take jira, nan take ta shigo.. Ameer sai aika mata mugun kallo yake a sace, yana tinanin idan ba Ita ba babu wanda zai tura ma Mu’azzam sak’on BAD dan yasan duk wanda ya tura sak’on so yake ya raba Mu’azzam d’in da Safeenah.. Maleeka ita kad’ai ce takeda wanann Motive d’in.