Sashe 124
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ya isa haka Kimin shiru..” Ya fad’i yana d’aukanta Cak cikin hannunsa.
Sadiya Ta kuma fashewa da kuka ta nufin cikin gidan a guje kukan na fin k’arfinta.
Patrick ya bita da kallo cikeda tausayawa dan shi kanshi yasha mamakin tuggun da Safeenah ta k’ulla.
Motar Safeenar Mu’azzam ya shigar da ita gefen mai zaman banza kafin ya zagayo ya zauna a mazaunin driver. Sai matse ido take kaman da gaske tana jin jiki, tana yi tana satan kallonsa yanda ya kai matuk’a wajen tsimewa.
Ya daidaita zamansa saman kujeran ya soma driving. Safeenah na kuma sakin sabon kuka tana fad’in cikinta.
Birki ya taka wanda saida ya sanyata had’iye kukan nata cak, ta d’ago tana dubansa a tsorace.
“Safeenah..!” Ya fad’i a hankali idanunsa naga kwalta.
Ta saci kallonsa kad’an. Lokaci guda yaci gaba da furta “If something bad happens to your pregnancy.. Believe me, you will regret it..!”
Ya d’ago yana dubanta yana jinjina kai alamun tabbatarwa, hannayensa saman steering wheel yake ci gaba da fad’in “Idan kika kashe mun d’a da ganganciniki ki yarda dani, bazan sassauta miki ba har sai kin biya abinda kika aikata... Ki rubuta hakan ki ajiye..” Yana maganar yana jinjina kai alamun tabbatar da kalamansa.
Baki sake Safeenah ke dubansa, sai kuma ta soma sakin huci tana fad’in “Matarka tayi niyyan kashe min d’a shine zaka tasa ni gaba da fad’a kana gani Ina cikin sever pain amma dikda haka bayan wancan makirar kake bi.”
“Ke kar ki maidani D’aniska.. Nasan abinda nake.. Mai ya kaiki gidan in the first place.. Ni ne zaki raina ma hankali, wani Wai kinada appointment da Dr.. Inace jiya da dare mukaje kikaga likitan.. A yaushe kukayi setting appointment din..”
Ta turo baki ranta a jagule.
Ya kuma gyara zamansa yana fuskantar ta sosai “Kina jina.. Kar ki kuskura Safeenah.. Kar ki kuskura.. I am warning you.!” Ya k’arashe cikeda gargad’i, daidai sanda wayarsa Ta soma ruri. Mommy ce mai kiran nasa.
Ya d’an harari Safeenar dake ci gaba da ture turen baki kafin ya d’aga wayar.
Yana d’agawa Mommy Ta soma fad’in “Mu’azzam idan kana tare da Safeenah bata wayar muyi magana, ga wayarta ta bari a gida sann ta d’auki car keys ta fice ban Sani ba..”
Duban Safeenar ya kumayi kafin ya mik’a mata wayan ba tareda yace komai ba.
Ta amsa tana k’arawa a kunnenta dan ta fahimci Mommy ce. D’add’aya Mommy tai mata sann tace tasa aniya ta dawo gida.
**
Sadiya kaw tana shigewa gida wani sabon kuka Ta fashe dashi, Ta soma tinanin abubuwan da suka faru daki daki, tin daga k’in d’aga kiranta da yai yaita rejecting, sann da ya dawo baibi takanta ba, yanzu ga abinda ya mata, bai saurara daga b’angarenta ba amma ya hau kan abinda Safeenah tace.. Ta kuma tina yanda ya d’auki Safeenar cikin hannunsa ya shigar da ita mota.. Take taji wasu sabbin k’walla suna ciko idanunta. Cikin kuka Ta nufi upstairs ta d’auko handbag da mayafinta.
Tana fitowa Patrick ya tareta yana tambayarta Ina zata ganin har lokacin bata daina matsan idanunta da suka kod’e sabida kuka ba.
“Ma’am please don’t leave.. Laifina ne da na fitar da Karnunkan, Believe me bansan Oga ya iso ba.. Kuma bansan abun zai juya ya zama haka ba.. Dan Allah Ma’am kiyi hak’uri ki dawo.. It’s all my fault.. But I’m sure Oga zai fahimci matar can makirci kawai ta k’ulla.”
K’ok’arin saita kanta tai tace “Kar ka damu Patrick. Ka daina d’ora ma kanka laifi kaji koh.. Bazai ce komai ba dan na tafi..”
“But M’am last time da kika tafi na samu matsala sosai da oga, kar na kuma shiga wani matsalan.”
Ta girgiza kai kad’an tace “Wancan karon da wann akwai banbanci..” Tai maganar tana mai ficewa.
Patrick ya biyo bayanta yana fad’in “Ma’am toh ki bari a kirawo miki Cab..”
Bata sami zarafin sauraron Patrick ba dan tuni ta fice daga gidan. Patrick yai tsaye yana kallonta yana tunanin yanda zasu kuma kwashewa da Mu’azzam.
**
Haka Safeenah ta kumbura ta cika tai fam cikeda jin haushin plan d’inta bai mata aiki yanda taso ba.. Wllhi dole ta sanar dasu Daddy ciki ne da ita tasan zasu sa Mu’azzam ya maidata. Da wann tunanin suka iso gida.
Ya tasata gaba yana biye da ita, har lokacin a kumbure take kaman zata fashe.
Suna haurawa sama suka tadda Mommy tana jiran shigowarsu.
Aiko suna shiga Safeenah ta duk’a tana kame cikinta tana sakin k’ara kad’an.
Mommy dake cike fam da niyyan tsefe mata masifa nan tayo kanta tana ambaton sunanta. Mu’azzam ma ya k’araso yana ambato sunan Safeenar.
Mommy ta nufi d’aki babu shiri Ta d’auko mata wasu pills ta mik’a mata had’ida glass of water tace maza tasha.
Babu musu Safeenah Ta amsa Ta had’iyi pills d’in har guda biyu Mu’azzam na mata sannu.
Ikon Allah maimakon ciwo ya lafa amma tana shan wad’ann pills d’in da Mommy ta bata sai ciwo ya k’aru babu k’akk’autawa.
Mommy tai tsaye tana dubanta yayinda Mu’azzam ya d’an kuma duk’awa yana ambato sunan Safeenar wacce da gaske take murk’usoso yanzu kam.
“Feenah can you hear me.. Safeenah do you need a Dr..?” Dik a d’an birkice yake maganar.
Muryar Mommy ne ya katsesa “Babu yanda zataje.. Ba kuma Likitan da za’a kira..”
Da tsananin mamaki ya d’ago yana duban Mommy dake wann maganar ga d’iyarta cikin pain. Ya girgiza kai kad’an yace “Mommy kin kuwa ji mai kike cewa..?”
“K’warai kuwa naji kuma nasan mai nake cewa.. Duba nan kaga..” Tai masa nuni da k’afar Safeenah da tuni siririn Jini ya soma gangarowa.
Mommy Ta kafesa da idanu tana murmushi ga Safeenah kwance k’asa tana murk’usoso tana rik’e mararta.
“Gashi nan.. Ga D’an Naka yana fita... Sai ka duk’a ka tattara d’anka.. Na fad’a maka sai na d’au fansar duk k’uncin da ka jefa mu ciki.. Ba’a cin bashin Hajara a wanye lafiya Mu’azzam.. Wann shine sakamakon duk rashin darajan da ka jaza mana.. A tunaninka zan bari cikin nan ya fice garin sakarcin Safeenah da wautan ta ne.. A’a ai idan na bari D’an ya fice garin haukar Safeenah ai na cutu.. Ban k’untata maka ba kenan.. Naci alwashin ni zan salwantar da wann shegen cikin naka Mu’azzam.. Kaman yanda ka k’untata mun lokuta da dama... Kaman yanda ka k’untatawa d’iyata Safeenah.. Toh D’ah baifi D’ah na kaima kaji dik irin k’uncin da naji.. Gashi nan ga gudan jininka na bin k’asa.. Ka tsuguna ka kwashe gudan jinin naka..” Ta k’arashe tana masa nuni da jinin dake d’iga daga k’afafun Safeenah wacce keta ihu tana neman d’auki tana kame mararta.
A daidai lokacin Musaddiq da ihun Safeenah ya tadashi daga bacci ya shigo parlorn. Cak ya tsaya yana sauraren Mommy dake ci gaba da fad’iwa Mu’azzam ya duk’a ya kwashe gudan jininsa.
Wani irin zufa ne ke tsartsafo masa.. Duban Mommy yake cikin wane irin yanayi.. Ko a labarai bai tab’a ji ko ganin mai hali irin na Mommy ba.. Sabida mugun zuciya Ta zab’i Ta salwantar da jikanta dan kawai ta k’untata masa.. Shin mai yayi wa Mommy da tsanani..? Shin wann wane irin tsana ne.. Shin Sakin Safeenah da yayi a gabanta ne har yakai tai masa irin wann hukuncin kokuwa dai auren da yayi ba da saninsu bane sann ya tare da matar a gidan Safeenah kafin akai Safeenah shine dalilinta na yi masa wann hukuncin..? Shin cikin abubuwan da yai har akwai wanda yakai tai masa irin wann tsartsauran hukunci..?
Gumi bai daina karyowa daga cikin sumarsa zuwa goshinsa ba, yaci gaba da takowa yana duban Mommy cikin wane irin yanayi.. Jinjina kai ya shiga yi still yana duban Mommy “You.. You’ve gone too far..! Kin tafi da nisa wann karon.. Kin tafi da nisa.!” Ya k’arashe numfashinsa na fita a hankali yana kuma jinjina kai yana duban Mommy da idanunsa da suka gama kad’awa.
Juyawa yai zai fice Musaddiq yai saurin bin bayansa yana kiran sunansa saidai Inaa bai cimma Mu’azzam ba.
Musaddiq ya dawo da sauri ya k’arasa kan Safeenah yana k’ok’arin taimaka mata yana mata sannu, lokaci guda yake aikawa Mommy dake tsaye tana dubansu mugun kallo.
Safeenah kuka take tana fad’iwa Musaddiq “My Baby.. My baby Musaddiq.. My Baby.. I don’t wanna lose my Baby.. Tell me Musaddiq.. Please tell me nothing bad is goin to happen to my child.. Please tell me..!” Ta k’arashe cikin tsananin kuka mai ban tausayi tana kukan tana kame cikinta.
Musaddiq yai saurin rungume Safeenah daga nan yanda take duk’e tana cazgan kuka mai tab’a zuciya.
Hawaye ne yaji suna gangaro masa, tausayi da k’aunar ‘yaruwarsa fal zuciyarsa. Sosai ya rungume kan Safeenah cikin k’irjinsa yana k’ok’arin lallashinta.
Iya ce ta shigo Musaddiq yai mata umarni ta taimakawa Safeenah. Iya ma hankali tashe take k’ok’arin d’ago Safeenar. Tana mata sannu suka nufi d’aki har lokacin Safeenah kuka take cikin tsananin sanyin jiki tana kame da cikinta. Kallo guda zakai mata ka fahimci batama a cikin hayyacinta.
Suna shigewa d’aki Musaddiq ya d’ago yana duban Mommy yana jinjina kai, lokaci guda yake furta “Kin gama mugunta Mommy.. Kin gama cutar da kowa da muguwar zuciyarki..!”
Mommy Ta daka masa tsawa da fad’in “Musaddiq.!” Mommy taci gaba da huci tana fad’in “Ko ban cire wann tsinannen cikin ba Safeenah zata ciresa da haukarta.!”
Hawaye na zubo masa yaci gaba da jinjina kai yana fad’in “Kiyi shiru Mommy.. Kin riga da kin b’ata komai..!”
Mommy Ta soma hawaye tana fad’in “Bazan tab’a yarda na had’a iri da Nuratu ba.. Never Musaddiq..!”
Cikin kuka yake furta “Don’t call my name.. Don’t you dare call my name Mommy.. You are not going to stop Mommy.. Right..? Ke d’in Bazaki tab’a dakatawa ba..!” Yaci gaba da jinjina kai alamun tabbatarwa “Zan sanar da Mu’azzam da Daddy komai.. Duk abinda na sani akanki Mommy.. Zan sanar dasu komai.. Bazan kuma rufa miki asiri ba Mommy..!”
Cikin rashin fahimta Mommy ke girgiza kai tana fad’in “Mai kake nufi Musaddiq..? What are you talking about.. Mai ka sani akaina..?”
Sadiya Ta kuma fashewa da kuka ta nufin cikin gidan a guje kukan na fin k’arfinta.
Patrick ya bita da kallo cikeda tausayawa dan shi kanshi yasha mamakin tuggun da Safeenah ta k’ulla.
Motar Safeenar Mu’azzam ya shigar da ita gefen mai zaman banza kafin ya zagayo ya zauna a mazaunin driver. Sai matse ido take kaman da gaske tana jin jiki, tana yi tana satan kallonsa yanda ya kai matuk’a wajen tsimewa.
Ya daidaita zamansa saman kujeran ya soma driving. Safeenah na kuma sakin sabon kuka tana fad’in cikinta.
Birki ya taka wanda saida ya sanyata had’iye kukan nata cak, ta d’ago tana dubansa a tsorace.
“Safeenah..!” Ya fad’i a hankali idanunsa naga kwalta.
Ta saci kallonsa kad’an. Lokaci guda yaci gaba da furta “If something bad happens to your pregnancy.. Believe me, you will regret it..!”
Ya d’ago yana dubanta yana jinjina kai alamun tabbatarwa, hannayensa saman steering wheel yake ci gaba da fad’in “Idan kika kashe mun d’a da ganganciniki ki yarda dani, bazan sassauta miki ba har sai kin biya abinda kika aikata... Ki rubuta hakan ki ajiye..” Yana maganar yana jinjina kai alamun tabbatar da kalamansa.
Baki sake Safeenah ke dubansa, sai kuma ta soma sakin huci tana fad’in “Matarka tayi niyyan kashe min d’a shine zaka tasa ni gaba da fad’a kana gani Ina cikin sever pain amma dikda haka bayan wancan makirar kake bi.”
“Ke kar ki maidani D’aniska.. Nasan abinda nake.. Mai ya kaiki gidan in the first place.. Ni ne zaki raina ma hankali, wani Wai kinada appointment da Dr.. Inace jiya da dare mukaje kikaga likitan.. A yaushe kukayi setting appointment din..”
Ta turo baki ranta a jagule.
Ya kuma gyara zamansa yana fuskantar ta sosai “Kina jina.. Kar ki kuskura Safeenah.. Kar ki kuskura.. I am warning you.!” Ya k’arashe cikeda gargad’i, daidai sanda wayarsa Ta soma ruri. Mommy ce mai kiran nasa.
Ya d’an harari Safeenar dake ci gaba da ture turen baki kafin ya d’aga wayar.
Yana d’agawa Mommy Ta soma fad’in “Mu’azzam idan kana tare da Safeenah bata wayar muyi magana, ga wayarta ta bari a gida sann ta d’auki car keys ta fice ban Sani ba..”
Duban Safeenar ya kumayi kafin ya mik’a mata wayan ba tareda yace komai ba.
Ta amsa tana k’arawa a kunnenta dan ta fahimci Mommy ce. D’add’aya Mommy tai mata sann tace tasa aniya ta dawo gida.
**
Sadiya kaw tana shigewa gida wani sabon kuka Ta fashe dashi, Ta soma tinanin abubuwan da suka faru daki daki, tin daga k’in d’aga kiranta da yai yaita rejecting, sann da ya dawo baibi takanta ba, yanzu ga abinda ya mata, bai saurara daga b’angarenta ba amma ya hau kan abinda Safeenah tace.. Ta kuma tina yanda ya d’auki Safeenar cikin hannunsa ya shigar da ita mota.. Take taji wasu sabbin k’walla suna ciko idanunta. Cikin kuka Ta nufi upstairs ta d’auko handbag da mayafinta.
Tana fitowa Patrick ya tareta yana tambayarta Ina zata ganin har lokacin bata daina matsan idanunta da suka kod’e sabida kuka ba.
“Ma’am please don’t leave.. Laifina ne da na fitar da Karnunkan, Believe me bansan Oga ya iso ba.. Kuma bansan abun zai juya ya zama haka ba.. Dan Allah Ma’am kiyi hak’uri ki dawo.. It’s all my fault.. But I’m sure Oga zai fahimci matar can makirci kawai ta k’ulla.”
K’ok’arin saita kanta tai tace “Kar ka damu Patrick. Ka daina d’ora ma kanka laifi kaji koh.. Bazai ce komai ba dan na tafi..”
“But M’am last time da kika tafi na samu matsala sosai da oga, kar na kuma shiga wani matsalan.”
Ta girgiza kai kad’an tace “Wancan karon da wann akwai banbanci..” Tai maganar tana mai ficewa.
Patrick ya biyo bayanta yana fad’in “Ma’am toh ki bari a kirawo miki Cab..”
Bata sami zarafin sauraron Patrick ba dan tuni ta fice daga gidan. Patrick yai tsaye yana kallonta yana tunanin yanda zasu kuma kwashewa da Mu’azzam.
**
Haka Safeenah ta kumbura ta cika tai fam cikeda jin haushin plan d’inta bai mata aiki yanda taso ba.. Wllhi dole ta sanar dasu Daddy ciki ne da ita tasan zasu sa Mu’azzam ya maidata. Da wann tunanin suka iso gida.
Ya tasata gaba yana biye da ita, har lokacin a kumbure take kaman zata fashe.
Suna haurawa sama suka tadda Mommy tana jiran shigowarsu.
Aiko suna shiga Safeenah ta duk’a tana kame cikinta tana sakin k’ara kad’an.
Mommy dake cike fam da niyyan tsefe mata masifa nan tayo kanta tana ambaton sunanta. Mu’azzam ma ya k’araso yana ambato sunan Safeenar.
Mommy ta nufi d’aki babu shiri Ta d’auko mata wasu pills ta mik’a mata had’ida glass of water tace maza tasha.
Babu musu Safeenah Ta amsa Ta had’iyi pills d’in har guda biyu Mu’azzam na mata sannu.
Ikon Allah maimakon ciwo ya lafa amma tana shan wad’ann pills d’in da Mommy ta bata sai ciwo ya k’aru babu k’akk’autawa.
Mommy tai tsaye tana dubanta yayinda Mu’azzam ya d’an kuma duk’awa yana ambato sunan Safeenar wacce da gaske take murk’usoso yanzu kam.
“Feenah can you hear me.. Safeenah do you need a Dr..?” Dik a d’an birkice yake maganar.
Muryar Mommy ne ya katsesa “Babu yanda zataje.. Ba kuma Likitan da za’a kira..”
Da tsananin mamaki ya d’ago yana duban Mommy dake wann maganar ga d’iyarta cikin pain. Ya girgiza kai kad’an yace “Mommy kin kuwa ji mai kike cewa..?”
“K’warai kuwa naji kuma nasan mai nake cewa.. Duba nan kaga..” Tai masa nuni da k’afar Safeenah da tuni siririn Jini ya soma gangarowa.
Mommy Ta kafesa da idanu tana murmushi ga Safeenah kwance k’asa tana murk’usoso tana rik’e mararta.
“Gashi nan.. Ga D’an Naka yana fita... Sai ka duk’a ka tattara d’anka.. Na fad’a maka sai na d’au fansar duk k’uncin da ka jefa mu ciki.. Ba’a cin bashin Hajara a wanye lafiya Mu’azzam.. Wann shine sakamakon duk rashin darajan da ka jaza mana.. A tunaninka zan bari cikin nan ya fice garin sakarcin Safeenah da wautan ta ne.. A’a ai idan na bari D’an ya fice garin haukar Safeenah ai na cutu.. Ban k’untata maka ba kenan.. Naci alwashin ni zan salwantar da wann shegen cikin naka Mu’azzam.. Kaman yanda ka k’untata mun lokuta da dama... Kaman yanda ka k’untatawa d’iyata Safeenah.. Toh D’ah baifi D’ah na kaima kaji dik irin k’uncin da naji.. Gashi nan ga gudan jininka na bin k’asa.. Ka tsuguna ka kwashe gudan jinin naka..” Ta k’arashe tana masa nuni da jinin dake d’iga daga k’afafun Safeenah wacce keta ihu tana neman d’auki tana kame mararta.
A daidai lokacin Musaddiq da ihun Safeenah ya tadashi daga bacci ya shigo parlorn. Cak ya tsaya yana sauraren Mommy dake ci gaba da fad’iwa Mu’azzam ya duk’a ya kwashe gudan jininsa.
Wani irin zufa ne ke tsartsafo masa.. Duban Mommy yake cikin wane irin yanayi.. Ko a labarai bai tab’a ji ko ganin mai hali irin na Mommy ba.. Sabida mugun zuciya Ta zab’i Ta salwantar da jikanta dan kawai ta k’untata masa.. Shin mai yayi wa Mommy da tsanani..? Shin wann wane irin tsana ne.. Shin Sakin Safeenah da yayi a gabanta ne har yakai tai masa irin wann hukuncin kokuwa dai auren da yayi ba da saninsu bane sann ya tare da matar a gidan Safeenah kafin akai Safeenah shine dalilinta na yi masa wann hukuncin..? Shin cikin abubuwan da yai har akwai wanda yakai tai masa irin wann tsartsauran hukunci..?
Gumi bai daina karyowa daga cikin sumarsa zuwa goshinsa ba, yaci gaba da takowa yana duban Mommy cikin wane irin yanayi.. Jinjina kai ya shiga yi still yana duban Mommy “You.. You’ve gone too far..! Kin tafi da nisa wann karon.. Kin tafi da nisa.!” Ya k’arashe numfashinsa na fita a hankali yana kuma jinjina kai yana duban Mommy da idanunsa da suka gama kad’awa.
Juyawa yai zai fice Musaddiq yai saurin bin bayansa yana kiran sunansa saidai Inaa bai cimma Mu’azzam ba.
Musaddiq ya dawo da sauri ya k’arasa kan Safeenah yana k’ok’arin taimaka mata yana mata sannu, lokaci guda yake aikawa Mommy dake tsaye tana dubansu mugun kallo.
Safeenah kuka take tana fad’iwa Musaddiq “My Baby.. My baby Musaddiq.. My Baby.. I don’t wanna lose my Baby.. Tell me Musaddiq.. Please tell me nothing bad is goin to happen to my child.. Please tell me..!” Ta k’arashe cikin tsananin kuka mai ban tausayi tana kukan tana kame cikinta.
Musaddiq yai saurin rungume Safeenah daga nan yanda take duk’e tana cazgan kuka mai tab’a zuciya.
Hawaye ne yaji suna gangaro masa, tausayi da k’aunar ‘yaruwarsa fal zuciyarsa. Sosai ya rungume kan Safeenah cikin k’irjinsa yana k’ok’arin lallashinta.
Iya ce ta shigo Musaddiq yai mata umarni ta taimakawa Safeenah. Iya ma hankali tashe take k’ok’arin d’ago Safeenar. Tana mata sannu suka nufi d’aki har lokacin Safeenah kuka take cikin tsananin sanyin jiki tana kame da cikinta. Kallo guda zakai mata ka fahimci batama a cikin hayyacinta.
Suna shigewa d’aki Musaddiq ya d’ago yana duban Mommy yana jinjina kai, lokaci guda yake furta “Kin gama mugunta Mommy.. Kin gama cutar da kowa da muguwar zuciyarki..!”
Mommy Ta daka masa tsawa da fad’in “Musaddiq.!” Mommy taci gaba da huci tana fad’in “Ko ban cire wann tsinannen cikin ba Safeenah zata ciresa da haukarta.!”
Hawaye na zubo masa yaci gaba da jinjina kai yana fad’in “Kiyi shiru Mommy.. Kin riga da kin b’ata komai..!”
Mommy Ta soma hawaye tana fad’in “Bazan tab’a yarda na had’a iri da Nuratu ba.. Never Musaddiq..!”
Cikin kuka yake furta “Don’t call my name.. Don’t you dare call my name Mommy.. You are not going to stop Mommy.. Right..? Ke d’in Bazaki tab’a dakatawa ba..!” Yaci gaba da jinjina kai alamun tabbatarwa “Zan sanar da Mu’azzam da Daddy komai.. Duk abinda na sani akanki Mommy.. Zan sanar dasu komai.. Bazan kuma rufa miki asiri ba Mommy..!”
Cikin rashin fahimta Mommy ke girgiza kai tana fad’in “Mai kake nufi Musaddiq..? What are you talking about.. Mai ka sani akaina..?”