Sashe 15
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin huci kurum Mu’azzam yake yana dunk’ule hannunsa, lokaci guda ya bugi table d’in yana furta “I knew it.!” Lokaci guda ya fuzgi takardan ya fice daga office d’in cikin tsananin b’acin rai sai sakin huci yake kaman zai kifa k’asa...
Cikin sauri Assad yabi bayansa dan yasan komai ka iya faruwa tsakanin Mu’azzam da Chief Inspector.
Hankali tashe Assad ke k’ok’arin taresa ko kula Assad baiba har saida ya daki k’ofan Office d’in Chief..
Chief na cikin waya yana kwance cikin kujerarsa mai juyawa sai ganin Mu’azzam yai akansa yana sakin huci kaman wani mayuwancin zaki..
Babu shiri Chief ya katse wayar da yake yana duban Mu’azzam da tsananin mamaki
“How dare you barge into my office.. Who do you think you are..!” Cikin tsananin b’acin rai Chief yake maganar yana duban Mu’azzam dake tsaye gabansa idanunsa babu alamun tsoro..
Lokaci guda Mu’azzam ya d’ago Sketch d’in yana nunama Chief “Do you still have any reason to depend this criminal..?!”
Ko ba’a fad’a maka ba tsoro ya bayyana a fuskar Chief Inspector amma Sai ya dake yace “Kai k’aramin maras kunya. Kasan da wanda kake magana.. Naga irinka dubu kuma na gama dasu..”
Baikai aya ba Mu’azzam ya katsesa da fad’in “Bakaga irina ba kuma kafin kaga irina sai na tabbatar na gama dakai..”
Wannan karon murmushi Chief yai yace “Mind your language boy.. Bakada hujjan cewa na kare mai laifi domin kuwa dani da kai bamu San wanene Danger bamusan he’s connected to crime d’in nan ba sai yanzu...” Ya murmusa kad’an kafin yace “Har yanzu kaid’in yaro ne a gidan nan.. Har yanzu bakasan yanda Al’amara ke gudana a gida irin wannan ba.. You’re lucky, you’re from well known and respective family, I should’ve thrown you out cikin k’ask’anci . Now, get out of my office befor you lose everything .. Including your career as a police officer..!” Ya k’arashe muguwar murmushin saman fuskarsa..
Daidai lokacin Assad ya shigo a rud’e yana neman afuwan Chief on behalf of friend’s behavior..
Mu’azzam kaw har lokacin huci kurum yake yana duban Chief Inspector da idanunsa da tuni sun gama rinewa..
Chief ya dubi Assad d’in yace “Take him out.. Fitar dashi daga nan..!”
“Don’t touch me.. Don’t you dare touch me..!” Mu’azzam yai kashedi ma Assad kafin ya dubi Chief yace “Wata rana zamu had’u..! Alk’awari ne..!” Daga haka juyawa yai ya fice zuciyarsa na masa tsananin k’una..
Assad zai magana Mu’azzam ya d’aga masa hannu alamun dakatarwa “Not now Assad.!”
Fuzar da fuci kurum Assad yai kafin yabi bayan Mu’azzam d’in...
Su duka hud’in suna tsartsaye sunyi carko carko.. Suna kuma duban hoton Danger da ya bayyana cikin sketch d’in..
Assad ya nusa yace “What do we do now.. Danger must be in a hide tinda yasan dole za’a nemesa... Bazai tab’a zama nan kusa ba.. Allah Sa ma bai gudu ya bar gari ba..”
Yusuf yace “Ba Lallai Danger yasan ana nemansa ba, so ba lallai ace tsakanin jiya zuwa yau ya gudu ba..”
Muryar Mu’azzam suka sinkayo yana fad’in “We will track him down before yayi making move.. I know by now informer d’insa ya sanar dashi muna nemansa..!”
Gaba d’aya suka jinjina kai..
“Zamu fita yanzun nan zamuje unguwarsu Danger, but zamu fita ne a shirye dan nasan wannan area d’in territory d’insa ne komai ka iya faruwa..”
Suka jinjina kai suna amsawa.. Tuni ko Wannen su ya soma shirya weapon d’insa..
Maleeka ta d’an saci kallonsu yayinda suke ci gaba da tattaunawar yanda zasu tunk’ari al’amarin.. A hankali ta silale ta fice daga Ofishin gaba d’aya sai sauri take waya manne kunnenta tana faman waige waige..
A haka take gangarowa har ta d’anyi k’asa kad’an daga Building d’in nasu still tana ‘yan waige waige tana amsa waya..
Safeenah da k’arasowar motarsu wajen kenan Ta hangi Maleeka tsaye waya mak’ale kunnenta...
Wani irin wawan birki ta taka saida Meema dake zaune kujerar mai zaman banza ta saki ihu.
Hakan yayi daidai da k’aran da Umman Sadiya Ta saki wacce tayar Mota guda tabi mata kan k’afarta dan dama tin fitowarsu suke tsaye wajen suna neman abin hawa.. Umma ta sunkuya tana kame k’afarta dake mata zogi Sadiya na mata sannu..
D’agowa Sadiya tai tana jiran tagafitowar maras mutuncin matuk’in motar nan da yabi mata kan k’afar mahaifiya..
Wasu ‘yanmata ne ‘yangayun gaske guda biyu ta gansu Sun fito.. D’ayar fad’i take “Meema ki bud’e backseat ki d’auko.. Kiyi sauri mu k’arasa muci uwarta wllhi itace.. Bazan tab’a mance munin fuskarta ba..!”
Safeenah Batakai aya ba taji an rik’ota, ta juyo da mamaki tana duban wacce ta rik’eta.. Saida gabanta yayi wani irin fad’uwa da ganin kyakkyawar yarinyar data rik’ota tana sakin huci..
“Baiwar Allah baki gani ne kika bige min mahaifiya..?”
Sadiya tace tana duban Safeenar..
Wani irin wualak’antaccen kallo Safeenah da Meema suka raka Su Sadiya dashi kafin Meema tace “An bige ku d’in, ku makafi ne zaku tsaya bakin kwalta.. Ko kuma kurame ne ku da bazakuji sautin mota na zuwa ba..!”
Safeenah Ta finciki hannunta tana fad’in “Ke kika tsaya biyesu Meema, Ai shi Talaka dik yanda yaga mai kud’I hassada dashi yake.. K’iris yake jira ya hau d’aura masa laifi.. Muje kafin wancan shegiyar Ta tsere mana..”
Suka nufi d’aya length d’in cikin sauri yanda Maleeka take..
Sady tai kaman zatabi bayansu Umma ta rik’ota tana fad’in “K’yalesu Sadiya muji da rikicin dake kanmu bana fata mu kuma shiga wani fitinan..”
Sady tace “Amma Umma baki ganin abinda suka mana.”
Umma ta katseta da fad’in “K’yalesu Sadiya, ni mu samu mu bar wajen nan ma..” Ta k’arashe tana mai jan k’afar nata da k’yar Sadiya na mata sannu..
Maleeka tana tsaye taji an fincikota an fuzge wayar hannunta anyi jifa dashi had’ida kwasheta da wane irin mari mai walk’iya...
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*09*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Dafe da k’unci Maleeka ke dubansu da tsananin mamaki “Lafiya su waye ku..?”
Cikin azama Meema ta b’arke Babban roll d’in sanitary pad dake rik’e hannunta, kan kace mai sun shiga jifan fuskar Maleeka dashi.
Maleeka ta duk’a tana kare fuskarta da hannuwanta tana kuma tambayarsu su waye su mai ta masu..
Meema ta kuma jefa mata a fuska tana fad’in “Kinji Munafuka Adda Feenah tambaya ma take su waye mu.. Toh uwarki ne mu, ‘yar iska kawartuwa mai bin mazan mutane.”
Safeenah ta cab’i zancen da fad’in “Gashi nan kece matsiyaciya mai jiran namiji ya mata hidima, ki tattara duka.. Idan shi guda d’aya Yayi niyyan baki toh ga roll an baki.. Matsiyaciyar banza sauran kwalta..”
A hankali Meema ta soma jada baya sakamakon hango su Mu’azzam da tai sun fito daga building d’in.. Meema ta aune a guje ta nufi mota, tana bud’e marfin motar ta shige backseat.. Yanda ake aje k’afafu a wajen ta kwanta tai flat yanda babu mai iya hangota..
Safeenah kaw ta yanda take shiga bata nan take fita ba Sai jifan Maleeka take da sanitary pads tana kwashe mata albarka.. Mutane dake shigewa jefi jefi sai kallonsu suke da tsananin mamaki..
Assad ne ya soma hangosu.. Babu shiri ya tab’a Mu’azzam yace “Ai gacen Officer Maleeka.. But wait what’s going on..? Itada wacece..?”
Daidai lokacin Mu’azzam ya juyo, Assad na furta “Kaman Safeenah ce fah.. Mai take a nan..?”
Cikin sassarfa suka nufo yanda su Safeenah suke.. Da tsananin mamaki kurum Mu’azzam ke dubanta, bai zaici Safeenah zatayi abu makamancin haka ba..
“Safeenah.!!” Ya kirawo sunanta cikin tsananin b’acin rai
Cak ta tsaya ta dena abinda take.. Mu’azzam ya tsareta da idanunsa da suka kuma rikid’ewa zuwa ja, dama ransa a b’ace yake dan har ya kamo Danger Chief yasa ya sake shi gashi yanzu ya tabbata Danger nada alak’a da crime d’in da yake bincike..
Kallon wajen yake da mamaki, Wato abinda Safeenah ta gani cikin aljihunsa shine ta biyo Maleeka har Office taci mutuncinta dashi, watau a haukan Safeenah Maleeka budurwarsa ce.. Muryar Maleeka ne cikin kuka ya katse masa tinanin nasa “Sir, wllhi ni bansan mai na mata ba.. I don’t even know her, kawai gani nayi Ta soma attacking d’ina..”
Assad ne ya tari Maleeka da fad’in “Kiyi hak’uri Maleeka let’s talk somewhere else.. Kiyi hak’uri please..”
Maleeka ta d’ago tana duban Mu’azzam dake ci gaba da tururi ga Safeenah tsaye gabansa sai faman huci itama take tana ture turen baki..
Assad ya tasa Maleeka gaba yana fad’in suje.. Bataso tafiyan ba taso taga yanda Mu’azzam zasu kwashe da matarsa.. Ta kula matar Mu’azzam ce wannan wacce akayi aurensu sati biyu da suka shige, dama an fad’a mata cuna masa ita kawai akayi Mu’azzam ba sonta yake ba, Lallai yau ta tabbatar da hakan. Wani irin sanyi mai gauraye da annashuwa ne suka gauraye Zuciyarta.. Watau matar Mu’azzam tana tinanin Ita d’in budurwarsa ce, aiko bazata tab’a losing hope akan Mu’azzam ba tinda har ta zamto babban threat ga matarsa irin haka.. Da wannan rashin hankalin matar tasa tsaf zata iya samun gurbi a zuciyar Mu’azzam.. Ta saki murmushi mai sanyi tana biyeda Assad..
Wane irin duba kurum Mu’azzam ke aika mata, kallo guda zaka masa ka fahimci zuciyarsa a tsananin b’ace take, daga wannan sai wannan “Are you out of your mind..? Have you lost it..?! Kin kuwa San mai kikazo kika aikata a nan Safeenah.. Kinsan inane nan wajen kuwa.. Kinsan wa kikayi attacking da haukarki..?!”
Da tsananin mamaki Feenah ke dubansa wai tasan wa tayi attacking Wato ta wancan shegiyar yake bama ta ita ba.. Watau budurwarsa yake defending.. Ita kuma tayi laifi since she attacked his girlfriend..
Cikin muryar kuka take furta “Yes. Yes na San abinda na aikata.. kuma nasan wacce nayi attacking she’s nothing but your mistress wacce kake cin amanan aurenmu da Ita, kak’i na tare a GIDANA dik sabida Ita...”
“Feeeenahh..!” Ya daka mata wane irin tsawa had’ida d’ago hannunsa kaman zai kwad’a mata mari.. A hankali kuma ya sauk’e hannunsa nasa ba tareda ya mareta ba, yaci gaba da dubanta zuciyarsa ba masa zogi..
Cikin kuka Safeenah ke fad’in “Go ahead and hit me, nasan baka mance a k’ofar ofishinku muke ba.. Hakan zai zama hujjan cewa kaid’in maci amana ne kana cin amanata da wancan ‘yariskar so called Colleague d’in taka...!”
Cikin sauri Assad yabi bayansa dan yasan komai ka iya faruwa tsakanin Mu’azzam da Chief Inspector.
Hankali tashe Assad ke k’ok’arin taresa ko kula Assad baiba har saida ya daki k’ofan Office d’in Chief..
Chief na cikin waya yana kwance cikin kujerarsa mai juyawa sai ganin Mu’azzam yai akansa yana sakin huci kaman wani mayuwancin zaki..
Babu shiri Chief ya katse wayar da yake yana duban Mu’azzam da tsananin mamaki
“How dare you barge into my office.. Who do you think you are..!” Cikin tsananin b’acin rai Chief yake maganar yana duban Mu’azzam dake tsaye gabansa idanunsa babu alamun tsoro..
Lokaci guda Mu’azzam ya d’ago Sketch d’in yana nunama Chief “Do you still have any reason to depend this criminal..?!”
Ko ba’a fad’a maka ba tsoro ya bayyana a fuskar Chief Inspector amma Sai ya dake yace “Kai k’aramin maras kunya. Kasan da wanda kake magana.. Naga irinka dubu kuma na gama dasu..”
Baikai aya ba Mu’azzam ya katsesa da fad’in “Bakaga irina ba kuma kafin kaga irina sai na tabbatar na gama dakai..”
Wannan karon murmushi Chief yai yace “Mind your language boy.. Bakada hujjan cewa na kare mai laifi domin kuwa dani da kai bamu San wanene Danger bamusan he’s connected to crime d’in nan ba sai yanzu...” Ya murmusa kad’an kafin yace “Har yanzu kaid’in yaro ne a gidan nan.. Har yanzu bakasan yanda Al’amara ke gudana a gida irin wannan ba.. You’re lucky, you’re from well known and respective family, I should’ve thrown you out cikin k’ask’anci . Now, get out of my office befor you lose everything .. Including your career as a police officer..!” Ya k’arashe muguwar murmushin saman fuskarsa..
Daidai lokacin Assad ya shigo a rud’e yana neman afuwan Chief on behalf of friend’s behavior..
Mu’azzam kaw har lokacin huci kurum yake yana duban Chief Inspector da idanunsa da tuni sun gama rinewa..
Chief ya dubi Assad d’in yace “Take him out.. Fitar dashi daga nan..!”
“Don’t touch me.. Don’t you dare touch me..!” Mu’azzam yai kashedi ma Assad kafin ya dubi Chief yace “Wata rana zamu had’u..! Alk’awari ne..!” Daga haka juyawa yai ya fice zuciyarsa na masa tsananin k’una..
Assad zai magana Mu’azzam ya d’aga masa hannu alamun dakatarwa “Not now Assad.!”
Fuzar da fuci kurum Assad yai kafin yabi bayan Mu’azzam d’in...
Su duka hud’in suna tsartsaye sunyi carko carko.. Suna kuma duban hoton Danger da ya bayyana cikin sketch d’in..
Assad ya nusa yace “What do we do now.. Danger must be in a hide tinda yasan dole za’a nemesa... Bazai tab’a zama nan kusa ba.. Allah Sa ma bai gudu ya bar gari ba..”
Yusuf yace “Ba Lallai Danger yasan ana nemansa ba, so ba lallai ace tsakanin jiya zuwa yau ya gudu ba..”
Muryar Mu’azzam suka sinkayo yana fad’in “We will track him down before yayi making move.. I know by now informer d’insa ya sanar dashi muna nemansa..!”
Gaba d’aya suka jinjina kai..
“Zamu fita yanzun nan zamuje unguwarsu Danger, but zamu fita ne a shirye dan nasan wannan area d’in territory d’insa ne komai ka iya faruwa..”
Suka jinjina kai suna amsawa.. Tuni ko Wannen su ya soma shirya weapon d’insa..
Maleeka ta d’an saci kallonsu yayinda suke ci gaba da tattaunawar yanda zasu tunk’ari al’amarin.. A hankali ta silale ta fice daga Ofishin gaba d’aya sai sauri take waya manne kunnenta tana faman waige waige..
A haka take gangarowa har ta d’anyi k’asa kad’an daga Building d’in nasu still tana ‘yan waige waige tana amsa waya..
Safeenah da k’arasowar motarsu wajen kenan Ta hangi Maleeka tsaye waya mak’ale kunnenta...
Wani irin wawan birki ta taka saida Meema dake zaune kujerar mai zaman banza ta saki ihu.
Hakan yayi daidai da k’aran da Umman Sadiya Ta saki wacce tayar Mota guda tabi mata kan k’afarta dan dama tin fitowarsu suke tsaye wajen suna neman abin hawa.. Umma ta sunkuya tana kame k’afarta dake mata zogi Sadiya na mata sannu..
D’agowa Sadiya tai tana jiran tagafitowar maras mutuncin matuk’in motar nan da yabi mata kan k’afar mahaifiya..
Wasu ‘yanmata ne ‘yangayun gaske guda biyu ta gansu Sun fito.. D’ayar fad’i take “Meema ki bud’e backseat ki d’auko.. Kiyi sauri mu k’arasa muci uwarta wllhi itace.. Bazan tab’a mance munin fuskarta ba..!”
Safeenah Batakai aya ba taji an rik’ota, ta juyo da mamaki tana duban wacce ta rik’eta.. Saida gabanta yayi wani irin fad’uwa da ganin kyakkyawar yarinyar data rik’ota tana sakin huci..
“Baiwar Allah baki gani ne kika bige min mahaifiya..?”
Sadiya tace tana duban Safeenar..
Wani irin wualak’antaccen kallo Safeenah da Meema suka raka Su Sadiya dashi kafin Meema tace “An bige ku d’in, ku makafi ne zaku tsaya bakin kwalta.. Ko kuma kurame ne ku da bazakuji sautin mota na zuwa ba..!”
Safeenah Ta finciki hannunta tana fad’in “Ke kika tsaya biyesu Meema, Ai shi Talaka dik yanda yaga mai kud’I hassada dashi yake.. K’iris yake jira ya hau d’aura masa laifi.. Muje kafin wancan shegiyar Ta tsere mana..”
Suka nufi d’aya length d’in cikin sauri yanda Maleeka take..
Sady tai kaman zatabi bayansu Umma ta rik’ota tana fad’in “K’yalesu Sadiya muji da rikicin dake kanmu bana fata mu kuma shiga wani fitinan..”
Sady tace “Amma Umma baki ganin abinda suka mana.”
Umma ta katseta da fad’in “K’yalesu Sadiya, ni mu samu mu bar wajen nan ma..” Ta k’arashe tana mai jan k’afar nata da k’yar Sadiya na mata sannu..
Maleeka tana tsaye taji an fincikota an fuzge wayar hannunta anyi jifa dashi had’ida kwasheta da wane irin mari mai walk’iya...
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*09*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Dafe da k’unci Maleeka ke dubansu da tsananin mamaki “Lafiya su waye ku..?”
Cikin azama Meema ta b’arke Babban roll d’in sanitary pad dake rik’e hannunta, kan kace mai sun shiga jifan fuskar Maleeka dashi.
Maleeka ta duk’a tana kare fuskarta da hannuwanta tana kuma tambayarsu su waye su mai ta masu..
Meema ta kuma jefa mata a fuska tana fad’in “Kinji Munafuka Adda Feenah tambaya ma take su waye mu.. Toh uwarki ne mu, ‘yar iska kawartuwa mai bin mazan mutane.”
Safeenah ta cab’i zancen da fad’in “Gashi nan kece matsiyaciya mai jiran namiji ya mata hidima, ki tattara duka.. Idan shi guda d’aya Yayi niyyan baki toh ga roll an baki.. Matsiyaciyar banza sauran kwalta..”
A hankali Meema ta soma jada baya sakamakon hango su Mu’azzam da tai sun fito daga building d’in.. Meema ta aune a guje ta nufi mota, tana bud’e marfin motar ta shige backseat.. Yanda ake aje k’afafu a wajen ta kwanta tai flat yanda babu mai iya hangota..
Safeenah kaw ta yanda take shiga bata nan take fita ba Sai jifan Maleeka take da sanitary pads tana kwashe mata albarka.. Mutane dake shigewa jefi jefi sai kallonsu suke da tsananin mamaki..
Assad ne ya soma hangosu.. Babu shiri ya tab’a Mu’azzam yace “Ai gacen Officer Maleeka.. But wait what’s going on..? Itada wacece..?”
Daidai lokacin Mu’azzam ya juyo, Assad na furta “Kaman Safeenah ce fah.. Mai take a nan..?”
Cikin sassarfa suka nufo yanda su Safeenah suke.. Da tsananin mamaki kurum Mu’azzam ke dubanta, bai zaici Safeenah zatayi abu makamancin haka ba..
“Safeenah.!!” Ya kirawo sunanta cikin tsananin b’acin rai
Cak ta tsaya ta dena abinda take.. Mu’azzam ya tsareta da idanunsa da suka kuma rikid’ewa zuwa ja, dama ransa a b’ace yake dan har ya kamo Danger Chief yasa ya sake shi gashi yanzu ya tabbata Danger nada alak’a da crime d’in da yake bincike..
Kallon wajen yake da mamaki, Wato abinda Safeenah ta gani cikin aljihunsa shine ta biyo Maleeka har Office taci mutuncinta dashi, watau a haukan Safeenah Maleeka budurwarsa ce.. Muryar Maleeka ne cikin kuka ya katse masa tinanin nasa “Sir, wllhi ni bansan mai na mata ba.. I don’t even know her, kawai gani nayi Ta soma attacking d’ina..”
Assad ne ya tari Maleeka da fad’in “Kiyi hak’uri Maleeka let’s talk somewhere else.. Kiyi hak’uri please..”
Maleeka ta d’ago tana duban Mu’azzam dake ci gaba da tururi ga Safeenah tsaye gabansa sai faman huci itama take tana ture turen baki..
Assad ya tasa Maleeka gaba yana fad’in suje.. Bataso tafiyan ba taso taga yanda Mu’azzam zasu kwashe da matarsa.. Ta kula matar Mu’azzam ce wannan wacce akayi aurensu sati biyu da suka shige, dama an fad’a mata cuna masa ita kawai akayi Mu’azzam ba sonta yake ba, Lallai yau ta tabbatar da hakan. Wani irin sanyi mai gauraye da annashuwa ne suka gauraye Zuciyarta.. Watau matar Mu’azzam tana tinanin Ita d’in budurwarsa ce, aiko bazata tab’a losing hope akan Mu’azzam ba tinda har ta zamto babban threat ga matarsa irin haka.. Da wannan rashin hankalin matar tasa tsaf zata iya samun gurbi a zuciyar Mu’azzam.. Ta saki murmushi mai sanyi tana biyeda Assad..
Wane irin duba kurum Mu’azzam ke aika mata, kallo guda zaka masa ka fahimci zuciyarsa a tsananin b’ace take, daga wannan sai wannan “Are you out of your mind..? Have you lost it..?! Kin kuwa San mai kikazo kika aikata a nan Safeenah.. Kinsan inane nan wajen kuwa.. Kinsan wa kikayi attacking da haukarki..?!”
Da tsananin mamaki Feenah ke dubansa wai tasan wa tayi attacking Wato ta wancan shegiyar yake bama ta ita ba.. Watau budurwarsa yake defending.. Ita kuma tayi laifi since she attacked his girlfriend..
Cikin muryar kuka take furta “Yes. Yes na San abinda na aikata.. kuma nasan wacce nayi attacking she’s nothing but your mistress wacce kake cin amanan aurenmu da Ita, kak’i na tare a GIDANA dik sabida Ita...”
“Feeeenahh..!” Ya daka mata wane irin tsawa had’ida d’ago hannunsa kaman zai kwad’a mata mari.. A hankali kuma ya sauk’e hannunsa nasa ba tareda ya mareta ba, yaci gaba da dubanta zuciyarsa ba masa zogi..
Cikin kuka Safeenah ke fad’in “Go ahead and hit me, nasan baka mance a k’ofar ofishinku muke ba.. Hakan zai zama hujjan cewa kaid’in maci amana ne kana cin amanata da wancan ‘yariskar so called Colleague d’in taka...!”