Sashe 17
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Assad yai yace “I don’t think Chief Jaja zai aikata wani abu mai kama da haka sabida idan baka mance ba kafin Chief yasan da labarin anyi sketching fuskar Danger a matsayin Uncle d’in Sagir saida ka nufi Office d’insa ka sanar dashi.. Da ace yau ne Danger yasan da labarin an zana fuskarsa a matsayin Uncle d’in Sagir da mun samu wani trace ko alamun cewa yau ne ya gudu.. At least da mun samu mutane a majalisar.. Amma bamu samu trace ko wani alama na hakan ba.. It’s possible Danger yana cikin shirinsa tintini.. Ba Lallai ya kasance yanada agent a CID ba..”
K’urama waje guda idanu Mu’azzam yai yana nazari.. A hankali ya soma girgiza kai “No Assad.. Those people are smart, ‘Yanta’adda k’wararru bazasu bar wani trace ko alama ba.. I’m positive akwai snitch a department d’inmu..”
Assad ya d’an nusa kafin yace “Who do you have in mind..?”
“Mutum d’aya ne kuma ba kowa bane face Chief Jaja.” Ya fad’i yana duban Assad d’in.
“Be careful who you’re up against.. Kabi komai a sannu Mu’azzam har ka gano bakin zaren komai.. Ba komai bane da ya bayyana maka zai zamto gaskiya.. Nasan kasan da hakan..” Assad ya fad’i yana duban abokin nasa..
Fuzar da huci Mu’azzam yayi kafin yace “I trust my team members, you’re my best friend, Yusuf ma amintaccenmu ne.. Sannan Maleeka..”
Assad ya ida maganar da fad’in “Maleeka you’re her all time crush.. Muna tare da ita tin a police Academy.. And I guarantee you wannan yarinyar babu abinda take buri face taga Tayi abinda zai burgeka Ta samu karb’uwa wajenka.. She’ll never betray you. Inada guarantee akanta. She loves you so much..”
Mu’azzam ya d’an fuzar da fuci kad’an yana duban Yusuf da Maleeka daketa k’ok’arin neman trace na Danger dik yanda ya shiga ya fita.. A hankali yace “We’ve one option idan munaso mu kamo Danger da accomplices d’insa..”
Assad ya dubesa yace “Wani option kenan..?”
“The girl..” Ya fad’i yana duban Assad kafin yaci gaba da fad’in “Through her muka San cewa Danger nada saka hannu a crime d’in nan.. I believe through her zamu samo yanda Danger yake..”
“Kaman yaya.? According to her statement ita kanta da family d’inta basusan waye Danger ba.. Ta yaya zata samo mana yanda yake..?” Assad yace yana duban Mu’azzam d’in.
Murmusawa kad’an yayi kafin yace “Kana magana kaman ba ma’aikacin bincike ba.. Ai yanzu na tabbata Danger bazai bar family d’inta ba muddin yasan ansan wani abu akansa.. Nasan dole zai hanasu magana ma ‘yansanda ta ko wacce hanya.. Sannan zai saka masu ido idan yaga jami’an tsaro na zarya wajensu.. Zai making move d’insa.. Mu kuma zamu buga wasan idan yayi losing.. Caraf sai kama wuyarsa..”
Assad ya jinjina kai yace alamun gamsuwa sai kuma yace “But don’t you think rayuwar yarinyar da ahalinta zai zamto yana cikin garari..?”
Mu’azzam ya jinina Kai yace “Already cikin had’ari suke tinda sukai involving kansu da wannan criminal d’in.. They are in this mess already..”
Assad ya d’an nusa kafin Mu’azzam yace su tafi gidansu yarinyar.
Assad ne yai alama masu Maleeka da Yusuf yace Su k’araso su tafi..
**
Har lokacin Sadiya kife kanta yake kan gawan mahaifinta da tuni an gama shiryasa cikin suturarsa na gidan gaskiya.. kuka take da duka zuciyarta, cikin kuka take furta “Abba Maiyasa zasu maka haka.? Su waye suka maka haka..? Abba Dan Allah ka tashi.. Kar ka tafi ka barmu.. Abbbaaaa..!” Ta k’arashe cikin tsananin kuka
Tinda suka doso layin ya tsaya yana duban cincirindon mutanen dake tsartsaye k’ofar gidan nasu ana jajanta lamarin..
Wani mutumi da hatsarin ya faru gabansa yaci gaba da bama sauran labari “Ai mai mashin ne ya fara bugesa, kansa na rufe cikin rawani.. Malam Ibrahim tareda yaransa guda biyu yake tafiya sai mai mashin d’in ya bigesa ya cillasa wani gefen.. Yana cillasa gefe guda mai mota yabi kansa.. Wllhi abun abin tashin hankali kaidai..”
Mu’azzam kam bai iya sauraron tattaunawarsu ba Yusuf da Assad ne sukai sallama kafin suka ja mutumin gefe suna tambayarsa yai masu bayani dalla dalla yanda had’arin ya kasance.. Shikam Mu’azzam tuni ya kutsa Kai cikin gidan Dan tabbatar ma idanunsa abinda ke faruwa..
Cak ya tsaya yana dubanta yanda ta kifa kanta saman k’irjin mahaifinta tana kuka mai ban tausayi ga mahaifiyarta gefe rungume da k’annenta suma duk kukan suke.
Cikin sautin kuka Sady taci gaba da fad’in “Abba Dan Allah ka tashi kace ka yafe mun.. Nasan nayi maka laifuka da dama Abba, Abba dan Allah ka tashi kar ka tafi ka barmu bazamu iya ba.. Maiyasa suka kad’e mun kai Abba na..”
Muryarsa ne ya katseta da da fad’in “Because they believe your father knows something shiyasa suka kashe shi Dan kar ya tona masu asiri..!”
Cak Ta tsaya da kukan nata sakamako sinkayo muryarsa da Tai... Ta d’ago rinannun idanunta ta sauk’esu tsaf akansa, zuciyarta na mata wani irin zogi take dubansa.. Take tsanansa ya ninku cikin zuciyarta..
Cikin kuka ta mik’e tana furta “This is all your fault.. Ku kuka jawo aka kashe mana Abbanmu.. Maiyasa bazaku k’yalemu ba.. Bamu San mutumin da kuke nema ba, bamu San komai akansa ba.. Mun sanar daku Iyakacin abinda muka sani.. Mahaifina Bai cancanci a kashesa mercilessly irin haka ba... Just leave us alone already.. Ka tafi Dan Allah.. Kuje can ku nemi criminals d’in da kuke nema.. And leave us in peace..!” Ta k’arashe tana mai had’e hannayenta biyu waje guda alamun rok’o had’ida zubewa saman gwiwoyinta..
Dubanta kurum yake yana jin zuciyarsa na masa wani irin k’una.. Yana duban yanda hawayenta ke zubowa da sautin kukanta had’ida rok’onsa da takeyi ya tafi ya k’yalesu suji da rashin mahaifinsu da sukai.. A hankali ya soma jada baya still idanunsa akanta..
Cikin sauri Mu’azzam ya juya ya fice daga gidan gaba d’aya yana duban yanda Sadiya ta zube saman gwiwoyinta tana kuka mai tab’a zuciya..
Har ya shige su Assad dake faman tattare bayanai daga wajen mutanen unguwa basu lura dashi ba.. Sautin tashin motarsu kurum sukaji.. Assad ya saki baki yana dubansa.. Maleeka dake faman rubuce rubuce itama baki sake take duban Mu’azzam d’in..
A yanda sukaga ya kwashi motar sunsan komai ka iya faruwa..
Assad ya girgiza kai yana mai furta “Oh no..! Mu’azzam mai kake shirin aikatawa..?”
**
Ko parking mai kyau bai ida ba ya nufi ofishin Chief Inspector Jaja... A lobby ya iske Chief tareda wasu abokan aikinsu ‘yansanda suna tatauna wani matsalan.. Mu’azzam duban Chief kurum yake yana kuma sinkayo kukan yarinyar da yanda take fad’in an kashe mata mahaifi ba tareda ya aikata laifin komai ba.. Fuskar yarinyar yake hangowa cikin idanunsa yanda Ta duk’a tana zuban hawaye.. Baiyi wata wata ba yana isowa ya dunk’ule hannunsa yakai ma Chief naushi maiji da lafiya a Hanci wanda saida takai Chief har k’asa..
Ba Chief da yaji sauk’an naushin kaman a mafarki ba harta sauran ‘yansandan saida suka tsaya suna duban Mu’azzam cikin tsananin Shock Dan kaf d’insu babu wanda yaga zuwan Mu’azzam sauk’an naushin kawai suka gani..
Mu’azzam ya cakumo wuyan Chief yana fad’in “Lets end it now.. You better tell me waye kake karewa.. Ka sanar dani Manzo Jaja.. Waye kake karewa.. Do you know how many innocent lives are stake here.. Shin kasan rayuka nawa ka jefa cikin garari da gurb’atacciyan zuciyarka.. Tell me.. Tell me Chief Manzo Jaja..!!” Yanda yake jijjiga Chief dole ya baka tsoro..
Wane irin fincika Chief yai yana tsananin huci yayinda sauran ‘yansandan suka janye Mu’azzam daga jikin Chief..
Huci kurum Chief yake yana nuna Mu’azzam da ‘yar yatsa ga bakinsa dake fidda jini sabida naushin da Mu’azzam d’in yai masa “You’ll pay.. You’ll pay for this..!” Ya k’arashe yana mai shigewa ofishinsa cikin tsananin b’acin rai..
Daidai lokacin su Assad suka k’araso duk a birkice suke..
Yanda Assad ya hango Mu’azzam yasan mai aukuwa ya auku.. Saurin k’arasawa yai wajen abokin nasa dake faman yarfe hannuna wanda ya naushi Chief dashi.. Hannun Mu’azzam d’in kawai Assad ya duba da yanda yake yarfe hannun nasa ya fahimci cewa mai aukuwa ta auku..
Assad ya k’araso yana duban yanayin mutanen dake wajen yanda kowa yasha jinin jikinsa..
Dafa Mu’azzam d’in dake zaune saman kujera ya kifa kansa k’asa yai.. Ko baa ce kasan zuciyarsa ce ke tafarfasa
“Can you tell me now.. What really happened here..?” Baikai ga basa amsa ba sukaga ana mik’owa Mu’azzam d’in Doguwar takarda cikin envelop.. Saida ya dubi mai mik’o masa takardan kafin yasa hannu ya amsa takardan ba tareda ya amsa tambayar Assad ba..
Lokaci guda ya shiga warwareta.. A hankali ya lumshe idanunsa Dan yasan za’a rina haka.. Suspending d’insa akayi har na tsawon makonni biyu... Cikin sauri Assad ya amshi takardan yana karantawa..
Dafe kansa kurum Assad yai yana mai fuzar da fuci..
Cikin tsananin b’acin rai Assad ya soma fad’in “You see.. Kaga abinda nake fad’a maka Mu’azzam.. You never listen.. You’re so stubborn Mu’azzam.. Yanzu ga irinta nan kaja an dakatar dakai..”
Bai k’arasa sauraron Assad ba ya mik’e yai ficewarsa waje.. Assad ya biyo bayansa yana ci gaba da magana cikin tsananin b’acin rai..
Idan jacket d’in dake jikinsa ya amsa shima zai amsa.. Yanda motarsa ke ajiye ya isa ya shige, har lokacin Assad na masa magana yana k’ok’arin dakatar dashi suje dubawa Chief hak’uri ko rage masa tsawon wa’adin suspension d’in ne ayi amma ko ranka Assad baiba..
Tuni ya shige Mota ya fuzgeta.. Yana driving amma kukan yarinyar da rok’onsa da take su fice masu a rayuwa bai daina Yawo a kwanyarsa da dodon kunnuwarsa ba.. An kashe mata mahaifi dik akan binciken da yake na neman gaskiyar mutuwar ‘yaruwarsa.. A hankali ya lumshe idanunsa yana mai jin motar bayansa na danna masa horn.. Cikin sauri ya ware idanun nasa yana k’ok’arin saita kansa Dan k’iris ya rage baiyi causing accident ba..
Traffic ne ya tsaidasu, a daidai k’ofar wani kanti yake hango k’aton takardan Sanitary pad irin na advert d’in nan.. Lokaci guda ya tuna sanda Ta jefe shi da gidan abin.. Nan yake tina farkon had’uwarsu.. Yayi nisa duniyar tunani yaji ana masa horn motar bayansu alamun traffic light ya basu koren wuta..
K’urama waje guda idanu Mu’azzam yai yana nazari.. A hankali ya soma girgiza kai “No Assad.. Those people are smart, ‘Yanta’adda k’wararru bazasu bar wani trace ko alama ba.. I’m positive akwai snitch a department d’inmu..”
Assad ya d’an nusa kafin yace “Who do you have in mind..?”
“Mutum d’aya ne kuma ba kowa bane face Chief Jaja.” Ya fad’i yana duban Assad d’in.
“Be careful who you’re up against.. Kabi komai a sannu Mu’azzam har ka gano bakin zaren komai.. Ba komai bane da ya bayyana maka zai zamto gaskiya.. Nasan kasan da hakan..” Assad ya fad’i yana duban abokin nasa..
Fuzar da huci Mu’azzam yayi kafin yace “I trust my team members, you’re my best friend, Yusuf ma amintaccenmu ne.. Sannan Maleeka..”
Assad ya ida maganar da fad’in “Maleeka you’re her all time crush.. Muna tare da ita tin a police Academy.. And I guarantee you wannan yarinyar babu abinda take buri face taga Tayi abinda zai burgeka Ta samu karb’uwa wajenka.. She’ll never betray you. Inada guarantee akanta. She loves you so much..”
Mu’azzam ya d’an fuzar da fuci kad’an yana duban Yusuf da Maleeka daketa k’ok’arin neman trace na Danger dik yanda ya shiga ya fita.. A hankali yace “We’ve one option idan munaso mu kamo Danger da accomplices d’insa..”
Assad ya dubesa yace “Wani option kenan..?”
“The girl..” Ya fad’i yana duban Assad kafin yaci gaba da fad’in “Through her muka San cewa Danger nada saka hannu a crime d’in nan.. I believe through her zamu samo yanda Danger yake..”
“Kaman yaya.? According to her statement ita kanta da family d’inta basusan waye Danger ba.. Ta yaya zata samo mana yanda yake..?” Assad yace yana duban Mu’azzam d’in.
Murmusawa kad’an yayi kafin yace “Kana magana kaman ba ma’aikacin bincike ba.. Ai yanzu na tabbata Danger bazai bar family d’inta ba muddin yasan ansan wani abu akansa.. Nasan dole zai hanasu magana ma ‘yansanda ta ko wacce hanya.. Sannan zai saka masu ido idan yaga jami’an tsaro na zarya wajensu.. Zai making move d’insa.. Mu kuma zamu buga wasan idan yayi losing.. Caraf sai kama wuyarsa..”
Assad ya jinjina kai yace alamun gamsuwa sai kuma yace “But don’t you think rayuwar yarinyar da ahalinta zai zamto yana cikin garari..?”
Mu’azzam ya jinina Kai yace “Already cikin had’ari suke tinda sukai involving kansu da wannan criminal d’in.. They are in this mess already..”
Assad ya d’an nusa kafin Mu’azzam yace su tafi gidansu yarinyar.
Assad ne yai alama masu Maleeka da Yusuf yace Su k’araso su tafi..
**
Har lokacin Sadiya kife kanta yake kan gawan mahaifinta da tuni an gama shiryasa cikin suturarsa na gidan gaskiya.. kuka take da duka zuciyarta, cikin kuka take furta “Abba Maiyasa zasu maka haka.? Su waye suka maka haka..? Abba Dan Allah ka tashi.. Kar ka tafi ka barmu.. Abbbaaaa..!” Ta k’arashe cikin tsananin kuka
Tinda suka doso layin ya tsaya yana duban cincirindon mutanen dake tsartsaye k’ofar gidan nasu ana jajanta lamarin..
Wani mutumi da hatsarin ya faru gabansa yaci gaba da bama sauran labari “Ai mai mashin ne ya fara bugesa, kansa na rufe cikin rawani.. Malam Ibrahim tareda yaransa guda biyu yake tafiya sai mai mashin d’in ya bigesa ya cillasa wani gefen.. Yana cillasa gefe guda mai mota yabi kansa.. Wllhi abun abin tashin hankali kaidai..”
Mu’azzam kam bai iya sauraron tattaunawarsu ba Yusuf da Assad ne sukai sallama kafin suka ja mutumin gefe suna tambayarsa yai masu bayani dalla dalla yanda had’arin ya kasance.. Shikam Mu’azzam tuni ya kutsa Kai cikin gidan Dan tabbatar ma idanunsa abinda ke faruwa..
Cak ya tsaya yana dubanta yanda ta kifa kanta saman k’irjin mahaifinta tana kuka mai ban tausayi ga mahaifiyarta gefe rungume da k’annenta suma duk kukan suke.
Cikin sautin kuka Sady taci gaba da fad’in “Abba Dan Allah ka tashi kace ka yafe mun.. Nasan nayi maka laifuka da dama Abba, Abba dan Allah ka tashi kar ka tafi ka barmu bazamu iya ba.. Maiyasa suka kad’e mun kai Abba na..”
Muryarsa ne ya katseta da da fad’in “Because they believe your father knows something shiyasa suka kashe shi Dan kar ya tona masu asiri..!”
Cak Ta tsaya da kukan nata sakamako sinkayo muryarsa da Tai... Ta d’ago rinannun idanunta ta sauk’esu tsaf akansa, zuciyarta na mata wani irin zogi take dubansa.. Take tsanansa ya ninku cikin zuciyarta..
Cikin kuka ta mik’e tana furta “This is all your fault.. Ku kuka jawo aka kashe mana Abbanmu.. Maiyasa bazaku k’yalemu ba.. Bamu San mutumin da kuke nema ba, bamu San komai akansa ba.. Mun sanar daku Iyakacin abinda muka sani.. Mahaifina Bai cancanci a kashesa mercilessly irin haka ba... Just leave us alone already.. Ka tafi Dan Allah.. Kuje can ku nemi criminals d’in da kuke nema.. And leave us in peace..!” Ta k’arashe tana mai had’e hannayenta biyu waje guda alamun rok’o had’ida zubewa saman gwiwoyinta..
Dubanta kurum yake yana jin zuciyarsa na masa wani irin k’una.. Yana duban yanda hawayenta ke zubowa da sautin kukanta had’ida rok’onsa da takeyi ya tafi ya k’yalesu suji da rashin mahaifinsu da sukai.. A hankali ya soma jada baya still idanunsa akanta..
Cikin sauri Mu’azzam ya juya ya fice daga gidan gaba d’aya yana duban yanda Sadiya ta zube saman gwiwoyinta tana kuka mai tab’a zuciya..
Har ya shige su Assad dake faman tattare bayanai daga wajen mutanen unguwa basu lura dashi ba.. Sautin tashin motarsu kurum sukaji.. Assad ya saki baki yana dubansa.. Maleeka dake faman rubuce rubuce itama baki sake take duban Mu’azzam d’in..
A yanda sukaga ya kwashi motar sunsan komai ka iya faruwa..
Assad ya girgiza kai yana mai furta “Oh no..! Mu’azzam mai kake shirin aikatawa..?”
**
Ko parking mai kyau bai ida ba ya nufi ofishin Chief Inspector Jaja... A lobby ya iske Chief tareda wasu abokan aikinsu ‘yansanda suna tatauna wani matsalan.. Mu’azzam duban Chief kurum yake yana kuma sinkayo kukan yarinyar da yanda take fad’in an kashe mata mahaifi ba tareda ya aikata laifin komai ba.. Fuskar yarinyar yake hangowa cikin idanunsa yanda Ta duk’a tana zuban hawaye.. Baiyi wata wata ba yana isowa ya dunk’ule hannunsa yakai ma Chief naushi maiji da lafiya a Hanci wanda saida takai Chief har k’asa..
Ba Chief da yaji sauk’an naushin kaman a mafarki ba harta sauran ‘yansandan saida suka tsaya suna duban Mu’azzam cikin tsananin Shock Dan kaf d’insu babu wanda yaga zuwan Mu’azzam sauk’an naushin kawai suka gani..
Mu’azzam ya cakumo wuyan Chief yana fad’in “Lets end it now.. You better tell me waye kake karewa.. Ka sanar dani Manzo Jaja.. Waye kake karewa.. Do you know how many innocent lives are stake here.. Shin kasan rayuka nawa ka jefa cikin garari da gurb’atacciyan zuciyarka.. Tell me.. Tell me Chief Manzo Jaja..!!” Yanda yake jijjiga Chief dole ya baka tsoro..
Wane irin fincika Chief yai yana tsananin huci yayinda sauran ‘yansandan suka janye Mu’azzam daga jikin Chief..
Huci kurum Chief yake yana nuna Mu’azzam da ‘yar yatsa ga bakinsa dake fidda jini sabida naushin da Mu’azzam d’in yai masa “You’ll pay.. You’ll pay for this..!” Ya k’arashe yana mai shigewa ofishinsa cikin tsananin b’acin rai..
Daidai lokacin su Assad suka k’araso duk a birkice suke..
Yanda Assad ya hango Mu’azzam yasan mai aukuwa ya auku.. Saurin k’arasawa yai wajen abokin nasa dake faman yarfe hannuna wanda ya naushi Chief dashi.. Hannun Mu’azzam d’in kawai Assad ya duba da yanda yake yarfe hannun nasa ya fahimci cewa mai aukuwa ta auku..
Assad ya k’araso yana duban yanayin mutanen dake wajen yanda kowa yasha jinin jikinsa..
Dafa Mu’azzam d’in dake zaune saman kujera ya kifa kansa k’asa yai.. Ko baa ce kasan zuciyarsa ce ke tafarfasa
“Can you tell me now.. What really happened here..?” Baikai ga basa amsa ba sukaga ana mik’owa Mu’azzam d’in Doguwar takarda cikin envelop.. Saida ya dubi mai mik’o masa takardan kafin yasa hannu ya amsa takardan ba tareda ya amsa tambayar Assad ba..
Lokaci guda ya shiga warwareta.. A hankali ya lumshe idanunsa Dan yasan za’a rina haka.. Suspending d’insa akayi har na tsawon makonni biyu... Cikin sauri Assad ya amshi takardan yana karantawa..
Dafe kansa kurum Assad yai yana mai fuzar da fuci..
Cikin tsananin b’acin rai Assad ya soma fad’in “You see.. Kaga abinda nake fad’a maka Mu’azzam.. You never listen.. You’re so stubborn Mu’azzam.. Yanzu ga irinta nan kaja an dakatar dakai..”
Bai k’arasa sauraron Assad ba ya mik’e yai ficewarsa waje.. Assad ya biyo bayansa yana ci gaba da magana cikin tsananin b’acin rai..
Idan jacket d’in dake jikinsa ya amsa shima zai amsa.. Yanda motarsa ke ajiye ya isa ya shige, har lokacin Assad na masa magana yana k’ok’arin dakatar dashi suje dubawa Chief hak’uri ko rage masa tsawon wa’adin suspension d’in ne ayi amma ko ranka Assad baiba..
Tuni ya shige Mota ya fuzgeta.. Yana driving amma kukan yarinyar da rok’onsa da take su fice masu a rayuwa bai daina Yawo a kwanyarsa da dodon kunnuwarsa ba.. An kashe mata mahaifi dik akan binciken da yake na neman gaskiyar mutuwar ‘yaruwarsa.. A hankali ya lumshe idanunsa yana mai jin motar bayansa na danna masa horn.. Cikin sauri ya ware idanun nasa yana k’ok’arin saita kansa Dan k’iris ya rage baiyi causing accident ba..
Traffic ne ya tsaidasu, a daidai k’ofar wani kanti yake hango k’aton takardan Sanitary pad irin na advert d’in nan.. Lokaci guda ya tuna sanda Ta jefe shi da gidan abin.. Nan yake tina farkon had’uwarsu.. Yayi nisa duniyar tunani yaji ana masa horn motar bayansu alamun traffic light ya basu koren wuta..