Sashe 122
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sadiya kaw tana jin ya juya bai shigo ba taji kuka na zuwa mata gadan gadan, tana jin sanda ya bud’e d’akinsa ya shige. A yanda tasan shi ko bacci tai a nata d’akin baya tab’a yarda su raba shimfid’a, koda ace bacci ya d’auketa a d’akinta wasu lokutan farkawa take ta tsinci kanta a nasa d’akin ya sureta ya kaita can, wasu lokutan kuma shima kwanciyar yake a nata d’akin ta kula baya tab’a yarda suyi bacci ba cikin jikin juna ba.. Itama d’in zata iya cewa ta riga ta saba da hakan bacci cikin jikin mijinta, ya sabar mata da hakan yabi jikinta..Ta kuma jin wani rauni na taso mata can k’asar zuciyarta. Yanzu idan Safeenah ta dawo dole komai rabawa zasuyi.. Wai dama haka kishi yake.. Haka matan da mazajensu sukeji idan mazan suka kuma kawo wata mace.. Lallai duk macen da mijinta ya k’aro mata aure ta kumayi tawakkali ta amshi k’addararta a yanda yazo mata wann matar ta cika a kirata jarumar mata.. Kuma ta cika a nad’a mata Kambi na sarautar mata.. Tabbas zuciya rauni ne da ita mai juriya da tsoron Allah ne kawai Zata iya jure wann rad’ad’i na kishin.. Allah ka iyar mana abinda bazamu iya ba ka bamu abokan zama na k’warai idan ka k’addara hakan a garemu. Ta kuma lumshe idanunta a hankali siraran hawaye suka gangaro mata.
Mu’azzam kaw koda ya shigo ya hangeta tana bacci sai bai tasheta ba dan dama ba kwanciya zaiyi ba, research yake so ya d’an gudanar kan K’ungiya masu safaran mutane da yaci karo dashi cikin bincikensa. Dan haka tuni ya bud’e computer d’insa bayan ya ida shirinsa na bacci ya shiga bincike yana duba ko zai sami wani abu da zai nuna cewa an capke ‘yanta’addan a wancan lokacin maybe suna wani prison serving their sentences. Saidai duk iyakan binciken da zai bai samu labari mai kama da hakan ba.. Bacci b’arawo ne yai gaba da shi nan wajen.
**
A can b’angaren Safeenah kaw koda Mommy ta shigo ta taddata kafeta da idanu tai tana fad’in “Kar ki raina mun hankali Safeenah. Na Sani k’alau kike salon makirci ne kawai ya sanyaki kiran Mu’azzam...”
Safeenah Ta turo baki tace “Toh Mommy ya zanyi Ina son kasancewa da Uban D’a na.. Sai na zuba ido yana can yana cin soyayyarsa ni an barni da dakon yaro cikin jikina.. Mommy meye laifina Dan naso kasancewa da Uban d’a na..”
Mommy tace “Ke tafi can ki rufe mun baki.. Toh a haka ne zaki samu kulawarsa.? Aima saidai ki hau masa kai har kisa yaji baya marmarin cikin naki.. Ke barin Fad’a miki da wann hanyar da kika d’auko sam ba mai b’ullewa bace, bazaki samu kansa ba a haka.”
Safeenah tace “Tab ai wllhi Mommy yanzu na fara babu gudu babu jada baya sai na k’wato abinda yake nawa ne.. Kuma wann D’an cikin nawa shi zai taimaka min mu yak’i wancan shu’umar mu k’wato Babansa daga wajenta.. Idan kuma nai duk abinda zanyi bai working ba sai na sanar da Inne da Daddy nasan matuk’a suka San inada ciki dole a maida aurenmu da Mu’azzam.”
Mommy ta katseta da fad’in “Ashe ke shashasha ce lamba d’aya.. Banda Rashin wayo wayace miki ana sanar da samuwar k’aramin ciki haka gatse..? Idan kika sanar dasu yanzu sam bazasuyi d’okin cikin ba.. Amma idan kika bari suka fahimci haka sai kifi samun goyon bayansu da kulawarsu.. Koda wasa kar kiyi wann kuskuren..”
Feenah ta saki baki tana duban Mommy dan ita bataga mai zai hanasu farin ciki idan ta sanar dasu ba.
Mommy ta katseta da fad’in “Kina jina bazaki sanar dasu yanzu ba.. Ki bari akwai lokacin da na tanadar ma hakan.. Amma idan kika zab’i kiyi abinki ke kad’ai ni bazance komai ba Sai na zuba miki idanu kiyi duk yanda kike so.. Idan kikaje garin shashashancinki da haukarki kika salwantar da cikin kinga ai shikenan kin huta..”
Safeenah tai shiru tana sauraron Mommy.. Sai kuma ta jinjina kai tace “Shikenan Mommy bazan sanar dasu ba zan jira lokacin da Kikace d’in..”
“Yauwa yanzu naji batu.. Tashi muje ki kwanta ki huta..”
Babu musu Safeenah ta mik’e tabi bayan Mommy.
**
Washe gari ma sassafe ya fice Dan ko sallama bai samu sunyi ba Assad na jiransa akwai yanda zasuje sann yana so ya soma biyawa Prison wajen Yusuf kafin suje yanda zasuje da Assad d’in.
Koda Sadiya ta farka taga har ya fice Sabon tashin hankali ta shiga, ba d’abi’arsa bace fita bai mata sallama ba.. Ko sauri yake zai shigo ya manna mata kiss ya kuma mata sallama ya sanar da ita aiki na gaggawa ya taso masa.. Amma sai gashi yau ya fita kuma sam ita dai bataji alamun shigowarsa ba.. Mai hakan yake nufi..? Tai jigum abin na neman ya d’aga mata hankali cikin k’ank’anin lokaci. Taji kanta na wani irin sara mata ga daren jiya ba wani samun isasshen bacci tai ba, haka tai kusan kwana tana juyi. Kewan gida ne ya isheta.. Taji tana son taje taga Umma da ‘yanuwanta. Tai tunanin kiran layinsa sai kuma ta tuna jiya fah rejecting yai sann bai ko bi takanta ba har wann lokacin.. Jiki a sanyaye ta aje wayar nata ba tareda ta kirasa ba. Tai zaune a parlor kaman marainiya tana tinanin rayuwa da irin k’alubalen data fuskanta a rayuwa.. Shin wann ma wani sabon karatun ne..? Tambayar da zuciyarta tai mata. Kwanciya tai lak’was cikin kujera tana jin ko kitchen kaman bazata iya shiga ba a nan bacci b’arawo ya d’auketa abinka da wacce bata wani sami bacci daren da ya gabata ba.
**
Mu’azzam yai zaune yana jiran fitowar Yusuf a wajen da aka tanada domin ganawa sa prisoners.. Can ya hangosa ya nufo yanda yake wani ganduroba biye dashi.
Mu’azzam ya tsaresa da idanu yana dubansa yanda yake nufosa, a maimakon kayan ‘yansanda kayan prisoners ne jikinsa.. Ya d’an kauda fuskarsa kad’an yana jin wani abu na tokarin zuciyarsa.. Maiyasa abokinsa zaici amanarsa.. Maiyasa Yusuf..?
Daidai lokacin Yusuf ya k’araso gajeriyar murmushi saman fuskarsa, ya zauna a kujera mai kallon na Mu’azzam teburi ya raba tsakaninsu.
“Inspector, what brought you here this early..?” Yusuf ya tambaya yana d’an shafa hab’arsa kad’an idanunsa akan Mu’azzam d’in.
Mu’azzam ya kafesa da idanu yana dubansa, saida ya kwashi tsawon lokaci a haka har Yusuf ya soma gudura, ya saki murmushi yana ‘yan waige waige lokaci guda yana rage girman idanunsa kad’an “You shouldn’t been seen here Inspector.. You know this could be dangerous for me... Kar ka mance they have eyes everywhere.. Suna karantar duk wani movement d’ina..” Ya kuma duban Mu’azzam d’in yana sakin murmushi a hankali “I don’t want to get killed Inspector.. Nida munsan ya criminals suke gudanar da al’amaransu musamman a Prison.. They can easily eliminate me here.”
“Kayi magana idan baka so su kashe ka.. Ka fad’i duk abinda ka sani.. Na tabbata sentences d’inka bazai kai nasu ba.. Yusuf Maiyasa kake karesu.. Maiyasa ka zab’i ka biya laifinsu alhali su suna can suna ci gaba da b’arna.. Yusuf idan ka tab’a valuing aikin ka a matsayinka na jami’in tsaro zaka Fad’i gaskiya.. Yusuf wad’anda kake karewa bazasu tab’a k’yaleka ba koda kayi abinda suke so..” Ya d’anyi fasali yana dubansa Yusuf.. Su duka biyun duban juna suke, kafin Mu’azzam ya kuma daidaita zamansa yana fad’in “If you once valued our friendship zaka sanar dani abinda ka sani..”
Yasa hannu a aljihunsa ya ciro coin d’in Black African Team ya nunawa Yusuf yace “Tell me... What do you know about this..?”
Yusuf ya k’ura masa idanu yana kuma duban coin d’in kafin ya murmusa yace “Mai wann yake nufi..? Wann ai sisin kwabo ne..”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “Black Africa Team.. Mai ka sani gameda wann Syndicate d’in..?”
Yusuf ya murmusa kad’an yana shafa hab’arsa sai kuma yace “I don’t know.. Ban Sani ba Mu’azzam.. Bansan wani Syndicate mai wann sunan ba.”
Mu’azzam ya kuma jinjina kai yace “Human Trafficking Syndicate.. But it’s been long destroyed.. Danger is somehow connected to that Syndicate.. Idan har kana aiki ma Danger, I’m quite certain zaka iya sanin wani abu gameda Balck African Team..”
Yusuf ya d’an sosa kunnensa kad’an yana Murmusawa.
Mu’azzam ya kuma tsaresa da idanu yana fad’in “For all time sake Yusuf.. Please do what is right..” Ya k’arashe yana duban Yusuf d’in cikin yanayi na ban tausayi.
Jikin Yusuf ya d’anyi sanyi, Dan shi kansa cin amanan abokansa da yayi sosai abin ke masa ciwo.. Ya d’ago yana duban Mu’azzam ga lokacin komawansa ciki yayi Dan har ganduroba d’in ya k’araso yana jira suyi rounding up.
Yusuf ya mik’e Mu’azzam ma ya mik’e yana girgiza kai “Please Yusuf, do this for our friendship.”
Yusuf na murmushi yake duban Mu’azzam d’in, cikin k’arfin hali yake danne hawayen dake k’ok’arin ciko idanunsa “What Friendship are talking about Mu’azzam.. Abotan da na lalata.. Abotan da bai mana rana ba..? Abotan da ya rikid’a ya koma k’iyayya.. Wann abotan kake magana akai..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Bansan dalilinka na cin amananmu ba Yusuf amma na sani you are not like them.. Kai ba kaman su bane.. You still have good in you.. Kar kabi abinda zuciyarka ke fad’a maka.. Kabi abinda mind d’inka yake sanar dakai.. Expose them Yusuf.. Kar ka bari suyi amfani dakai..”
Yusuf ya murmusa kad’an kafin yace “I guess circumstance na rayuwa yakan iya jefa bawa cikin k’addaran da bai tab’a tsammanin zai tsinci kansa ciki ba.. It’s too late Mu’azzam.. Na riga da na makara.. Kaje Mu’azzam, I’ve faith in you.. I know you’ll bring them down.. Nasan zaka kamasu zaka cimmasu watarana.. Sabida ka d’auko hanya..” Ya d’anyi fasali yana rok’on Ganduroban ya k’ara masa mintoci kafin ya dubi Mu’azzam yaci gaba da fad’in “Zan fad’a maka wani abu guda d’aya.. Kaje ka nemo wanene BAT.. Idan ka cimma BAT ka samu kan K’umurcin da kaketa farauta..” Ya juya zai wuce Mu’azzam ya dakatar dashi da fad’in “Kana nufin Black African Team.. Shine BAT d’in..?”
Mu’azzam kaw koda ya shigo ya hangeta tana bacci sai bai tasheta ba dan dama ba kwanciya zaiyi ba, research yake so ya d’an gudanar kan K’ungiya masu safaran mutane da yaci karo dashi cikin bincikensa. Dan haka tuni ya bud’e computer d’insa bayan ya ida shirinsa na bacci ya shiga bincike yana duba ko zai sami wani abu da zai nuna cewa an capke ‘yanta’addan a wancan lokacin maybe suna wani prison serving their sentences. Saidai duk iyakan binciken da zai bai samu labari mai kama da hakan ba.. Bacci b’arawo ne yai gaba da shi nan wajen.
**
A can b’angaren Safeenah kaw koda Mommy ta shigo ta taddata kafeta da idanu tai tana fad’in “Kar ki raina mun hankali Safeenah. Na Sani k’alau kike salon makirci ne kawai ya sanyaki kiran Mu’azzam...”
Safeenah Ta turo baki tace “Toh Mommy ya zanyi Ina son kasancewa da Uban D’a na.. Sai na zuba ido yana can yana cin soyayyarsa ni an barni da dakon yaro cikin jikina.. Mommy meye laifina Dan naso kasancewa da Uban d’a na..”
Mommy tace “Ke tafi can ki rufe mun baki.. Toh a haka ne zaki samu kulawarsa.? Aima saidai ki hau masa kai har kisa yaji baya marmarin cikin naki.. Ke barin Fad’a miki da wann hanyar da kika d’auko sam ba mai b’ullewa bace, bazaki samu kansa ba a haka.”
Safeenah tace “Tab ai wllhi Mommy yanzu na fara babu gudu babu jada baya sai na k’wato abinda yake nawa ne.. Kuma wann D’an cikin nawa shi zai taimaka min mu yak’i wancan shu’umar mu k’wato Babansa daga wajenta.. Idan kuma nai duk abinda zanyi bai working ba sai na sanar da Inne da Daddy nasan matuk’a suka San inada ciki dole a maida aurenmu da Mu’azzam.”
Mommy ta katseta da fad’in “Ashe ke shashasha ce lamba d’aya.. Banda Rashin wayo wayace miki ana sanar da samuwar k’aramin ciki haka gatse..? Idan kika sanar dasu yanzu sam bazasuyi d’okin cikin ba.. Amma idan kika bari suka fahimci haka sai kifi samun goyon bayansu da kulawarsu.. Koda wasa kar kiyi wann kuskuren..”
Feenah ta saki baki tana duban Mommy dan ita bataga mai zai hanasu farin ciki idan ta sanar dasu ba.
Mommy ta katseta da fad’in “Kina jina bazaki sanar dasu yanzu ba.. Ki bari akwai lokacin da na tanadar ma hakan.. Amma idan kika zab’i kiyi abinki ke kad’ai ni bazance komai ba Sai na zuba miki idanu kiyi duk yanda kike so.. Idan kikaje garin shashashancinki da haukarki kika salwantar da cikin kinga ai shikenan kin huta..”
Safeenah tai shiru tana sauraron Mommy.. Sai kuma ta jinjina kai tace “Shikenan Mommy bazan sanar dasu ba zan jira lokacin da Kikace d’in..”
“Yauwa yanzu naji batu.. Tashi muje ki kwanta ki huta..”
Babu musu Safeenah ta mik’e tabi bayan Mommy.
**
Washe gari ma sassafe ya fice Dan ko sallama bai samu sunyi ba Assad na jiransa akwai yanda zasuje sann yana so ya soma biyawa Prison wajen Yusuf kafin suje yanda zasuje da Assad d’in.
Koda Sadiya ta farka taga har ya fice Sabon tashin hankali ta shiga, ba d’abi’arsa bace fita bai mata sallama ba.. Ko sauri yake zai shigo ya manna mata kiss ya kuma mata sallama ya sanar da ita aiki na gaggawa ya taso masa.. Amma sai gashi yau ya fita kuma sam ita dai bataji alamun shigowarsa ba.. Mai hakan yake nufi..? Tai jigum abin na neman ya d’aga mata hankali cikin k’ank’anin lokaci. Taji kanta na wani irin sara mata ga daren jiya ba wani samun isasshen bacci tai ba, haka tai kusan kwana tana juyi. Kewan gida ne ya isheta.. Taji tana son taje taga Umma da ‘yanuwanta. Tai tunanin kiran layinsa sai kuma ta tuna jiya fah rejecting yai sann bai ko bi takanta ba har wann lokacin.. Jiki a sanyaye ta aje wayar nata ba tareda ta kirasa ba. Tai zaune a parlor kaman marainiya tana tinanin rayuwa da irin k’alubalen data fuskanta a rayuwa.. Shin wann ma wani sabon karatun ne..? Tambayar da zuciyarta tai mata. Kwanciya tai lak’was cikin kujera tana jin ko kitchen kaman bazata iya shiga ba a nan bacci b’arawo ya d’auketa abinka da wacce bata wani sami bacci daren da ya gabata ba.
**
Mu’azzam yai zaune yana jiran fitowar Yusuf a wajen da aka tanada domin ganawa sa prisoners.. Can ya hangosa ya nufo yanda yake wani ganduroba biye dashi.
Mu’azzam ya tsaresa da idanu yana dubansa yanda yake nufosa, a maimakon kayan ‘yansanda kayan prisoners ne jikinsa.. Ya d’an kauda fuskarsa kad’an yana jin wani abu na tokarin zuciyarsa.. Maiyasa abokinsa zaici amanarsa.. Maiyasa Yusuf..?
Daidai lokacin Yusuf ya k’araso gajeriyar murmushi saman fuskarsa, ya zauna a kujera mai kallon na Mu’azzam teburi ya raba tsakaninsu.
“Inspector, what brought you here this early..?” Yusuf ya tambaya yana d’an shafa hab’arsa kad’an idanunsa akan Mu’azzam d’in.
Mu’azzam ya kafesa da idanu yana dubansa, saida ya kwashi tsawon lokaci a haka har Yusuf ya soma gudura, ya saki murmushi yana ‘yan waige waige lokaci guda yana rage girman idanunsa kad’an “You shouldn’t been seen here Inspector.. You know this could be dangerous for me... Kar ka mance they have eyes everywhere.. Suna karantar duk wani movement d’ina..” Ya kuma duban Mu’azzam d’in yana sakin murmushi a hankali “I don’t want to get killed Inspector.. Nida munsan ya criminals suke gudanar da al’amaransu musamman a Prison.. They can easily eliminate me here.”
“Kayi magana idan baka so su kashe ka.. Ka fad’i duk abinda ka sani.. Na tabbata sentences d’inka bazai kai nasu ba.. Yusuf Maiyasa kake karesu.. Maiyasa ka zab’i ka biya laifinsu alhali su suna can suna ci gaba da b’arna.. Yusuf idan ka tab’a valuing aikin ka a matsayinka na jami’in tsaro zaka Fad’i gaskiya.. Yusuf wad’anda kake karewa bazasu tab’a k’yaleka ba koda kayi abinda suke so..” Ya d’anyi fasali yana dubansa Yusuf.. Su duka biyun duban juna suke, kafin Mu’azzam ya kuma daidaita zamansa yana fad’in “If you once valued our friendship zaka sanar dani abinda ka sani..”
Yasa hannu a aljihunsa ya ciro coin d’in Black African Team ya nunawa Yusuf yace “Tell me... What do you know about this..?”
Yusuf ya k’ura masa idanu yana kuma duban coin d’in kafin ya murmusa yace “Mai wann yake nufi..? Wann ai sisin kwabo ne..”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “Black Africa Team.. Mai ka sani gameda wann Syndicate d’in..?”
Yusuf ya murmusa kad’an yana shafa hab’arsa sai kuma yace “I don’t know.. Ban Sani ba Mu’azzam.. Bansan wani Syndicate mai wann sunan ba.”
Mu’azzam ya kuma jinjina kai yace “Human Trafficking Syndicate.. But it’s been long destroyed.. Danger is somehow connected to that Syndicate.. Idan har kana aiki ma Danger, I’m quite certain zaka iya sanin wani abu gameda Balck African Team..”
Yusuf ya d’an sosa kunnensa kad’an yana Murmusawa.
Mu’azzam ya kuma tsaresa da idanu yana fad’in “For all time sake Yusuf.. Please do what is right..” Ya k’arashe yana duban Yusuf d’in cikin yanayi na ban tausayi.
Jikin Yusuf ya d’anyi sanyi, Dan shi kansa cin amanan abokansa da yayi sosai abin ke masa ciwo.. Ya d’ago yana duban Mu’azzam ga lokacin komawansa ciki yayi Dan har ganduroba d’in ya k’araso yana jira suyi rounding up.
Yusuf ya mik’e Mu’azzam ma ya mik’e yana girgiza kai “Please Yusuf, do this for our friendship.”
Yusuf na murmushi yake duban Mu’azzam d’in, cikin k’arfin hali yake danne hawayen dake k’ok’arin ciko idanunsa “What Friendship are talking about Mu’azzam.. Abotan da na lalata.. Abotan da bai mana rana ba..? Abotan da ya rikid’a ya koma k’iyayya.. Wann abotan kake magana akai..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Bansan dalilinka na cin amananmu ba Yusuf amma na sani you are not like them.. Kai ba kaman su bane.. You still have good in you.. Kar kabi abinda zuciyarka ke fad’a maka.. Kabi abinda mind d’inka yake sanar dakai.. Expose them Yusuf.. Kar ka bari suyi amfani dakai..”
Yusuf ya murmusa kad’an kafin yace “I guess circumstance na rayuwa yakan iya jefa bawa cikin k’addaran da bai tab’a tsammanin zai tsinci kansa ciki ba.. It’s too late Mu’azzam.. Na riga da na makara.. Kaje Mu’azzam, I’ve faith in you.. I know you’ll bring them down.. Nasan zaka kamasu zaka cimmasu watarana.. Sabida ka d’auko hanya..” Ya d’anyi fasali yana rok’on Ganduroban ya k’ara masa mintoci kafin ya dubi Mu’azzam yaci gaba da fad’in “Zan fad’a maka wani abu guda d’aya.. Kaje ka nemo wanene BAT.. Idan ka cimma BAT ka samu kan K’umurcin da kaketa farauta..” Ya juya zai wuce Mu’azzam ya dakatar dashi da fad’in “Kana nufin Black African Team.. Shine BAT d’in..?”