Sashe 16
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali yake jinjina kai still yana dubanta da rinannun idanunsa “Wannan shine hujjarki na zuwa har wajen aiki na kici mutunci na.. Fine, Yayi kyau Safeenah.. Zan tabbatar kin biya duk abubuwan da kika aikata.. You’ll pay dearly Safeenah.. Daga rana mai kaman ta yau kin gama rashin kunya, Idan kuma ba haka ba sunana ba Mu’azzam Abubakar Gamji ba...!” Ya k’arashe yana sakin murmushin nasa da gefen baki wanda tasan idan yayi wani sharrin nasu na ‘yansanda zai k’ulla a cewar Safeenah..
Tai raurau da idanu tana dubansa yanda ya tsime kaman ba shine ya saki muguwar murmushin nan ba..
“Shige muje..!” Ya fad’i yana nuna mata hanya.
Jiki a matuk’ar sanyaye Safeenah tabi bayansa tana goge hawayen dake kwance idanunta..
Front seat ya bud’e yace ta shige, babu musu ta shige kafin ya zaga mazaunin mai driver ya shige.. Dik wannan drama Safeenah tama mance tareda Meema suke.. Ita kaw Meema tana jin shigowarsu Ta kuma mak’alewa k’asan Seat tana addu’an Allah ya ceceta yasa kar Ya Mu’azzam ya ganta.. Ita batasan Addah Safeenah wace irin sokuwa bace da har zata bari Ya Mu’azzam ya kamata gashi yanzu shi zai driving d’insu home, ai kuwa wllhi saidai ta kwanta k’asar motar har su isa gida a haka..
A rashin hankalin Meema Mu’azzam bai ganta kwance k’asar motar bane, saidai Ta kula kaman da gangan ya dinga tsalle saman speed bumps da motar.. Idan Meema taji zafi saidai ta toshe bakinta kar tayi ihu ya jita ya gane tana motar.. Haka ya dinga gwarata saman kwalta tana matse bakinta dan azaba..
Ga tsananin mamakin Safeena gidansa da akai mata jere ya kaisu.. Ta d’ago tana dubansa da Mamaki...
“Mai Zamuyi a nan..?”
“Isn’t it obvious. Gidanki na kawoki.. Ki zauna har lokacin da gidan zai gundureki..”Ya bata amsa kai tsaye yana mai ficewa daga cikin motar..
Meema dai taji anyi parking batasan Ina akazo ba har saida taji Muryan Mu’azzam yana Fad’iwa Safeenah gidanta ya kawota..
Safeenah kaw tab’e baki tai kad’an zuciyarta na mata sanyi, tana ganin ya bud’e motar ya fice Ta soma furta “Weldon Feenah.. Kinyi daidai..Ko banza kwalliya Ta biya kud’in Sabulu gashi da kanka baka jira wani ya kawo maka ni ba ka kawoni da kanka..” Ta saki Murmushi tana k’ok’arin bud’e motar taji wani irin haushin police dogs irin manya manyan nan masu kaman kuraye..
Wani irin k’ara Safeenah ta saki ta jawo marfin motar babu shiri..
Ihun da Safeenah ta saki ya sanya Meema mik’ewa zaune cikin motar tana kallon yanda suke...
Itakam Safeenah har Ta mance Wai tare suke da Meema saida Meemar ta taso daga mab’oyarta..
Meema ta soma salati tana fad’in “Mun shiga uku mun mutu mun lalace.. Addah Feenah Police Dogs d’insa ya kwance mana ya barmu rufe cikin Mota yayi tafiyarsa..”
Idan karnukan sukai haushi sai Safeenah da Meema sun manne waje d’aya dan tsoro suna sakin ihu.. Wane irin haushi mai diri da ban tsoro suke..Gashi babu hali Su bud’e glass d’in motar Karnukan zasuyi tsalle su shigo motar, gashi Mu’azzam ya kashe motar ya cire key balle su kunna motar ko AC ne Su kunna.. Ga zafin cikin Mota ga Karnuka waje sai haushi suke jikin motar suna zagaye motar..
K’iris ya rage Meema bata saki fitsari ba ganin Mu’azzam ya fice daga cikin gidan ya kullesu ya barsu rufe cikin Mota police dogs na kewayesu suna shawagi a jikin motar..
Meema ta saki ihu tana fad’in “Adda Feenah wllhi ficewa zaiyi dan Allah ki kirasa ya dawo ya cecemu ya fitar damu.. Wllhi suffocating zamuyi cikin motar nan idan ya tafi ya barmu.. Dan Allah ki tsaidashi.. Na shiga uku ni Meema Wllhi ni tsautsayi ne dama ya sani biyoki.. Mun shiga uku wllhi horo zai mana irin tasu Ta ‘yansanda mu ba criminals ba.. Adda Feenah dan Allah ki ceceni a fiddani daga gidan nan dama ke gidanki ne..”
Cikin kuka Feenah tace “Ke ni Kimin shiru duk na kece kika kawo shawarin ba.. Wayyo na shiga ukku..” Ta sake sakin k’ara a daidai lokacin da karnukan suke kuma haushi..
Shi kaw Mu’azzam Ko ajikinsa yana ficewa ya tari cab ya nufi location d’in da abokan aikinsa ke jiransa..
**
A b’angaren su Sadiya saida suka biya wani chemist aka duba k’afar Umma aka d’aure mata cikin bandage kafin suka nufi Gida.. Saidai suna dosowa layinsu gabansu yayi wani irin yankewa ya fad’i.. Cincirondon mutane suka hango, hakan ya sanyasu d’an k’ara sauri dikda cewa Umma d’ingishi take Sadiyar ce mai taimaka mata..
Gabansu bai ida yankewa ba saida suka hango mutanen tare suke k’ofar gidansu, ga mutum kwance cikin jini Habeeb da Ashiru sun kifa Kai saman k’irjin mutumin suna kuka.. Take Sadiya taji duniyar na juya mata, Ta rasa tafiya take kan k’afafunta kokuwa a iska take, zuciyarta yaci gaba da tsinkewa suna mai kuma tunk’aran dandatson mutanen..
Duniyar Sadiya bata ida juyewa ba saida ta sinkayo muryar Ashiru yana jijjiga mutumin yana fad’in “Abba..! Abba dan Allah ka tashi.. Abba ka tashi dan Allah.. Abba naaa..!!”
“Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un” Shine kalman da Umma ta iya furtawa.. Sadiya kuwa hannu biyu Ta saka aka had’ida sakin wani irin k’ara tana mai silalewa wajen..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*10*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
FUFORE
_Adamawa State, Nigeria_
Ta kasance ranace na cin kasuwar garin, mutane daga ko wacce lungu da sak’o sai tururuwan zuwa kasuwar suke domin saye da sayawarwan hajojinsu. Mutane da rugagen da suke kusa dasu sukan shigo garin domin cin Kasuwa..
Wata kyakkyawar budurwa ce zaune k’asar Rumfar azara wacce bazata gaza shekaru 18 ba, ga tulin k’ulli k’ullin magunguna gabanta. tana karkad’a karan barankaci tana fad’i cikin wak’e irin yanda masu saida magani suke “Azo a sayi magani.. Sai an gwada ake sanin na k’warai. Magani ko wacce iri ce zaka samu wajenmu.. Azo a sayi maganin AJIDDE d’iyar Kyallu mai warka warka.. Ina saurayi mai shirin yin wasan shad’i Ina budurwa mai neman Farin jini.. Ina me neman lak’anin kariya daga mugun baki ko maita, toh ga Ajidde ta taho maku da warka warka...Azo a gwada maganin Ajidde d’iyar Kyallu mai Warka warka.. Dik garin nan babu wanda baisan amincin maganinmu ba.. Azo a gwada..!” Cikin harshen fillanci take tallan magungunan nata.. Kan kace mai an wawushe magungunanta..
Ajidde ta Washe baki tana k’irga cinikin da tai, ta kuma turo kallabinta gaba tana kuma k’irga kud’ad’en “Wo ni Ajidde wllhi Inna Kyallu yau dole ki saka mun albarka.. Kai jama’a watau dai idan kana so kayi kud’i nan take ka zamo macuci..” Ta shek’e da dariya tana tura kud’d’en cikin lalitarta “Ahab wawayen banza ku kuka sani idan maganin bai maku aiki ba.. Heheheh wllhi nidai babu ruwana Inna Kyallu ce ta d’auran talla..”
Tana ida fad’in haka ta mik’e daga Rumfar tata ta nufi gida tin kafin Kasuwa ta watse sabida ta gama saida kayyayakinta..
Tana isowa gida ta hangi d’akinda Kyallu take duba majinyata wata mata mai tsohon ciki Ta fito.. Kyallu na biyeda ita cikin shigarta ta bak’ar riga.. Wannan kakkauran bak’ar riga itace rigar Kyallu duk zafi duk sanyi. Ga uban daud’a da rigar tayi.. Ita kanta Kyallun idan ka dubeta sai ta baka k’yama sabida tsaban datti da daud’anta..
Hannayen mata mai cikin rik’eda guraye da layu Kyallu naci gaba da fad’in “Ki tabbata ki d’aura gurun nan dan shine maganin mugun baki harma da mayu.. Shi zai baki kariya Keda abin da ke cikinki daga duk mai nemanki da sharri bama kishiyoyinki da suka saka ido kan abin dake cikinki ba, zai baku kariya daga sharrin mugu... Shi kuma layan da zaran kin haihu a d’aura ma jaririn a wuyarsa shi zai zame masa kariya..”
Matar cikeda jin dad’I had’ida amincewa da abunda Kyallu ta fad’I mata take jinjina kai tana ma Kyallu godiya cikin tab’ewa da dulmuyewar basira.
Matar sukai sallama da Kyallu kafin Ajidde ta k’arasa wajen Kyallu.
“Inna Kyallu albishirinki.. Yau dai kaf na saida komai dole ki saka min albarka..”
Dariya mai sauti Kyallu tai da muryarta mai gwab’in gaske kana tace “Ai babu albarka tattareda ke Ajidde.. Ki daina mafarkin samun albarka daga wajena.. K’irgo kud’ad’ena ki mik’o mun..”
Jikin Ajidde ya d’anyi sanyi.. lokaci guda ta shiga fiddo kud’ad’en tana mik’a ma Kyallu..
Kyallu ta k’irgaga kud’ad’enta ta soke a hamnatarta.
“Yauwa kina jina..?”
Ajidde ta gyad’a kai a hankali
Kyallu taci gaba da fad’in “Gobe zakije Gidan Gonar nan dake wajen gari ki kai maganin matar nan..”
Nan fah Ajidde Ta soma Washe baki dan sau d’aya kawai da sukaje gidan gonar nan taji tana son wajen.. Ga shukoki koraye gwanin ban sha’awa ga kuma dabbobi masu yawan gaske kama daga shanunmu na gida har zuwa irin na turawan nan iyaka ganinka dan yawansu.. Kai gaskiya a cikin noma da kiwo akwai albarka mai tarin yawa..
Tuni Ajidde Ta soma murna ta mance fushin da take na rashin saka mata albarka da Kyallu batayi.
**
ABUJA
Kaman yanda sukai tsammani basu tadda Danger ba, majalisar k’ofar shagonsa ma babu kowa babu komai kaman anyi shara..
Shiru Mu’azzam yai yana nazari sanda suka keb’e su biyu shida Assad.
“I told you so.. Mutumin nan must be in hiding, an sanar dashi muna nemansa.. Idan bai fice a gari ba Toh kuwa shakka babu yana b’oye wani wajen. Idan ba Chief Jaja bane ya sanar dashi waye zai sanar dashi.. Who could be his informer Assad.?!” Ya k’arashe yana sakin huci a hankali.
Assad ya nusa yace “Ba Lallai ya zama Chief Jaja ba, sabida Chief ma bai san da hakan ba har saida abin ya kasance.. And it could be anyone from our Department.. Kasan yanda Al’amara suke a wajenmu..”
D’an jim Mu’azzam yayi kafin ya girgiza kai yace “No way.. Binciken nan is classified, there’s no how wani daga department d’inmu zai zama snitch... The only Rat here is Chief Jaja.. And don’t forget a aiki irin namu wanda ya d’auraka kan bincike zai iya maka zagon k’asa domin ya b’afar da basirarka..”
Tai raurau da idanu tana dubansa yanda ya tsime kaman ba shine ya saki muguwar murmushin nan ba..
“Shige muje..!” Ya fad’i yana nuna mata hanya.
Jiki a matuk’ar sanyaye Safeenah tabi bayansa tana goge hawayen dake kwance idanunta..
Front seat ya bud’e yace ta shige, babu musu ta shige kafin ya zaga mazaunin mai driver ya shige.. Dik wannan drama Safeenah tama mance tareda Meema suke.. Ita kaw Meema tana jin shigowarsu Ta kuma mak’alewa k’asan Seat tana addu’an Allah ya ceceta yasa kar Ya Mu’azzam ya ganta.. Ita batasan Addah Safeenah wace irin sokuwa bace da har zata bari Ya Mu’azzam ya kamata gashi yanzu shi zai driving d’insu home, ai kuwa wllhi saidai ta kwanta k’asar motar har su isa gida a haka..
A rashin hankalin Meema Mu’azzam bai ganta kwance k’asar motar bane, saidai Ta kula kaman da gangan ya dinga tsalle saman speed bumps da motar.. Idan Meema taji zafi saidai ta toshe bakinta kar tayi ihu ya jita ya gane tana motar.. Haka ya dinga gwarata saman kwalta tana matse bakinta dan azaba..
Ga tsananin mamakin Safeena gidansa da akai mata jere ya kaisu.. Ta d’ago tana dubansa da Mamaki...
“Mai Zamuyi a nan..?”
“Isn’t it obvious. Gidanki na kawoki.. Ki zauna har lokacin da gidan zai gundureki..”Ya bata amsa kai tsaye yana mai ficewa daga cikin motar..
Meema dai taji anyi parking batasan Ina akazo ba har saida taji Muryan Mu’azzam yana Fad’iwa Safeenah gidanta ya kawota..
Safeenah kaw tab’e baki tai kad’an zuciyarta na mata sanyi, tana ganin ya bud’e motar ya fice Ta soma furta “Weldon Feenah.. Kinyi daidai..Ko banza kwalliya Ta biya kud’in Sabulu gashi da kanka baka jira wani ya kawo maka ni ba ka kawoni da kanka..” Ta saki Murmushi tana k’ok’arin bud’e motar taji wani irin haushin police dogs irin manya manyan nan masu kaman kuraye..
Wani irin k’ara Safeenah ta saki ta jawo marfin motar babu shiri..
Ihun da Safeenah ta saki ya sanya Meema mik’ewa zaune cikin motar tana kallon yanda suke...
Itakam Safeenah har Ta mance Wai tare suke da Meema saida Meemar ta taso daga mab’oyarta..
Meema ta soma salati tana fad’in “Mun shiga uku mun mutu mun lalace.. Addah Feenah Police Dogs d’insa ya kwance mana ya barmu rufe cikin Mota yayi tafiyarsa..”
Idan karnukan sukai haushi sai Safeenah da Meema sun manne waje d’aya dan tsoro suna sakin ihu.. Wane irin haushi mai diri da ban tsoro suke..Gashi babu hali Su bud’e glass d’in motar Karnukan zasuyi tsalle su shigo motar, gashi Mu’azzam ya kashe motar ya cire key balle su kunna motar ko AC ne Su kunna.. Ga zafin cikin Mota ga Karnuka waje sai haushi suke jikin motar suna zagaye motar..
K’iris ya rage Meema bata saki fitsari ba ganin Mu’azzam ya fice daga cikin gidan ya kullesu ya barsu rufe cikin Mota police dogs na kewayesu suna shawagi a jikin motar..
Meema ta saki ihu tana fad’in “Adda Feenah wllhi ficewa zaiyi dan Allah ki kirasa ya dawo ya cecemu ya fitar damu.. Wllhi suffocating zamuyi cikin motar nan idan ya tafi ya barmu.. Dan Allah ki tsaidashi.. Na shiga uku ni Meema Wllhi ni tsautsayi ne dama ya sani biyoki.. Mun shiga uku wllhi horo zai mana irin tasu Ta ‘yansanda mu ba criminals ba.. Adda Feenah dan Allah ki ceceni a fiddani daga gidan nan dama ke gidanki ne..”
Cikin kuka Feenah tace “Ke ni Kimin shiru duk na kece kika kawo shawarin ba.. Wayyo na shiga ukku..” Ta sake sakin k’ara a daidai lokacin da karnukan suke kuma haushi..
Shi kaw Mu’azzam Ko ajikinsa yana ficewa ya tari cab ya nufi location d’in da abokan aikinsa ke jiransa..
**
A b’angaren su Sadiya saida suka biya wani chemist aka duba k’afar Umma aka d’aure mata cikin bandage kafin suka nufi Gida.. Saidai suna dosowa layinsu gabansu yayi wani irin yankewa ya fad’i.. Cincirondon mutane suka hango, hakan ya sanyasu d’an k’ara sauri dikda cewa Umma d’ingishi take Sadiyar ce mai taimaka mata..
Gabansu bai ida yankewa ba saida suka hango mutanen tare suke k’ofar gidansu, ga mutum kwance cikin jini Habeeb da Ashiru sun kifa Kai saman k’irjin mutumin suna kuka.. Take Sadiya taji duniyar na juya mata, Ta rasa tafiya take kan k’afafunta kokuwa a iska take, zuciyarta yaci gaba da tsinkewa suna mai kuma tunk’aran dandatson mutanen..
Duniyar Sadiya bata ida juyewa ba saida ta sinkayo muryar Ashiru yana jijjiga mutumin yana fad’in “Abba..! Abba dan Allah ka tashi.. Abba ka tashi dan Allah.. Abba naaa..!!”
“Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un” Shine kalman da Umma ta iya furtawa.. Sadiya kuwa hannu biyu Ta saka aka had’ida sakin wani irin k’ara tana mai silalewa wajen..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*10*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
FUFORE
_Adamawa State, Nigeria_
Ta kasance ranace na cin kasuwar garin, mutane daga ko wacce lungu da sak’o sai tururuwan zuwa kasuwar suke domin saye da sayawarwan hajojinsu. Mutane da rugagen da suke kusa dasu sukan shigo garin domin cin Kasuwa..
Wata kyakkyawar budurwa ce zaune k’asar Rumfar azara wacce bazata gaza shekaru 18 ba, ga tulin k’ulli k’ullin magunguna gabanta. tana karkad’a karan barankaci tana fad’i cikin wak’e irin yanda masu saida magani suke “Azo a sayi magani.. Sai an gwada ake sanin na k’warai. Magani ko wacce iri ce zaka samu wajenmu.. Azo a sayi maganin AJIDDE d’iyar Kyallu mai warka warka.. Ina saurayi mai shirin yin wasan shad’i Ina budurwa mai neman Farin jini.. Ina me neman lak’anin kariya daga mugun baki ko maita, toh ga Ajidde ta taho maku da warka warka...Azo a gwada maganin Ajidde d’iyar Kyallu mai Warka warka.. Dik garin nan babu wanda baisan amincin maganinmu ba.. Azo a gwada..!” Cikin harshen fillanci take tallan magungunan nata.. Kan kace mai an wawushe magungunanta..
Ajidde ta Washe baki tana k’irga cinikin da tai, ta kuma turo kallabinta gaba tana kuma k’irga kud’ad’en “Wo ni Ajidde wllhi Inna Kyallu yau dole ki saka mun albarka.. Kai jama’a watau dai idan kana so kayi kud’i nan take ka zamo macuci..” Ta shek’e da dariya tana tura kud’d’en cikin lalitarta “Ahab wawayen banza ku kuka sani idan maganin bai maku aiki ba.. Heheheh wllhi nidai babu ruwana Inna Kyallu ce ta d’auran talla..”
Tana ida fad’in haka ta mik’e daga Rumfar tata ta nufi gida tin kafin Kasuwa ta watse sabida ta gama saida kayyayakinta..
Tana isowa gida ta hangi d’akinda Kyallu take duba majinyata wata mata mai tsohon ciki Ta fito.. Kyallu na biyeda ita cikin shigarta ta bak’ar riga.. Wannan kakkauran bak’ar riga itace rigar Kyallu duk zafi duk sanyi. Ga uban daud’a da rigar tayi.. Ita kanta Kyallun idan ka dubeta sai ta baka k’yama sabida tsaban datti da daud’anta..
Hannayen mata mai cikin rik’eda guraye da layu Kyallu naci gaba da fad’in “Ki tabbata ki d’aura gurun nan dan shine maganin mugun baki harma da mayu.. Shi zai baki kariya Keda abin da ke cikinki daga duk mai nemanki da sharri bama kishiyoyinki da suka saka ido kan abin dake cikinki ba, zai baku kariya daga sharrin mugu... Shi kuma layan da zaran kin haihu a d’aura ma jaririn a wuyarsa shi zai zame masa kariya..”
Matar cikeda jin dad’I had’ida amincewa da abunda Kyallu ta fad’I mata take jinjina kai tana ma Kyallu godiya cikin tab’ewa da dulmuyewar basira.
Matar sukai sallama da Kyallu kafin Ajidde ta k’arasa wajen Kyallu.
“Inna Kyallu albishirinki.. Yau dai kaf na saida komai dole ki saka min albarka..”
Dariya mai sauti Kyallu tai da muryarta mai gwab’in gaske kana tace “Ai babu albarka tattareda ke Ajidde.. Ki daina mafarkin samun albarka daga wajena.. K’irgo kud’ad’ena ki mik’o mun..”
Jikin Ajidde ya d’anyi sanyi.. lokaci guda ta shiga fiddo kud’ad’en tana mik’a ma Kyallu..
Kyallu ta k’irgaga kud’ad’enta ta soke a hamnatarta.
“Yauwa kina jina..?”
Ajidde ta gyad’a kai a hankali
Kyallu taci gaba da fad’in “Gobe zakije Gidan Gonar nan dake wajen gari ki kai maganin matar nan..”
Nan fah Ajidde Ta soma Washe baki dan sau d’aya kawai da sukaje gidan gonar nan taji tana son wajen.. Ga shukoki koraye gwanin ban sha’awa ga kuma dabbobi masu yawan gaske kama daga shanunmu na gida har zuwa irin na turawan nan iyaka ganinka dan yawansu.. Kai gaskiya a cikin noma da kiwo akwai albarka mai tarin yawa..
Tuni Ajidde Ta soma murna ta mance fushin da take na rashin saka mata albarka da Kyallu batayi.
**
ABUJA
Kaman yanda sukai tsammani basu tadda Danger ba, majalisar k’ofar shagonsa ma babu kowa babu komai kaman anyi shara..
Shiru Mu’azzam yai yana nazari sanda suka keb’e su biyu shida Assad.
“I told you so.. Mutumin nan must be in hiding, an sanar dashi muna nemansa.. Idan bai fice a gari ba Toh kuwa shakka babu yana b’oye wani wajen. Idan ba Chief Jaja bane ya sanar dashi waye zai sanar dashi.. Who could be his informer Assad.?!” Ya k’arashe yana sakin huci a hankali.
Assad ya nusa yace “Ba Lallai ya zama Chief Jaja ba, sabida Chief ma bai san da hakan ba har saida abin ya kasance.. And it could be anyone from our Department.. Kasan yanda Al’amara suke a wajenmu..”
D’an jim Mu’azzam yayi kafin ya girgiza kai yace “No way.. Binciken nan is classified, there’s no how wani daga department d’inmu zai zama snitch... The only Rat here is Chief Jaja.. And don’t forget a aiki irin namu wanda ya d’auraka kan bincike zai iya maka zagon k’asa domin ya b’afar da basirarka..”