Sashe 21
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yau d’inma hakance ta kasance da Ajidde..
Malama Hafsah na aji tana ma matan aure karatu Ajidde ta shigo da k’yar da k’yar kaman zata kifa k’asa..
‘Yan aji suna ganin Ajidde suka soma k’ok’arin mik’ewa kowacce tana neman hanyar gudu dan an canfa ance tanada Farin k’afa dik yanda taje Sai bala’i ya auku wajen.. Malama ta tsawatar masu da fad’in “Shin ba yanzu muka gama karatu kan yarda da canfi ba.. Canfi haramun ne a musulunci.”
Wata mata Ta d’aga hannu tace “Malama inada tambaya”
Malama Ta jinjina mata kai tace “Ina sauraronki..”
“Amma malama ai akwai Kambun baka.. Shin shi ba canfi bane..?”
Malama ta jinjina kai tace “K’warai Al’ainu haqqun. Akwai Kambun baka, harta a musulunci an yarda akwai Kambun baka, yazo kuma a sunna cewa akwai Kambun baka har an bamu addu’a da zamu dinga yi domin neman tsari daga sharrin Ido wanda ake cema kambun baka.. D’aura laya ko wani abu mai kama da haka da sunan neman kariya daga sharrin ido haramun ne a musulunci.. Yin hakan shirka ne inji Manzon Allah SAW, hadisin yana nan a cikin Musnad Ahmad 16969.” Malama ta d’an tsagaita kafin taci gaba da fad’in “Wacce dik take neman kariya daga sharrin ido ko Kambun baka ga abinda zatace ‘A’uthzu bi kalimatillahit taammaati min kulli shaid’anin wa haammaa wa min kulli ainin laammaa.’ Wannan addu’a ce ingantacciya datazo a sunna sannan zaki iya karanta ma yaranki ko wacce safiya da maraice domin nema masu kariya daga sharrin ido dama duk wani shed’ani ko abin sharri.. Babban darasin da nake so mu d’auka a nan shine wani baya tab’a sauk’ar maka da bala’i sai idan Allah yaso haka wani baya tab’a kawo maka nasara sai idan Allah yaso Kun fahimta..”
Gaba d’aya suka amsa da “Na’am Malama mun gane..”
Malama ta jinjina kai tace “Monita ki bud’e shafin da muka k’ara jiya ayi bitarsa kafin na dawo muyi k’ari.. Ku d’an ara min lokaci naji da Ajidde..”
Gaba d’aya suka jinjina kai suna amsa mata..
Malama ta janyo Ajidde suka fice zuwa tsakar gidanta..
Dik karatun kore shirka da aikata tauhidi da malama tai tsaf Ajidde ta saurareta, gaba d’aya jikin Ajidde yayi sanyi domin kuwa abinda Inna Kyallu ta d’aurata Kai kenan..
Malama ta nufi kitchen ta d’auko ma Ajidde abinci Ta bata tace ta zauna taci..
Saidai yau gaba d’aya jikin Ajidden a sanyaye yake babu sokancin data saba yima Malama.. Tak’i zama taci abincin ta fice sai waige waige take tana kuma duban Malamar rungume da kwanon abincin. Sauri sauri ta fice dan kar Inna Kyallu ta dawo ta tadda bata nan..
Malama Ta bita da kallo cikeda tausayawa har Ta b’ace ma ganinta.. Allah ya gani rayuwar yarinyar sosai yake bata tausayi..
**
Koda Kyallu ta isa gidan gonar sassafe tasa aka rufesu a d’aki daga ita sai Aunty Nurah, tai mata hayak’i da surace na magani.. Ta ciro wasu layu guda biyu ta bama Aunty Shemau tace a saka cikin matashin da Aunty Nuratu ke kwanciya..
Shemau Ta amsa tanai mata godiya.. Nan take sanar da Aunty Shemaun idan bata sami zuwa Washe gari ba zata turo d’iyarta ta bata maganin dan ita kusan ko yaushe fama take da masu karb’an magani..
Aunty Shemau tace babu damuwa za’ayi dik abinda Kyallu tace d’in..
Koda suka fito Daddy na parlor yana jira ya shiga yayi sallama da matarsa dan a yau d’in zai koma Abuja..
Koda Daddy yaga Kyallu tsareta da idanu yayi dan haka kurum yaji mata mai maganin bata wani kwanta masa ba amma yasan ba daga appearance na mutum bane kyaun magani.. Kuma basu san a Ina maganin Nuratu yake ba.. Idan aka dace sai maganin wannan matan yayi mata aiki..
Shemau dikda tasha jinin jikinta da ganin Daddy zaune yana jira a parlor hakan bai hanata wayancewa ta risina tana gaida Daddy had’ida introducing Kyallu mai magani..
Daddy ya amsa masu da sakin fuska ya kumayi ma Kyallu godiya..
Har zasu shige Daddy ya tsaida Shemau, ya ciro kud’ad’e da dama yace a k’ara wa mai maganin..
Kyallu ta kanne idanu tana duban tulin kud’in da aka bata.. Tuni ta Washe baki ta shiga yima Daddy godiya da addu’an girma.. Lokaci guda tana kuma gwad’a maganinta da fad’in nan da k’ank’amin lokaci zasuga canji jikin Nuratu..
Daddy yace Allah yasa haka kafin ya nufi d’akin..
Kwance take fuskarta Ta kuma yin fayau Sai hancinta da d’an bakinta kake hangowa, Ya k’ura mata idanu k’walla fal idanunsa.. A hankali ya duk’a ya d’aura hannunsa guda saman nata. Cikin rawar murya yake furta “Bansan ko na cika alk’awarin da na d’aukar ma d’anuwana ba cewa zan kula da bayansa.. I don’t know why I’m feeling this way.. Like I failed somehow.. Ban cika alk’awarin dana d’aukar ma d’anuwana cewa zan kula da bayansa ba.. It’s been 15 long years kina kwance cikin jinya ba tareda Kinsan a Ina kike ba.. And.. And Ikram..” Kuka ya hana Daddy ci gaba da magana, kansa kife gefen Nuratun, yake furtawa cikin murya irinta mai kuka “I failed to protect his family.. Na kasa kula dasu as I promised to.. Na kasa..!”
Mu’azzam yai tsaye bakin k’ofa yana duban yanda Daddy ke kuka kan mahaifiyarsa yana fad’in ya kasa kula dasu.. A hankali yake takowa cikin d’akin har ya k’araso yanda Daddy ke duk’e.. Yakai hannu ya dafasa.
Daddy na d’agowa da yaga Mu’azzam d’in sai ya kuma jin rauni can k’asar zuciyarsa..
A hankali Mu’azzam ya duk’a ya rik’o hannayen Daddy cikin nasa “Baka gaza ba Daddy.. What was meant to happen happened. Kuma Ka kula da bayan mahaifina kaman yanda kayi alk’awari.. Daidai da rana guda baka fasa cika alk’awarinka ba.. You’re true definition of a good brother Daddy... You’ve been taking care of us ever since my father passed.. You’ve become a father to his children and a husband to his wife wacce tin sanda ka aureta Allah ya jarabceta da jinya.. I’ve seen a lot of men wad’anda idan matansu Sun kamu da cuta irin haka har gida suke maidasu suje suyi jinya wasu ma auren ya k’are.. But bakayi haka ba Daddy.. Kai d’in ka d’auki d’awainiyar jinyarta kuma ka kula da ita daidai da rana guda baka gaza ba..”
Saurin girgiza kai Daddy yai yana mai duban Mu’azzam d’in “Don’t say those words Mu’azzam dik abinda nayi nauyi ne da ya rataya a wuyana and it’s not a favor kaji koh.. Come here..” Ya k’arashe yana rungumar Mu’azzam d’in.
Uncle Salman dake tsaye jikin k’ofa da ido ya tsaresu, lokaci guda ya koma da baya ba tareda ya bari sun gansa ba.
**
SULEJA
Tashin hankali goma da ashirin shine abinda Sadiya da ahalinta ke fuskanta, a yayinda mahaifinsu ko rufa kwanaki uku baiyi ba da mutuwa Tabawa ta kuma sakosu gaba da maganan biyan kud’inta.. Babu yanda Umma batai ba ta bari ko takaba ne ta gama idan yaso sai ta fita ta nemo mata kud’ad’enta ko wani aikin ne sai tayi ta samo mata kud’ad’enta..
Tabawa tace atafau ita bataji ba bata gani ba. Yo wani irin aiki ne ma zatayi ta samo mata kud’ad’enta idan ba Sana’ar bin maza data d’aura ‘yarta akai zasuyi Su biyata kud’ad’enta ba.. Wanann magana na Tabawa sosai ya tab’a Zuciyar Umman Sadiya.. Abinda batayi tin k’uruciya ba shine Tabawa take jifanta da munanan kalamai irin haka.. Ya zama dole Ta nemo wa Tabawa kud’ad’enta dan abin ya zama akwai tab’a mutunci da tozarci bazata bari Ta kuma traumatizing yaranta ba bayan tashin hankalin rashin mahaifinsu da suke ciki already.. Hakan yasa Umma yanke shawarin tink’aran Committee na masallacin unguwa ko da akwai irin taimakon da zasu masu su rabu da Tabawa.. Malam Liman ya gyara zama had’ida nusawa kad’an yace “Da farko nasiha zan fara maki da ita.. Ita wannan rayuwar da kuke gani duka ba yawa bace da ita, sannan dik halinda bawa zai tsinci kansa ciki jarabawa ake masa.. Bazai yuwu ace koda Yaushe mun samu abinda muke so ba.. Sannan Ko yatsunmu muka duba ba daidai bane wani yafi wani toh haka Ubangiji ya tsara mana rayuwarmu.. Wani yafika kaima kafi wani.. Kai wani arzikin lafiya ma kawai yake nema dikda d’imbin tarin dukiyar da yake dashi wanda zai iya kashe ko nawa ne domin ya samu wannan lafiyar amma bai samu ba.. Ga dukiyar Allah ya basa amma babu lafiya da zaiji dad’in dukiyar.. Kaikuma idan ka dubi kanka kaga Allah ya huwace maka wannan lafiyan sai kayi tunanin ya gama baka babban arziki.. Har kullum idan zamuke duba rayuwar na sama damu toh fah bazamu tab’a gode ma Allah da tarin ni’imomin da ya mana ba.. Amma idan muka dubi na k’asa damu sai muyi masa godiya da ni’imominsa garemu.. Shi kuma Sai ya k’ara mana domin fad’insa da yace _’Idan kuka gode Mun Ni kuma Zan k’ara maku_.’ “
Umma na matsan k’walla cikin hijabinta take jinjina kai “Haka ne Malam.. Kuma in sha Allahu mun d’auki darasi.. Ina kuma fatan masu halin kwad’ayi irin nawa abinda ya faru dani da d’iyata ya zamto izna garesu..” Kuka ya hanata ci gaba da magana
Malam Liman yace “Ki daina kuka in sha Allah Committee na masallaci zatayi iya k’ok’arinta ta had’o abinda za’a iya samu a baku ku rage bashin.. Ubangiji ya dafa mana gaba d’aya..”Ya k’arashe yana mai mik’ewa ya kuma yima Umma ta’aziya kafin ya fice.
Sadiya tai tagumi tana duban mahaifiyarta, ga k’annenta dake gefe har lokacin kuka suke. Hawaye suka kuma gangaro mata tana tina mahaifinta da k’alubale na rayuwa da suka fuskanta.. Inama mahaifinta zai dawo gareta da ta kasance irin d’iyar da yake so ta zama.. Amma saidai shi lokaci baya jira, idan ya wuce ya wuce kenan har abada..
Malama Hafsah na aji tana ma matan aure karatu Ajidde ta shigo da k’yar da k’yar kaman zata kifa k’asa..
‘Yan aji suna ganin Ajidde suka soma k’ok’arin mik’ewa kowacce tana neman hanyar gudu dan an canfa ance tanada Farin k’afa dik yanda taje Sai bala’i ya auku wajen.. Malama ta tsawatar masu da fad’in “Shin ba yanzu muka gama karatu kan yarda da canfi ba.. Canfi haramun ne a musulunci.”
Wata mata Ta d’aga hannu tace “Malama inada tambaya”
Malama Ta jinjina mata kai tace “Ina sauraronki..”
“Amma malama ai akwai Kambun baka.. Shin shi ba canfi bane..?”
Malama ta jinjina kai tace “K’warai Al’ainu haqqun. Akwai Kambun baka, harta a musulunci an yarda akwai Kambun baka, yazo kuma a sunna cewa akwai Kambun baka har an bamu addu’a da zamu dinga yi domin neman tsari daga sharrin Ido wanda ake cema kambun baka.. D’aura laya ko wani abu mai kama da haka da sunan neman kariya daga sharrin ido haramun ne a musulunci.. Yin hakan shirka ne inji Manzon Allah SAW, hadisin yana nan a cikin Musnad Ahmad 16969.” Malama ta d’an tsagaita kafin taci gaba da fad’in “Wacce dik take neman kariya daga sharrin ido ko Kambun baka ga abinda zatace ‘A’uthzu bi kalimatillahit taammaati min kulli shaid’anin wa haammaa wa min kulli ainin laammaa.’ Wannan addu’a ce ingantacciya datazo a sunna sannan zaki iya karanta ma yaranki ko wacce safiya da maraice domin nema masu kariya daga sharrin ido dama duk wani shed’ani ko abin sharri.. Babban darasin da nake so mu d’auka a nan shine wani baya tab’a sauk’ar maka da bala’i sai idan Allah yaso haka wani baya tab’a kawo maka nasara sai idan Allah yaso Kun fahimta..”
Gaba d’aya suka amsa da “Na’am Malama mun gane..”
Malama ta jinjina kai tace “Monita ki bud’e shafin da muka k’ara jiya ayi bitarsa kafin na dawo muyi k’ari.. Ku d’an ara min lokaci naji da Ajidde..”
Gaba d’aya suka jinjina kai suna amsa mata..
Malama ta janyo Ajidde suka fice zuwa tsakar gidanta..
Dik karatun kore shirka da aikata tauhidi da malama tai tsaf Ajidde ta saurareta, gaba d’aya jikin Ajidde yayi sanyi domin kuwa abinda Inna Kyallu ta d’aurata Kai kenan..
Malama ta nufi kitchen ta d’auko ma Ajidde abinci Ta bata tace ta zauna taci..
Saidai yau gaba d’aya jikin Ajidden a sanyaye yake babu sokancin data saba yima Malama.. Tak’i zama taci abincin ta fice sai waige waige take tana kuma duban Malamar rungume da kwanon abincin. Sauri sauri ta fice dan kar Inna Kyallu ta dawo ta tadda bata nan..
Malama Ta bita da kallo cikeda tausayawa har Ta b’ace ma ganinta.. Allah ya gani rayuwar yarinyar sosai yake bata tausayi..
**
Koda Kyallu ta isa gidan gonar sassafe tasa aka rufesu a d’aki daga ita sai Aunty Nurah, tai mata hayak’i da surace na magani.. Ta ciro wasu layu guda biyu ta bama Aunty Shemau tace a saka cikin matashin da Aunty Nuratu ke kwanciya..
Shemau Ta amsa tanai mata godiya.. Nan take sanar da Aunty Shemaun idan bata sami zuwa Washe gari ba zata turo d’iyarta ta bata maganin dan ita kusan ko yaushe fama take da masu karb’an magani..
Aunty Shemau tace babu damuwa za’ayi dik abinda Kyallu tace d’in..
Koda suka fito Daddy na parlor yana jira ya shiga yayi sallama da matarsa dan a yau d’in zai koma Abuja..
Koda Daddy yaga Kyallu tsareta da idanu yayi dan haka kurum yaji mata mai maganin bata wani kwanta masa ba amma yasan ba daga appearance na mutum bane kyaun magani.. Kuma basu san a Ina maganin Nuratu yake ba.. Idan aka dace sai maganin wannan matan yayi mata aiki..
Shemau dikda tasha jinin jikinta da ganin Daddy zaune yana jira a parlor hakan bai hanata wayancewa ta risina tana gaida Daddy had’ida introducing Kyallu mai magani..
Daddy ya amsa masu da sakin fuska ya kumayi ma Kyallu godiya..
Har zasu shige Daddy ya tsaida Shemau, ya ciro kud’ad’e da dama yace a k’ara wa mai maganin..
Kyallu ta kanne idanu tana duban tulin kud’in da aka bata.. Tuni ta Washe baki ta shiga yima Daddy godiya da addu’an girma.. Lokaci guda tana kuma gwad’a maganinta da fad’in nan da k’ank’amin lokaci zasuga canji jikin Nuratu..
Daddy yace Allah yasa haka kafin ya nufi d’akin..
Kwance take fuskarta Ta kuma yin fayau Sai hancinta da d’an bakinta kake hangowa, Ya k’ura mata idanu k’walla fal idanunsa.. A hankali ya duk’a ya d’aura hannunsa guda saman nata. Cikin rawar murya yake furta “Bansan ko na cika alk’awarin da na d’aukar ma d’anuwana ba cewa zan kula da bayansa.. I don’t know why I’m feeling this way.. Like I failed somehow.. Ban cika alk’awarin dana d’aukar ma d’anuwana cewa zan kula da bayansa ba.. It’s been 15 long years kina kwance cikin jinya ba tareda Kinsan a Ina kike ba.. And.. And Ikram..” Kuka ya hana Daddy ci gaba da magana, kansa kife gefen Nuratun, yake furtawa cikin murya irinta mai kuka “I failed to protect his family.. Na kasa kula dasu as I promised to.. Na kasa..!”
Mu’azzam yai tsaye bakin k’ofa yana duban yanda Daddy ke kuka kan mahaifiyarsa yana fad’in ya kasa kula dasu.. A hankali yake takowa cikin d’akin har ya k’araso yanda Daddy ke duk’e.. Yakai hannu ya dafasa.
Daddy na d’agowa da yaga Mu’azzam d’in sai ya kuma jin rauni can k’asar zuciyarsa..
A hankali Mu’azzam ya duk’a ya rik’o hannayen Daddy cikin nasa “Baka gaza ba Daddy.. What was meant to happen happened. Kuma Ka kula da bayan mahaifina kaman yanda kayi alk’awari.. Daidai da rana guda baka fasa cika alk’awarinka ba.. You’re true definition of a good brother Daddy... You’ve been taking care of us ever since my father passed.. You’ve become a father to his children and a husband to his wife wacce tin sanda ka aureta Allah ya jarabceta da jinya.. I’ve seen a lot of men wad’anda idan matansu Sun kamu da cuta irin haka har gida suke maidasu suje suyi jinya wasu ma auren ya k’are.. But bakayi haka ba Daddy.. Kai d’in ka d’auki d’awainiyar jinyarta kuma ka kula da ita daidai da rana guda baka gaza ba..”
Saurin girgiza kai Daddy yai yana mai duban Mu’azzam d’in “Don’t say those words Mu’azzam dik abinda nayi nauyi ne da ya rataya a wuyana and it’s not a favor kaji koh.. Come here..” Ya k’arashe yana rungumar Mu’azzam d’in.
Uncle Salman dake tsaye jikin k’ofa da ido ya tsaresu, lokaci guda ya koma da baya ba tareda ya bari sun gansa ba.
**
SULEJA
Tashin hankali goma da ashirin shine abinda Sadiya da ahalinta ke fuskanta, a yayinda mahaifinsu ko rufa kwanaki uku baiyi ba da mutuwa Tabawa ta kuma sakosu gaba da maganan biyan kud’inta.. Babu yanda Umma batai ba ta bari ko takaba ne ta gama idan yaso sai ta fita ta nemo mata kud’ad’enta ko wani aikin ne sai tayi ta samo mata kud’ad’enta..
Tabawa tace atafau ita bataji ba bata gani ba. Yo wani irin aiki ne ma zatayi ta samo mata kud’ad’enta idan ba Sana’ar bin maza data d’aura ‘yarta akai zasuyi Su biyata kud’ad’enta ba.. Wanann magana na Tabawa sosai ya tab’a Zuciyar Umman Sadiya.. Abinda batayi tin k’uruciya ba shine Tabawa take jifanta da munanan kalamai irin haka.. Ya zama dole Ta nemo wa Tabawa kud’ad’enta dan abin ya zama akwai tab’a mutunci da tozarci bazata bari Ta kuma traumatizing yaranta ba bayan tashin hankalin rashin mahaifinsu da suke ciki already.. Hakan yasa Umma yanke shawarin tink’aran Committee na masallacin unguwa ko da akwai irin taimakon da zasu masu su rabu da Tabawa.. Malam Liman ya gyara zama had’ida nusawa kad’an yace “Da farko nasiha zan fara maki da ita.. Ita wannan rayuwar da kuke gani duka ba yawa bace da ita, sannan dik halinda bawa zai tsinci kansa ciki jarabawa ake masa.. Bazai yuwu ace koda Yaushe mun samu abinda muke so ba.. Sannan Ko yatsunmu muka duba ba daidai bane wani yafi wani toh haka Ubangiji ya tsara mana rayuwarmu.. Wani yafika kaima kafi wani.. Kai wani arzikin lafiya ma kawai yake nema dikda d’imbin tarin dukiyar da yake dashi wanda zai iya kashe ko nawa ne domin ya samu wannan lafiyar amma bai samu ba.. Ga dukiyar Allah ya basa amma babu lafiya da zaiji dad’in dukiyar.. Kaikuma idan ka dubi kanka kaga Allah ya huwace maka wannan lafiyan sai kayi tunanin ya gama baka babban arziki.. Har kullum idan zamuke duba rayuwar na sama damu toh fah bazamu tab’a gode ma Allah da tarin ni’imomin da ya mana ba.. Amma idan muka dubi na k’asa damu sai muyi masa godiya da ni’imominsa garemu.. Shi kuma Sai ya k’ara mana domin fad’insa da yace _’Idan kuka gode Mun Ni kuma Zan k’ara maku_.’ “
Umma na matsan k’walla cikin hijabinta take jinjina kai “Haka ne Malam.. Kuma in sha Allahu mun d’auki darasi.. Ina kuma fatan masu halin kwad’ayi irin nawa abinda ya faru dani da d’iyata ya zamto izna garesu..” Kuka ya hanata ci gaba da magana
Malam Liman yace “Ki daina kuka in sha Allah Committee na masallaci zatayi iya k’ok’arinta ta had’o abinda za’a iya samu a baku ku rage bashin.. Ubangiji ya dafa mana gaba d’aya..”Ya k’arashe yana mai mik’ewa ya kuma yima Umma ta’aziya kafin ya fice.
Sadiya tai tagumi tana duban mahaifiyarta, ga k’annenta dake gefe har lokacin kuka suke. Hawaye suka kuma gangaro mata tana tina mahaifinta da k’alubale na rayuwa da suka fuskanta.. Inama mahaifinta zai dawo gareta da ta kasance irin d’iyar da yake so ta zama.. Amma saidai shi lokaci baya jira, idan ya wuce ya wuce kenan har abada..