Sashe 29
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yabi bayanta da kallo zuciyarsa fari k’al, kad’a Kai yai yace a fili “Bari dai naita lallab’a ki har ki shigo...” Yana ida fad’in haka ya gyad’a Kai yana mai kuma Washe baki ya shige.
**
Washe gari sassafe Tabawa tai kiran Asabe mai kayan Koli.
Tabawa ta k’irgo kud’ad’e cikin wanda Alhaji Isyaku ya bata, Ta mik’awa Asabe Mai kayan Koli tace “Kina jina dik abinda na sanar dake haka zaki sanar da matarsa.. Asabe koda wasa kar ki ce ni na sanar dake..”
Asabe Ta jinjina kai tana tura kud’in cikin posar ta. “Haba Hajiya Tabai, indai dan wannan ne ai bakida matsala, da Asabe fah kike zancen..”
Tabawa ta murmusa cikeda jin dad’i tace “Yauwa tawan.. Idan har hak’ata ta cimma ruwa zan k’ara miki wani abu..” Asabe Ta Washe baki cikeda farin ciki.. Tuni ta aza kayanta na Koli aka ta nufi layin gidan Alhaji Isyaku.
Tabawa tabi bayanta da kallo zuciyarta fari k’al. A fili take furta “Alhaji Isyaku kenan ai wllhi bazan bari ka auri yarinyar nan ba, auren nan saidai ayi dani Koda zaka biya masu bashin amma bakada mata sai ni Tabawa. Zan d’aga masu hankali dan ka biya masu bashi sannan zan sa matarka da d’iyarka su d’aga masu hankali suk’i amincewa da buk’atarka bayan ka biya masu bashin..” Tana ida fad’in haka ta bushe da muguwar dariya kafin ta shige gida.
**
Maman Sabeera na zaune parlor tana kallon shirin good morning Nigeria da ake nunawa da sanyin safiya a tashar NTA Asabe mai kayan Koli tai sallama.
Iyatu mai masu aikatau ce ta amsa mata sallamar tace ta jira ta shiga ta tambayi Hajiya idan zata sayi wani abin.
Asabe tace “Dakata ba saye da sayarwa ya kawoni na ba.. Alhaji na gida Ko ya fice..?”
Iyatu tai jim kafin tace “Ai Jiya Alhaji bai dawo gida ba inaga wajen aiki ya kwana..”
Asabe ta zaro ido waje tace “Bai kwana gida ba..? Ikon Allah Toh ki shiga kice mata magana nazo mata dashi mahimmiya kan maigidanta.”
Iyatu ta dubeta da mamaki amma sai ta jinjina kai tace “Shikenan.” Lokaci guda ta shige ta nufo parlor ta tadda Maman Sabeera ta sanar da ita abinda Asabe mai Kayan Koli ta fad’a mata.
Mamaki ya cika Maman Sabeera jin Wai magana Asabe tazo mata dashi kan mijinta. Ta nusa tana tinani kafin taceda Iyatu “Kice mata Ta shigo.”
Iyatu ta jinjina kai kafin ta fice yin iso ma Asabe.
Jim kad’an Asabe ta shigo d’aikeda kayan Kolinta, ta nemi waje daga k’asa ta zauna tana gaida Maman Sabeera.
Maman Sabeera Ta dubeta da mamaki tace “Asabe kikace yau ba talla kikazo ba.. Toh wani magana ne ya kawo ki kan maigidana.?”
Asabe Ta d’an Tab’e baki tana ‘yan waige waige tace “Hmm ai Hajiya abinda nazo dashi yau yafi k’arfin talla.. Amma Hajiya jiya Kinsan yanda mijinki ya kwana..?”
Da tsananin mamaki Maman Sabeera ke dubanta ganin basu saba irin wannan batu ba, iyakaci ta shigo da kayan kolinta ta tallata ta fice. Amma yau Asabe tazo mata da batu mai girma.
Girgiza kai kad’an Maman Sabeera tai “Ban.. Fahimceki ba Asabe.. Mai kike nufi..?”
Asabe ta kuma gyara zama tana duban Maman Sabeera “Hajiya wllhi wllhi abinda zan fad’a miki Sai ya firgitaki.. Idan dai har bakisan yanda mijinki ya kwana jiya ba kuma bakisan da wa ya kwana ba ni zan sanar dake dan na sani..”
Zuciyar Maman Sabeera yaci gaba da bugawa cikin sauri, mijinta ya saba kwana cikin Abuja idan dare ya masa sabida tsananin holdup da cinkoson Abuja yakan sa wataran ya kwana ga yanda k’asar Ta koma babu tsaro, wataran yakan ce aiki ya rik’esa zai kwana cikin Abuja da safe ya dawo. Amma koda wasa bata tab’a saka ma ranta cewa mijinta na ha’intarta ba tuni ta kyautata masa zato tinda ma kafin ya kwana cikin Abujan Sai ya kirata ya sanar da Ita cewa zai kwana aiki ya rik’esa gudun Karma zargi ko abu mai kama da haka ya shiga tsakaninsu. Cikin rashin yarda da batun Asabe Ta mik’e tana nuna ma Asabe k’ofa “Kinga Asabe tashi kawai ki fice.. Kafin ranmu gaba d’aya ya b’aci.. Tashi ki fice min a gida ni bana shiga gulma da gutsiri tsomen unguwar nan.. Tashi ki fice min a gida kuma kar ki sake dawowa idan da irin batun nan zaki Zo..”
Asabe Ta murmusa tace “Hajiya wllhi Allah na rantse miki da Allah daren jiya mijinki na unguwar nan kuma nasan da wa yake tare.. Ni ganau ce ba jiyau ba, na gansa da yarinyar nan Sadiya kuma yau kusan kwanaki uku kenan yana zarya k’ofar gidansu.. Ina mai tabbatar miki d’aukanta yayi suka fice suka kwana tare.. Ai dai Kinsan wacece Sadiya a unguwar nan Sadiya Sady Pretty da tai k’aurin suna wajen rab’an maza masu abin duniya.. Toh ta fad’o kan mijinki zata k’wak’wale abin hannunsa.. Dan wllhi jiya tare na gansu kaman zai mata sijadda dan biyayya..”
Bibbiyu Maman Sabeera ta soma gani, hazo hazo da wani irin duhuwa ne suka gifta k’wayar idanunta. A yayinda Sabeera da fitowarta kenan daga kitchen rik’eda mug dik taji tattaunawarsu a kunnuwanta.. Wani irin k’ara ta saki had’ida sake mug d’in dake hannunta ya watse saman tiles..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*18*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Da kuka Sabeera ta k’araso gabansu tana fad’in “A’a badai Babana ba.. Badai k’awata Sadiya ba.. Mama kar ki yarda da maganar wannan matar I’m sure k’arya take.. Ki tashi.. Tashi ki fice mana daga gida..!” Tai maganar tana k’ok’arin finciko Asabe dake duk’e wajen ta zuba masu ta mujiya.
Maman Sabeera kam tama kasa tantance abinda ke faruwa. Kaman daga wani duniyar take sinkayo kukan Sabeera da maganganunta.
Asabe ta mik’e tana fad’in “Idan k’arya nake maku ku tare mutanen lungunsu ku tambayesu ko kuma kuje da kanku dan ance zuwa dakai yafi sak’o. Nidai na gama nawa tinda sanar daku.. Ya rage naku ku yarda ko kar ku yarda. Allah bamu alheri.” Tana ida fad’in haka ta mik’e ta aza bahon kayan Kolinta aka Ta nufo waje, tuni Ta cika ma rigarta iska aka bar Sabeera da Mamanta babu mai iya ba ma wani hak’uri. Cikin muryar kuka Sabeera ke duban mahaifiyarta tana fad’in “Mama k’arya take kar ki yarda da ita.. Wllhi nayi imani Sadiya bazata tab’a aikata haka ba.. Nasan Sadiya nasan halinta wllhi sharri ne kawai irinta mutanen unguwar nan.. Mama dan Allah Kema kice min baki yarda ba..!”
Maman Sabeera bata iya furta koda kalma ba sai hawaye dake zarya saman k’uncinta. Cikin sauri ta mik’e ta nufi d’aki tana jin kukan da gaske na zuwa mata. Sabeera tabi bayanta da sauri tana kiranta amma inaa bata ko tsaya ba balle ta saurari Sabeera ta shige d’aki kayanta.
Silalewa Sabeera tai a wajen kukanta na k’aruwa itama. Hiran wasu course mates d’insu take tinawa data sinkaya wataran a makaranta cewa akasari ba duka ba iyaye da suka faye tak’ura da tsanani ka bincika ta yuyu shima watsewarsa yake da yaran wasu baiso ayi da nasa shiyasa yake masu mugun tsanani. Tai saurin toshe kunnuwanta tana girgiza kai dan bata so ta amince da hakan.. Wani tinanin ne ya kuma d’arsuwa mata a zuciya.. Ita kad’ai ta aminta da Sadiya, itace bata mata kallon da sauran mutane suke mata a unguwar.. Ta yarda da ita d’ari bisa d’ari sannan ta saka ma ranta cewa Sadiya ba mutuniyar banza bace but Maiyasa yanzu take jin shakku akan hakan.. Kardai da gaske Sadiya cin amanarta take.. Take taji zuciyarta na wani irin bugawa, gwara taji labarin mahaifinta na neman wata daban badai Sadiya k’awarta data d’auki yarda ta d’aura mata ba.. Waima tsaya mahaifinta ya mata iyaka da Sadiya ta ya za’a ce su biyu d’in suna tare.. Cikin sauri ta shiga girgiza kai tana furta “No.. no .. no I can’t take this anymore.. I need to find out myself..” Tana ida fad’in haka Ta mik’e Ta nufi nata d’akin dan shiryawa.
Cikin kuka Maman Sabeera ta kirawo k’awarta Ramatu a waya tana sanar da ita tashin hankalin da suka wayi gari dashi, a fujajan Ramatu tace gata tafe maganar yafi k’arfin ayita a waya dan dama basuda nisa unguwar tasu.
Sabeera kaw tuni ta fice dikda mahaifinta ya mata iyaka da waje balle gidansu Sadiya tin bayan abinda ya faru. Ta’aziyan mahaifinsu ne kawai Mamanta Ta mata cover suka tafi tare. Tafiya Sabeera take a layin tana jin zuciyarta na mata wani irin d’aci, babu addu’an da take cikin zuciyarta face Allah yasa duk abubuwan nan da taji k’arya ne babu gaskiya ko guda a ciki.. Bata jin zuciyarta zata iya d’aukan cin amana daga babban aminiyarta irin Sadiya wacce ta d’auki yarda da komai ta d’aura mata. Tana tafe tana tinanin tazo wuce shagon Maman Emeka ai kuwa saiga wasu ‘yanmata ‘yan unguwar a k’ofar Kantin sun Sai bredi da dangin abin kari kumallo.. D’ayar ta tab’a d’ayar tana nuna mata Sabeera dake had’a hanya zata nufi lungun gidansu Sadiya.
Cikin azama suka nufo Sabeera suna kiran sunanta, taja Ta tsaya tana dubansu da idanunta da tuni sun kod’e sunyi ja dan kuka..
“Laa Sabeera ina kika nufa..? Kardai gidansu Sady Pretty..” Ta d’an tab’e baki kad’an yace “Ai kuwa ko Jiya naga Babanki k’ofar gidan yana zance kuma kaman Sady Pretty na gani..”
D’ayan ta cab’i zancen da fad’in “Ni da naga motar Babanta bakin lungun ma nayi zaton Sabeerar ce ashe ashe dai Baba ne..”
Cikin tsananin huci Sabeera ke dubansu, ta kasa magana sai dubansu da idanu da take.. ‘Yanmatan suka dubi juna kafin d’ayar ta tab’e baki ta janyo hannun ‘yaruwar tata tana fad’in “Kinga k’awata Zo muje.. Allah dai ya kyauta k’awancen cin amana..”
Tamkar wacce aka dasa dutse haka Sabeera ta tsaya a wajen.. Shikenan dai Wato ta tabbata da gaske Mahaifinta saurayin Sadiya ne.. Kuma ko da wasa bata tab’a hasasho hakan ba, bata tab’a tunanin hakan ka iya kasancewa ba.. Da k’yar take d’aga k’afafunta tana ganin hanya na rabe mata bibbiyu.. A haka Ta k’araso gidansu Sadiya.
Sadiya da Umma na zaune tsakar gidan tana duba k’afar Umma da har yanzu yake d’an mata ciwo, tamkar wacce aka jefota haka sukaga Sabeera akansu..
**
Washe gari sassafe Tabawa tai kiran Asabe mai kayan Koli.
Tabawa ta k’irgo kud’ad’e cikin wanda Alhaji Isyaku ya bata, Ta mik’awa Asabe Mai kayan Koli tace “Kina jina dik abinda na sanar dake haka zaki sanar da matarsa.. Asabe koda wasa kar ki ce ni na sanar dake..”
Asabe Ta jinjina kai tana tura kud’in cikin posar ta. “Haba Hajiya Tabai, indai dan wannan ne ai bakida matsala, da Asabe fah kike zancen..”
Tabawa ta murmusa cikeda jin dad’i tace “Yauwa tawan.. Idan har hak’ata ta cimma ruwa zan k’ara miki wani abu..” Asabe Ta Washe baki cikeda farin ciki.. Tuni ta aza kayanta na Koli aka ta nufi layin gidan Alhaji Isyaku.
Tabawa tabi bayanta da kallo zuciyarta fari k’al. A fili take furta “Alhaji Isyaku kenan ai wllhi bazan bari ka auri yarinyar nan ba, auren nan saidai ayi dani Koda zaka biya masu bashin amma bakada mata sai ni Tabawa. Zan d’aga masu hankali dan ka biya masu bashi sannan zan sa matarka da d’iyarka su d’aga masu hankali suk’i amincewa da buk’atarka bayan ka biya masu bashin..” Tana ida fad’in haka ta bushe da muguwar dariya kafin ta shige gida.
**
Maman Sabeera na zaune parlor tana kallon shirin good morning Nigeria da ake nunawa da sanyin safiya a tashar NTA Asabe mai kayan Koli tai sallama.
Iyatu mai masu aikatau ce ta amsa mata sallamar tace ta jira ta shiga ta tambayi Hajiya idan zata sayi wani abin.
Asabe tace “Dakata ba saye da sayarwa ya kawoni na ba.. Alhaji na gida Ko ya fice..?”
Iyatu tai jim kafin tace “Ai Jiya Alhaji bai dawo gida ba inaga wajen aiki ya kwana..”
Asabe ta zaro ido waje tace “Bai kwana gida ba..? Ikon Allah Toh ki shiga kice mata magana nazo mata dashi mahimmiya kan maigidanta.”
Iyatu ta dubeta da mamaki amma sai ta jinjina kai tace “Shikenan.” Lokaci guda ta shige ta nufo parlor ta tadda Maman Sabeera ta sanar da ita abinda Asabe mai Kayan Koli ta fad’a mata.
Mamaki ya cika Maman Sabeera jin Wai magana Asabe tazo mata dashi kan mijinta. Ta nusa tana tinani kafin taceda Iyatu “Kice mata Ta shigo.”
Iyatu ta jinjina kai kafin ta fice yin iso ma Asabe.
Jim kad’an Asabe ta shigo d’aikeda kayan Kolinta, ta nemi waje daga k’asa ta zauna tana gaida Maman Sabeera.
Maman Sabeera Ta dubeta da mamaki tace “Asabe kikace yau ba talla kikazo ba.. Toh wani magana ne ya kawo ki kan maigidana.?”
Asabe Ta d’an Tab’e baki tana ‘yan waige waige tace “Hmm ai Hajiya abinda nazo dashi yau yafi k’arfin talla.. Amma Hajiya jiya Kinsan yanda mijinki ya kwana..?”
Da tsananin mamaki Maman Sabeera ke dubanta ganin basu saba irin wannan batu ba, iyakaci ta shigo da kayan kolinta ta tallata ta fice. Amma yau Asabe tazo mata da batu mai girma.
Girgiza kai kad’an Maman Sabeera tai “Ban.. Fahimceki ba Asabe.. Mai kike nufi..?”
Asabe ta kuma gyara zama tana duban Maman Sabeera “Hajiya wllhi wllhi abinda zan fad’a miki Sai ya firgitaki.. Idan dai har bakisan yanda mijinki ya kwana jiya ba kuma bakisan da wa ya kwana ba ni zan sanar dake dan na sani..”
Zuciyar Maman Sabeera yaci gaba da bugawa cikin sauri, mijinta ya saba kwana cikin Abuja idan dare ya masa sabida tsananin holdup da cinkoson Abuja yakan sa wataran ya kwana ga yanda k’asar Ta koma babu tsaro, wataran yakan ce aiki ya rik’esa zai kwana cikin Abuja da safe ya dawo. Amma koda wasa bata tab’a saka ma ranta cewa mijinta na ha’intarta ba tuni ta kyautata masa zato tinda ma kafin ya kwana cikin Abujan Sai ya kirata ya sanar da Ita cewa zai kwana aiki ya rik’esa gudun Karma zargi ko abu mai kama da haka ya shiga tsakaninsu. Cikin rashin yarda da batun Asabe Ta mik’e tana nuna ma Asabe k’ofa “Kinga Asabe tashi kawai ki fice.. Kafin ranmu gaba d’aya ya b’aci.. Tashi ki fice min a gida ni bana shiga gulma da gutsiri tsomen unguwar nan.. Tashi ki fice min a gida kuma kar ki sake dawowa idan da irin batun nan zaki Zo..”
Asabe Ta murmusa tace “Hajiya wllhi Allah na rantse miki da Allah daren jiya mijinki na unguwar nan kuma nasan da wa yake tare.. Ni ganau ce ba jiyau ba, na gansa da yarinyar nan Sadiya kuma yau kusan kwanaki uku kenan yana zarya k’ofar gidansu.. Ina mai tabbatar miki d’aukanta yayi suka fice suka kwana tare.. Ai dai Kinsan wacece Sadiya a unguwar nan Sadiya Sady Pretty da tai k’aurin suna wajen rab’an maza masu abin duniya.. Toh ta fad’o kan mijinki zata k’wak’wale abin hannunsa.. Dan wllhi jiya tare na gansu kaman zai mata sijadda dan biyayya..”
Bibbiyu Maman Sabeera ta soma gani, hazo hazo da wani irin duhuwa ne suka gifta k’wayar idanunta. A yayinda Sabeera da fitowarta kenan daga kitchen rik’eda mug dik taji tattaunawarsu a kunnuwanta.. Wani irin k’ara ta saki had’ida sake mug d’in dake hannunta ya watse saman tiles..
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*18*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Da kuka Sabeera ta k’araso gabansu tana fad’in “A’a badai Babana ba.. Badai k’awata Sadiya ba.. Mama kar ki yarda da maganar wannan matar I’m sure k’arya take.. Ki tashi.. Tashi ki fice mana daga gida..!” Tai maganar tana k’ok’arin finciko Asabe dake duk’e wajen ta zuba masu ta mujiya.
Maman Sabeera kam tama kasa tantance abinda ke faruwa. Kaman daga wani duniyar take sinkayo kukan Sabeera da maganganunta.
Asabe ta mik’e tana fad’in “Idan k’arya nake maku ku tare mutanen lungunsu ku tambayesu ko kuma kuje da kanku dan ance zuwa dakai yafi sak’o. Nidai na gama nawa tinda sanar daku.. Ya rage naku ku yarda ko kar ku yarda. Allah bamu alheri.” Tana ida fad’in haka ta mik’e ta aza bahon kayan Kolinta aka Ta nufo waje, tuni Ta cika ma rigarta iska aka bar Sabeera da Mamanta babu mai iya ba ma wani hak’uri. Cikin muryar kuka Sabeera ke duban mahaifiyarta tana fad’in “Mama k’arya take kar ki yarda da ita.. Wllhi nayi imani Sadiya bazata tab’a aikata haka ba.. Nasan Sadiya nasan halinta wllhi sharri ne kawai irinta mutanen unguwar nan.. Mama dan Allah Kema kice min baki yarda ba..!”
Maman Sabeera bata iya furta koda kalma ba sai hawaye dake zarya saman k’uncinta. Cikin sauri ta mik’e ta nufi d’aki tana jin kukan da gaske na zuwa mata. Sabeera tabi bayanta da sauri tana kiranta amma inaa bata ko tsaya ba balle ta saurari Sabeera ta shige d’aki kayanta.
Silalewa Sabeera tai a wajen kukanta na k’aruwa itama. Hiran wasu course mates d’insu take tinawa data sinkaya wataran a makaranta cewa akasari ba duka ba iyaye da suka faye tak’ura da tsanani ka bincika ta yuyu shima watsewarsa yake da yaran wasu baiso ayi da nasa shiyasa yake masu mugun tsanani. Tai saurin toshe kunnuwanta tana girgiza kai dan bata so ta amince da hakan.. Wani tinanin ne ya kuma d’arsuwa mata a zuciya.. Ita kad’ai ta aminta da Sadiya, itace bata mata kallon da sauran mutane suke mata a unguwar.. Ta yarda da ita d’ari bisa d’ari sannan ta saka ma ranta cewa Sadiya ba mutuniyar banza bace but Maiyasa yanzu take jin shakku akan hakan.. Kardai da gaske Sadiya cin amanarta take.. Take taji zuciyarta na wani irin bugawa, gwara taji labarin mahaifinta na neman wata daban badai Sadiya k’awarta data d’auki yarda ta d’aura mata ba.. Waima tsaya mahaifinta ya mata iyaka da Sadiya ta ya za’a ce su biyu d’in suna tare.. Cikin sauri ta shiga girgiza kai tana furta “No.. no .. no I can’t take this anymore.. I need to find out myself..” Tana ida fad’in haka Ta mik’e Ta nufi nata d’akin dan shiryawa.
Cikin kuka Maman Sabeera ta kirawo k’awarta Ramatu a waya tana sanar da ita tashin hankalin da suka wayi gari dashi, a fujajan Ramatu tace gata tafe maganar yafi k’arfin ayita a waya dan dama basuda nisa unguwar tasu.
Sabeera kaw tuni ta fice dikda mahaifinta ya mata iyaka da waje balle gidansu Sadiya tin bayan abinda ya faru. Ta’aziyan mahaifinsu ne kawai Mamanta Ta mata cover suka tafi tare. Tafiya Sabeera take a layin tana jin zuciyarta na mata wani irin d’aci, babu addu’an da take cikin zuciyarta face Allah yasa duk abubuwan nan da taji k’arya ne babu gaskiya ko guda a ciki.. Bata jin zuciyarta zata iya d’aukan cin amana daga babban aminiyarta irin Sadiya wacce ta d’auki yarda da komai ta d’aura mata. Tana tafe tana tinanin tazo wuce shagon Maman Emeka ai kuwa saiga wasu ‘yanmata ‘yan unguwar a k’ofar Kantin sun Sai bredi da dangin abin kari kumallo.. D’ayar ta tab’a d’ayar tana nuna mata Sabeera dake had’a hanya zata nufi lungun gidansu Sadiya.
Cikin azama suka nufo Sabeera suna kiran sunanta, taja Ta tsaya tana dubansu da idanunta da tuni sun kod’e sunyi ja dan kuka..
“Laa Sabeera ina kika nufa..? Kardai gidansu Sady Pretty..” Ta d’an tab’e baki kad’an yace “Ai kuwa ko Jiya naga Babanki k’ofar gidan yana zance kuma kaman Sady Pretty na gani..”
D’ayan ta cab’i zancen da fad’in “Ni da naga motar Babanta bakin lungun ma nayi zaton Sabeerar ce ashe ashe dai Baba ne..”
Cikin tsananin huci Sabeera ke dubansu, ta kasa magana sai dubansu da idanu da take.. ‘Yanmatan suka dubi juna kafin d’ayar ta tab’e baki ta janyo hannun ‘yaruwar tata tana fad’in “Kinga k’awata Zo muje.. Allah dai ya kyauta k’awancen cin amana..”
Tamkar wacce aka dasa dutse haka Sabeera ta tsaya a wajen.. Shikenan dai Wato ta tabbata da gaske Mahaifinta saurayin Sadiya ne.. Kuma ko da wasa bata tab’a hasasho hakan ba, bata tab’a tunanin hakan ka iya kasancewa ba.. Da k’yar take d’aga k’afafunta tana ganin hanya na rabe mata bibbiyu.. A haka Ta k’araso gidansu Sadiya.
Sadiya da Umma na zaune tsakar gidan tana duba k’afar Umma da har yanzu yake d’an mata ciwo, tamkar wacce aka jefota haka sukaga Sabeera akansu..