Sashe 93
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ji yai hannunta guda ya sauk’a saman nasa hannun dake d’aure kan na mahaifiyarsa.. Ya dubi hannayen nasu d’aya bisa d’aya. Nasa saman na mahaifiyarsa saiko na matarsa sadiya da ta aza saman nasa hannun. Ya d’ago yana duban fuskarta da hawaye ke gangarowa. A hankali ta soma fad’in “Allah baya d’aura ma rai abinda bazata iya ba. In sha Allah zata sami lafiya.. Kar ka yanke tsammani daga rahamar Ubangiji kaji.. Da izinin Allah zata sami lafiya ta zamto Tamkar bata kwanta jinyar nan ba.. Muyi fatan jinya ya zamto mata kaffaran kura kurai kaji..!” Tana maganar hawaye na gangaro mata cikin yanayin muryar mai tsananin rauni.
Ya jinjina mata kai a hankali yana mai sakin murmushi “In sha Allah..!” Ya furta yana duban idanunta kafin ya d’ago d’aya hannunsa ya shiga goge mata hawayenta.
Yana goge mata hawayen yake fad’in “Kinsan cewa itace sanadiyar had’uwarmu..?”
D’an duban fuskarsa tai tana mai son Ganin k’wayar idanunsa.
“Kace Itace sanadiyar had’uwarmu.?” Sadiya ta tambaya tana dubansa dikda cewa shid’in ba cikin idanunta yake duba ba fuskarta yanda yatsun hannunsa ke sauk’a yana goge mata hawayen nan yake duba.
A hankali ya jinjina mata kai kafin yace “Nayi alk’awari wa Mamy cewa matuk’a Ina aikin D’ansanda zan zak’ulo wanda duk ya kashe mata d’iyarta Ikram da izinin Allah.. A ta dalilin binciken mutuwar Ikram na had’u dake har ta kaimu ga aure.. Kinga Mamy tana cikin sanadi.” Ya k’arashe yana mai sauk’e k’wayar idanunsa cikin nata.
Ta janye nata idanunta daga barin duban nasa tana mai sakin murmushi a hankal.
Murmushin shima yasaki kafin ya maido da dubansa ga mahaifiyarsa.
Ya kuma rik’e hannun mahaifiyar tasa dake bacci cikin nasa kafin ya soma fad’in “Mamy.. Ga d’iyarki na kawo miki ku gaisa..” Sai ya d’anyi fasali ya karkato yana duban Sadiya. Lokaci guda yaci gaba da furta “Although She’s the most stubborn person I’ve ever met.. Ko cikin mutanen da nake gwagwarmaya dasu a interrogation room, ban tab’a cin karo da stubborn person irinta ba..” Ji yai ta mintsili hannunsa dake cikin nata.
Ya d’an saki k’ara yana dubanta yanda ta firfito da idanu waje.
Lokaci guda take girgiza masa kai kafin tace “That’s not true..” Ta fad’i kaman zatai kuka.
“Ok nayi shiru kar na fad’a..? Baki so Mamy taji halin ‘yar nata ne..?”
Tai narai narai da idanu had’ida mak’e masa kafad’a alamun a’a.
Yai intertwining yatsun hannayensu kafin yace “Bribe me idan baki so na fad’a mata..”
Ta zaro ido waje tace “D’an sanda da karb’an cin hanci da rashawa..?” Tai maganar a hankali kaman mai tsoron kar Mamayn ta jita.
Ya kashe murya kad’an shima kafin yace “Believe me this one is allowed..” Ya fad’i yana kashe mata ido guda. Hakan yayi daidai da shigowar Inne sallama saman bakinta.
Suka amsa mata sallamar Sadiya na cire hannunta daga nasa. Ta gyara zamanta sosai daga nan yanda take zaune gaban gadon Mamy.
Inne ta k’araso tana tambayarsu ko Mamyn tayi bacci.
Mu’azzam ya bata amsa da fad’in tayi bacci ai.
Inne ta jinjina kai kafin ta dubi Sadiya da ta sadda kanta k’asa lullub’e da mayafi sai kuma ta dubi Mu’azzam tace “Zata kwana wajena gobe idan Allah ya kaimu da yammaci a kaita d’akinta kaman yanda aka saba a al’ada.. Ba wani taro za’ai ba duba da yanayin jikin Nuratu.. ‘Yan uwa k’alilan ne zasu mata rakiya zuwa d’akinta kaji koh..”
A hankali ya furta “Toh Inne..” Kana jin yanda ya amsa kasan a dole ya amsa hakan.
Inne ta dubi Sadiya tace “Tashi maza kije koh.. Idan kina son wani abin ki fad’awa Hindu kinji koh.. Ki saki jikinki nan gida ne kinji koh..”
Sadiya ta sadda kanta tana mai amsawa da “Toh Inne..”
Tana tafe yana binta da Kallo har ta b’acewa ganinsa. Inne na hankalce dashi.
Ganin Inne shi take duba ya d’an sanyashi sosa kai kad’an.
“Mu’azzam..”
“Na’am Inne..” Ya amsa yana dubanta dan tinda yaji batace Modibbo ba ta kirasa da sunansa kai tsaye yasan magana ce mai girma zata masa.
Inne ta juya ta nufi parlor tana fad’in “Biyo ni muyi magana.”
Babu musu ya mik’e yabi bayanta.
A nan parlorn Aunty Nuratun suka zauna, Inne ta tsaresa da idanu.
Ya d’an sadda kansa kad’an ba tareda yace komai ba.
“Magana nake so muyi kan Safeenah..”
Yanajin ta ambaci Safeenah a ransa yace anzo wajen.
Inne taci gaba da fad’in “Safeenah ta kirani tana kuka.. Kasan bana d’aukan shashashancin Safeenah amma abinda ta sanar dani cikin waya ya matuk’ar d’aga mun hankali had’ida bani mamaki.. Mu’azzam kana cikin hankalinka zaka furta kalmar saki wa matarka kuma ‘yaruwarka a cikin gidan Mahaifinta.. Gaban mahaifiyarta da kowa nata dan kawai kayi sabon aure..? Babu wanda zai hanaka aure kuma babu wanda zai hanaka d’aukar matarka ka tafi da Ita yanda kake so.. Amma Safeenah tace mun kan kawai tace itama sai ta biyoka shine ka furta cewa ka saketa saikace wata ‘yar tsana.. Haba Mu’azzam saki fah ba k’aramin abu bane.. Ba’a wasa da saki.. Cikin gidan nan kaf wa kaga ya taso yana haka.. Mu ba’a mana wannan shaida ba. Mata hak’uri ake dasu, sabida Kai namiji ne tinanin ka da nasu ba zaizo d’aya ba. Sannan koda mace ta buk’aci saki bazaka biye mata ba.. Dan idan aka biye na mata sai a sakesu sau d’ari musamman idan akan kishiya ce.. Modibbo kishi nada matuk’ar zafi wanda ba Don Allah ne ya hukunta hakan ba kanajin akwai macen da zata amince mijinta ya zauna da wata ce.. A al’amari irin na aure dole a kula da irin haka musamman duba da yanda Kayowa Safeenar wata mata a tsakanin k’ank’anin lokaci.. Banji dad’in abinda ka aikata ba kuma ban amince ka aikata hakan ba saida nasa Safeenah ta bani Hajara a waya ta sanar dani K’warai anyi haka dan kasan bana yarda da wautan Safeenah..” Ta k’arashe cikin b’acin rai.
Tinda ta fara magana kansa ke a k’asa. Saida ya bari ta ida kafin ya d’ago yace “Inne kiyi hak’uri.. Nasan bakiji dad’i ba kuma banso Labarin ya riskeki a irin haka ba.. kiyi hak’uri Inne..” Ya k’arashe cikin kwantar da murya.
Lokaci guda yaci gaba da fad’in “Inne basu sanar dake gaskiyar abinda ya faru ba.. Quite alright na saki Safeenah amma basu sanar dake yanda al’amarin ya kasance ba..”
Inne ta dubesa a d’an karkace kafin tace “Watau dai da gaske dai kayi sakin..”
Mu’azzam ya jinjina kai a hankali kafin yace “Nayi amma ba wancan dalilin da Safeenah ta sanar dake bane ya sanyani yin sakin.. Inne ban saki Safeenah dan nayi wani aure ba sann ban saketa dan zan d’auko Sadiya na taho da ita nan ba..”
Inne ta katsesa da fad’in “Kana nufin k’arya sukai maka kenan..?”
“Kusan haka Inne..”
Inne ta girgiza kai tace “Wai meke faruwa ne Modibbo..?”
Mu’azzam ya gyara zamansa kad’an yana fad’in “Ni banso kiji wann labarin ba.. Dan nasan zai tada miki hankali ne kawai.. Amma tinda ita Safeenar ita ta kiraki ta sanar dake, kuma hakan na nufin ita ta zab’i kiji, zan sanar dake duk abinda ya faru Inne..”
Inne ta gyara zama tana saurarensa.
Tiryan tiryan Mu’azzam ke karanto mata dik abinda ya faru.. Tin daga kulle masa k’ofa da Safeenah tai wanda hakan ya hanasa shiga ya sanar mata tafiyar nasa balle yai mata sallama, har d’auko bindigarsa da tai taima Sadiya barazana da rayuwarta harde da munanan kalaman da ta dinga ambatonsa dashi har dai zuwa harba bindigar jikin garu da Safeenah tai zuwa zab’i data basa tsakaninta da Sadiya.. Ko abu guda bai b’oyewa Inne ba sai zuwan Mommy gidansa da tai tace sai ya saki Safeenah shine kawai bai sanar da Inne ba dan har wannan lokaci Kallon Uwa yakewa Mommy dan yasan ko mai Mommy zata masa bazai tab’a biyan d’awainiyar da sukai masu ba daga ita har Daddy musamman akan mahaifiyarsa. Sam baijin zai iya tozarta Mommy koda mai zata masa.
Inne da take jin abun, shaye da mamaki take dubansa “Safeenah tace da bindiga zata harbi mutum..?”
Mu’azzam yai shiru baici komai ba dan dama ba’a sanar da Innen ba lokacin da aka kama Safeenah ta zama suspect na mutuwar Ikram.
Inne taci gaba da fad’in “Ikon Allah.. Abu kaman a cikin shirin wasan kwaikwayo... Kuma waima duk Ina shi Marwan d’in ake wann rashin hankalin cikin gidansa..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Daddy baya gida shima dawowa yai ya tadda al’amarin..”
Inne ta jinjina kai tace “Yanzu a gidan Marwan ake wannan rashin hankalin.. Ita Safeenah ba’a wauta ta tsaya kawai ba abin nata harda hauka ne..? Wann ai Ba abin yin shiru bane abin a nema mata magani ne dan batada hankali bamu San mai zata aikata gaba ba..”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Inne da hankalinta tasan abinda take.. Attention take nema as always.”
Inne ta jinjina kai tace “Eh Lallai.. Safeenah da harba bindiga..?” Tai maganar tana kuma jinjina lamarin.
Sauk’e ajiyan zuciya yai kafin yace “Inne ki kwantar da hankalinki komai ya shige.. Safeenah bazata sake barazana ma wani da bindiga ba.”
Tsegege take dubansa kafin tace “Idan aka barta gaba sakewa zatai, zan kira shi Marwan d’in naji wani mataki ya d’auka kan haukar Safeenah.. Asibitin mahaukata zai kaita ko ajeta zai a gidansa.. Dan idan a gidansa zai barta gwara ya kawo mun ita nan a sakata a mari da turu ehe..!”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “A’a Inne kar ki kira Daddy please, nasan yanzu haka bayan abinda Safeenah tai gaba d’aya hankalinsa ba’a kwance bane.. Banso hankalin Daddy ya kuma tashi.”
Ta tsaresa da idanu kafin ta murmusa kad’an tace “Kai da Marwan kuna matuk’ar son juna.. Ina Farin ciki da matuk’ar alfahari da hakan.. Badon bansan mai ke rufe cikin zuciya ba da Sai nace kai kafi soyuwa a gareshi sama da nasa yaran.”
Musaddiq dake k’ok’arin shigowa parlorn fasa shiga yai sakamakon abinda ya sinkayo Inne na fad’i.. Tabbas gaskiya ne. Daddy yafi son Mu’azzam sama dasu.. Jiki a sanyaye Musaddiq ya koma da baya ya fasa shiga.
Ya jinjina mata kai a hankali yana mai sakin murmushi “In sha Allah..!” Ya furta yana duban idanunta kafin ya d’ago d’aya hannunsa ya shiga goge mata hawayenta.
Yana goge mata hawayen yake fad’in “Kinsan cewa itace sanadiyar had’uwarmu..?”
D’an duban fuskarsa tai tana mai son Ganin k’wayar idanunsa.
“Kace Itace sanadiyar had’uwarmu.?” Sadiya ta tambaya tana dubansa dikda cewa shid’in ba cikin idanunta yake duba ba fuskarta yanda yatsun hannunsa ke sauk’a yana goge mata hawayen nan yake duba.
A hankali ya jinjina mata kai kafin yace “Nayi alk’awari wa Mamy cewa matuk’a Ina aikin D’ansanda zan zak’ulo wanda duk ya kashe mata d’iyarta Ikram da izinin Allah.. A ta dalilin binciken mutuwar Ikram na had’u dake har ta kaimu ga aure.. Kinga Mamy tana cikin sanadi.” Ya k’arashe yana mai sauk’e k’wayar idanunsa cikin nata.
Ta janye nata idanunta daga barin duban nasa tana mai sakin murmushi a hankal.
Murmushin shima yasaki kafin ya maido da dubansa ga mahaifiyarsa.
Ya kuma rik’e hannun mahaifiyar tasa dake bacci cikin nasa kafin ya soma fad’in “Mamy.. Ga d’iyarki na kawo miki ku gaisa..” Sai ya d’anyi fasali ya karkato yana duban Sadiya. Lokaci guda yaci gaba da furta “Although She’s the most stubborn person I’ve ever met.. Ko cikin mutanen da nake gwagwarmaya dasu a interrogation room, ban tab’a cin karo da stubborn person irinta ba..” Ji yai ta mintsili hannunsa dake cikin nata.
Ya d’an saki k’ara yana dubanta yanda ta firfito da idanu waje.
Lokaci guda take girgiza masa kai kafin tace “That’s not true..” Ta fad’i kaman zatai kuka.
“Ok nayi shiru kar na fad’a..? Baki so Mamy taji halin ‘yar nata ne..?”
Tai narai narai da idanu had’ida mak’e masa kafad’a alamun a’a.
Yai intertwining yatsun hannayensu kafin yace “Bribe me idan baki so na fad’a mata..”
Ta zaro ido waje tace “D’an sanda da karb’an cin hanci da rashawa..?” Tai maganar a hankali kaman mai tsoron kar Mamayn ta jita.
Ya kashe murya kad’an shima kafin yace “Believe me this one is allowed..” Ya fad’i yana kashe mata ido guda. Hakan yayi daidai da shigowar Inne sallama saman bakinta.
Suka amsa mata sallamar Sadiya na cire hannunta daga nasa. Ta gyara zamanta sosai daga nan yanda take zaune gaban gadon Mamy.
Inne ta k’araso tana tambayarsu ko Mamyn tayi bacci.
Mu’azzam ya bata amsa da fad’in tayi bacci ai.
Inne ta jinjina kai kafin ta dubi Sadiya da ta sadda kanta k’asa lullub’e da mayafi sai kuma ta dubi Mu’azzam tace “Zata kwana wajena gobe idan Allah ya kaimu da yammaci a kaita d’akinta kaman yanda aka saba a al’ada.. Ba wani taro za’ai ba duba da yanayin jikin Nuratu.. ‘Yan uwa k’alilan ne zasu mata rakiya zuwa d’akinta kaji koh..”
A hankali ya furta “Toh Inne..” Kana jin yanda ya amsa kasan a dole ya amsa hakan.
Inne ta dubi Sadiya tace “Tashi maza kije koh.. Idan kina son wani abin ki fad’awa Hindu kinji koh.. Ki saki jikinki nan gida ne kinji koh..”
Sadiya ta sadda kanta tana mai amsawa da “Toh Inne..”
Tana tafe yana binta da Kallo har ta b’acewa ganinsa. Inne na hankalce dashi.
Ganin Inne shi take duba ya d’an sanyashi sosa kai kad’an.
“Mu’azzam..”
“Na’am Inne..” Ya amsa yana dubanta dan tinda yaji batace Modibbo ba ta kirasa da sunansa kai tsaye yasan magana ce mai girma zata masa.
Inne ta juya ta nufi parlor tana fad’in “Biyo ni muyi magana.”
Babu musu ya mik’e yabi bayanta.
A nan parlorn Aunty Nuratun suka zauna, Inne ta tsaresa da idanu.
Ya d’an sadda kansa kad’an ba tareda yace komai ba.
“Magana nake so muyi kan Safeenah..”
Yanajin ta ambaci Safeenah a ransa yace anzo wajen.
Inne taci gaba da fad’in “Safeenah ta kirani tana kuka.. Kasan bana d’aukan shashashancin Safeenah amma abinda ta sanar dani cikin waya ya matuk’ar d’aga mun hankali had’ida bani mamaki.. Mu’azzam kana cikin hankalinka zaka furta kalmar saki wa matarka kuma ‘yaruwarka a cikin gidan Mahaifinta.. Gaban mahaifiyarta da kowa nata dan kawai kayi sabon aure..? Babu wanda zai hanaka aure kuma babu wanda zai hanaka d’aukar matarka ka tafi da Ita yanda kake so.. Amma Safeenah tace mun kan kawai tace itama sai ta biyoka shine ka furta cewa ka saketa saikace wata ‘yar tsana.. Haba Mu’azzam saki fah ba k’aramin abu bane.. Ba’a wasa da saki.. Cikin gidan nan kaf wa kaga ya taso yana haka.. Mu ba’a mana wannan shaida ba. Mata hak’uri ake dasu, sabida Kai namiji ne tinanin ka da nasu ba zaizo d’aya ba. Sannan koda mace ta buk’aci saki bazaka biye mata ba.. Dan idan aka biye na mata sai a sakesu sau d’ari musamman idan akan kishiya ce.. Modibbo kishi nada matuk’ar zafi wanda ba Don Allah ne ya hukunta hakan ba kanajin akwai macen da zata amince mijinta ya zauna da wata ce.. A al’amari irin na aure dole a kula da irin haka musamman duba da yanda Kayowa Safeenar wata mata a tsakanin k’ank’anin lokaci.. Banji dad’in abinda ka aikata ba kuma ban amince ka aikata hakan ba saida nasa Safeenah ta bani Hajara a waya ta sanar dani K’warai anyi haka dan kasan bana yarda da wautan Safeenah..” Ta k’arashe cikin b’acin rai.
Tinda ta fara magana kansa ke a k’asa. Saida ya bari ta ida kafin ya d’ago yace “Inne kiyi hak’uri.. Nasan bakiji dad’i ba kuma banso Labarin ya riskeki a irin haka ba.. kiyi hak’uri Inne..” Ya k’arashe cikin kwantar da murya.
Lokaci guda yaci gaba da fad’in “Inne basu sanar dake gaskiyar abinda ya faru ba.. Quite alright na saki Safeenah amma basu sanar dake yanda al’amarin ya kasance ba..”
Inne ta dubesa a d’an karkace kafin tace “Watau dai da gaske dai kayi sakin..”
Mu’azzam ya jinjina kai a hankali kafin yace “Nayi amma ba wancan dalilin da Safeenah ta sanar dake bane ya sanyani yin sakin.. Inne ban saki Safeenah dan nayi wani aure ba sann ban saketa dan zan d’auko Sadiya na taho da ita nan ba..”
Inne ta katsesa da fad’in “Kana nufin k’arya sukai maka kenan..?”
“Kusan haka Inne..”
Inne ta girgiza kai tace “Wai meke faruwa ne Modibbo..?”
Mu’azzam ya gyara zamansa kad’an yana fad’in “Ni banso kiji wann labarin ba.. Dan nasan zai tada miki hankali ne kawai.. Amma tinda ita Safeenar ita ta kiraki ta sanar dake, kuma hakan na nufin ita ta zab’i kiji, zan sanar dake duk abinda ya faru Inne..”
Inne ta gyara zama tana saurarensa.
Tiryan tiryan Mu’azzam ke karanto mata dik abinda ya faru.. Tin daga kulle masa k’ofa da Safeenah tai wanda hakan ya hanasa shiga ya sanar mata tafiyar nasa balle yai mata sallama, har d’auko bindigarsa da tai taima Sadiya barazana da rayuwarta harde da munanan kalaman da ta dinga ambatonsa dashi har dai zuwa harba bindigar jikin garu da Safeenah tai zuwa zab’i data basa tsakaninta da Sadiya.. Ko abu guda bai b’oyewa Inne ba sai zuwan Mommy gidansa da tai tace sai ya saki Safeenah shine kawai bai sanar da Inne ba dan har wannan lokaci Kallon Uwa yakewa Mommy dan yasan ko mai Mommy zata masa bazai tab’a biyan d’awainiyar da sukai masu ba daga ita har Daddy musamman akan mahaifiyarsa. Sam baijin zai iya tozarta Mommy koda mai zata masa.
Inne da take jin abun, shaye da mamaki take dubansa “Safeenah tace da bindiga zata harbi mutum..?”
Mu’azzam yai shiru baici komai ba dan dama ba’a sanar da Innen ba lokacin da aka kama Safeenah ta zama suspect na mutuwar Ikram.
Inne taci gaba da fad’in “Ikon Allah.. Abu kaman a cikin shirin wasan kwaikwayo... Kuma waima duk Ina shi Marwan d’in ake wann rashin hankalin cikin gidansa..?”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Daddy baya gida shima dawowa yai ya tadda al’amarin..”
Inne ta jinjina kai tace “Yanzu a gidan Marwan ake wannan rashin hankalin.. Ita Safeenah ba’a wauta ta tsaya kawai ba abin nata harda hauka ne..? Wann ai Ba abin yin shiru bane abin a nema mata magani ne dan batada hankali bamu San mai zata aikata gaba ba..”
Mu’azzam ya girgiza kai yace “Inne da hankalinta tasan abinda take.. Attention take nema as always.”
Inne ta jinjina kai tace “Eh Lallai.. Safeenah da harba bindiga..?” Tai maganar tana kuma jinjina lamarin.
Sauk’e ajiyan zuciya yai kafin yace “Inne ki kwantar da hankalinki komai ya shige.. Safeenah bazata sake barazana ma wani da bindiga ba.”
Tsegege take dubansa kafin tace “Idan aka barta gaba sakewa zatai, zan kira shi Marwan d’in naji wani mataki ya d’auka kan haukar Safeenah.. Asibitin mahaukata zai kaita ko ajeta zai a gidansa.. Dan idan a gidansa zai barta gwara ya kawo mun ita nan a sakata a mari da turu ehe..!”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “A’a Inne kar ki kira Daddy please, nasan yanzu haka bayan abinda Safeenah tai gaba d’aya hankalinsa ba’a kwance bane.. Banso hankalin Daddy ya kuma tashi.”
Ta tsaresa da idanu kafin ta murmusa kad’an tace “Kai da Marwan kuna matuk’ar son juna.. Ina Farin ciki da matuk’ar alfahari da hakan.. Badon bansan mai ke rufe cikin zuciya ba da Sai nace kai kafi soyuwa a gareshi sama da nasa yaran.”
Musaddiq dake k’ok’arin shigowa parlorn fasa shiga yai sakamakon abinda ya sinkayo Inne na fad’i.. Tabbas gaskiya ne. Daddy yafi son Mu’azzam sama dasu.. Jiki a sanyaye Musaddiq ya koma da baya ya fasa shiga.