Sashe 121
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jiki babu kuzari ya mik’e ya soma had’a botiran rigarsa still wayar manne kunnensa yana fad’in “Ya isa haka, gani nan tahowa.. Kar ki kuskura kice zakiyi driving.. Gani nan zuwa..” Ya k’arashe yana duban Sadiya data tsaresa da idanu alamun bata gane meke faruwa ba.
Peck ya manna mata a gefen kumatu yana mai matsar da bakinsa saitin kunnenta, cikin sigan rad’a ya furta “Wait for me right here kinji koh.” Yai maganar murya a dashe.
Ya mik’e yana duba agogon dake d’aure hannunsa ya nuna 10:30pm. Lokaci guda yake furta “Safeenah needs me now.. Zamuyi magana idan na dawo kinji koh.”
Bata iya amsa sa ba sai nanata abinda yace cikin zuciyarta take. Wai Safeenah ke buk’atarsa.. A cikin daren nan.? toh meke faruwa kenan.? Ji tai jikinta yayi mugun sanyi. A hankali ta kuma nitsewa cikin gadon tana janyo bargo Ta rufa akanta. Har lokacin zuciyarta bai daina tsinkewa ba. Safeenah tana buk’atarsa cikin daren nan? Abinda fah ya fad’a mata kenan.. Sai nanata kalmar take cikin zuciyarta . Ta lumshe idanunta a hankali tana k’ok’arin nitsa zuciyarta. Har lokacin ta Kasa ficewa daga cikin gadon.
**
Yana isowa gidan ya tadda Safeenah ita kad’ai a parlor sai kuka take tana fad’in mararta da bayanta ciwo suke mata. Aiko tana ganin Mu’azzam ta kuma fashewa da wani irin kuka tana ciza labb’anta. Sai yarfe hannu take alamun tana jin jiki.
Ya k’araso cikin sauri ganin ita kad’aice a parlorn. Ya duk’o cikeda kulawa yana dubanta “Tun yaushe ne Bakida lafiya.. Kuma duk gidan nan a rasa mai kaiki asibiti.?”
Cikin yanayi na kuka take fad’in “Musaddiq Bai dawo gida ba.. Ba driver ko d’aya dake kwana a gidan nan yanzu. Meema kuma tun last week ta tafi sch a hostel take zama. (Meema ta samu gurbin karatu a Nile University dake birnin tarayya).
Safeenah taci gaba da kuka tana fad’in “And Mommy yanzu bata iya tuk’i musamman da dare.. Kuma Mommyn da Kiki duk sunyi bacci.. Ni kad’ai aka bari a nan, na tashi zan tafi d’aki naci marata da bayana sun rik’e ko tafiya bazan iya ba.” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya.
Ya d’an girgiza kansa kad’an yace “Tashi muje.. Zaki iya tashi..?”
Ta kuma fashe masa da kuka tana girgiza kai lokaci guda take furta “Bazan iya tashi ba.. Ciwo yake mun..”
D’an sunkuyowa yai yana k’ok’arin kai hannunsa jikinta, sai kuma yaji tana kuma sakin k’ara babu shiri ya tallafota yana fad’in suje.
Safeenah ta Kasa tafiya sai Sabon kukan da ta sakar masa tana kuma d’ingile k’afarta alamun bazata iya tafiya ba.
D’aukanta yai cak ya nufo downstairs da ita. Bai wata wata ba ya sakata a mota yana mata sannu ganin yanda taketa ciza baki tana dafe bayanta da cikinta.
Asibitin da Ta soma ganin Dr tai masa umarni suje.. Suna zuwa kaw Dr d’in yai attending nasu.. Ya duba Safeenah ya bata magunguna.. Mu’azzam ya tambayi ko Babyn na lafiya.. Dr yace yana lafiya amma a dinga kulawa, dama dole zata dinga jin irin wad’ann pains d’in lokaci zuwa lokaci musamman dake cikin k’arami ne ga kuma yanayin da yazo dashi na had’arin ficewa ko wani lokaci.. Abu k’ank’ani zai iya sa cikin ya salwanta.. Saidai a dinga kula.
Mu’azzam yai masa godiya yana jinjina kai ”Za’a kula in sha Allah Dr..”
Sukai masabaha had’ida sallama, Mu’azzam yai masa godiya.
Da k’yar Safeenah ta mik’e tana jan k’afarta, Mu’azzam na biye da ita dan gani yake kaman zata iya fad’uwa k’asa tsaban yanda take taka k’afarta da k’yar. A haka suka isa mota, Safeenah sai raki take tana kuma narke masa.
Suna tafe saman kwalta sukazo Shige DownTown Take away.
Safeenah tace Shawarma take son ci. Parking yai yana tambayarta ko akwai abinda take so bayan Shawarma. Ta girgiza masa kai kad’an alamun a’a.
Wallet d’insa kurum ya d’auka ya fice, ya mance wayarsa nan cikin motar.
Safeenah ta dubi wayar tana tab’e baki kad’an, hannunta Takai saman wayar ta d’an Shafa hasken wayar ya bayyana. Ta murmusa cikeda jin dad’in yanda time ya tafi, har kusan k’arfe 12:30pm. Bata janye idanunta daga barin duban wayar ba taji wayar na vibrating. Ta duba mai kira taga an rubuta _Beautiful_ Dogon tsaki Safeenah taja dan tasan shegiyar can ce mai kira. Katse kiran tai. Nan kiran ya kuma shigowa Safeenah ta kuma katsewa tana murmushi take furta “Wann lokaci na ne yarinya.. Sai lokacin da naga dama ya koma miki.. Yanzu ne zakiyi danasanin shiga tsakanina da My Halal har kiyi gangancin baje Koli a Gidana.” Ta murmusa kafin Ta jefa wayar nasa k’asan seat yanda zai kaman wayar ta fad’a wajen bai sani bane.
Ta hangosa yana rik’e da takeaway d’in. Nan ta kuma shigewa cikin kujera tana lumshe idanunta kaman mai bacci.
Duba d’aya Mu’azzam yai mata ya janye idanunsa, sai kuma ya k’ara dubanta yaga kaman bacci take gashi ta tak’ura cikin seat d’in.. D’an rank’wafowa yai yana k’ok’arin kwantar mata da kujeran dan taji dad’in kishingid’an nata.. Safeenah tana jin ya rank’wafo Sai ta fad’o jikinsa da gangan kaman batasan tayi hakan ba. Ya tsaya cak ya daina abinda yake k’ok’arin yi.. Cikin dabara ya janye Safeenah daga jikinsa kafin ya kwantar mata da kujeran. A hankali ya daidaita nasa zaman cikin kujeransa kafin ya soma driving.
Cikin Zuciyar Safeenah fal annashuwa, ta kula yanda yake driving d’in ma cikeda kulawa ne dan kar wani abu ya samu Babynsu.
A haka har suka iso gida. Ya d’an bubbuga kujeran da take zaune bisa “Feenah wake up now.. We are here.”
Ta bud’e idanunta da k’yar kaman mai baccin gaske.
Ta yunk’ura Zata tashi ta d’an saki k’ara kad’an tana fad’in “My back still hurts..”
Sannu ya dinga mata yana fad’in ta k’ok’arta ta fito. Haka Safeenah ta fito daga cikin motar kaman mai koyon tafiya. Mu’azzam ya rik’o sauran tarkacan, danginsu maganinta da takeaway d’in.
Iya dake jiransu dan sanda zasu fice sun had’u da ita Mu’azzam d’in ya sanar da ita zai kai Safeenah asibiti. Nan take masu sannu da dawowa tana tambayar jikin Safeenah.
Har d’aki Mu’azzam ya rakata, ya d’auko ruwa ya bata maganin yace tasha. Babu musu Ta amsa tasha tana kuma narke masa.
Saida ya tabbata tasha maganin kafin ya mik’e yana zira hannayensa cikin aljihun jeans d’insa. D’an shafa aljihun yai yana duba wayarsa yaji bata nan. Nan yai tunanin k’ila a mota ya barta.
Safeenah na hankalce dashi Ta fahimci wayarsa yake nema. Ta marairaice fuska tana fad’in “Yanzu tafiya zakayi..?”
Ya d’an dubeta sai kuma yace “Is there something you need..?”
Tai rau rau da idanu tace “Yanzu idan naji ciwo cikin dare fah..? You heard what the Dr said ai.” Cikin shagwab’a take maganar.
D’an shafa fuskarsa yai yana fuzar da fuci kad’an “Feenah bazai yuwu kiyi amfani da cikin jikinki ki zaunar dani a nan ba.. Kar wann tunanin ya shiga kanki kin fahimta.” Ya k’arashe yana d’an bud’e idanunsa.
Cikin yanayi mai ban tausai ta jinjina kai tace “Na Sani.. I know my place.. You don’t need to remind me.. Nima dan Ina cikin ciwo ne shiyasa na kiraka kuma dan babu wanda zan kira ne..” Ta k’arashe kaman zata saki kuka.
Ya d’an furzar da huci kad’an yace “Ki kwanta ki huta haka nan.. Ni zan wuce.. Allah ya baki lafiya.. And please ki kula..”
A hankali ta jinjina masa kai tana mai binsa da kallo har ya fice.. Ji tai kaman ta nufesa a guje ta rungume bayansa sabida tsananin kewar kasancewa tare dashi da tai. Ta lumshe idanunta hawaye masu zafi suka gangaro mata.
Shiko Mu’azzam agogon dake manne Parlorn k’asa yake duba har kusan k’arfe 12:am Wato shabiyu na dare.
Duban Iya dake rakub’e gefe yai tana gyangyad’awa alamun fitowarsa take jira. Mu’azzam yai mata sallama cikeda kulawa kafin ya fice.
Mommy tana jin fitarsa ta mik’e ta nufi d’akin Safeenah.
**
A b’angaren Sadiya kaw katse kiranta da yai har sau biyu shine babban abinda yafi d’aga mata hankali gashi har shabiyun dare ta gauta bai dawo ba. Wasu irin k’walla ne taji suna ciko idanunta. Maike shirin faruwa da ita da aurenta..? Tambayar da ya tsaya mata kenan a zuciyarta wanda yasa tuni taji k’walla sun ciko idanunta.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*62*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ta jima sosai zaune a parlorn ko zataji zuwansa amma shiru bai K’araso ba. Jiki a sanyaye ta koma d’aki tai zaune bakin gado had’ida rapka uban tagumi. Wata zuciya tana tuhumarta ‘Kika sani ko ya maida auren Safeenah ne..? Toh amma Maiyasa zaiyi rejecting call d’inta.?’ Tai saurin lumshe idanunta tana San yakice tunanin koma menene cikin zuciyarta. Tashi tai ta d’auro alwala tai sallah raka’a biyu tana addu’an Allah ya sassauta ma zuciyarta. Duk k’alubalen da jarabawa da zata fuskanta a gidan aurenta Allah ya bata juriya da hak’urin cinye wann jarabawar. Tinda aure dama ibada ne. Kuma dik abinda akace ibada ne Toh kuwa dole a fuskanci k’alubale cikinsa. Ta ida addu’o’inta ta mik’e ta haye Gado idanunta kan agogo tana sauraren ko zataji an bud’e gate.
Can taji shigowarsa, maimakon ta mik’e ta nufo parlor sai ta kuma nitsewa cikin gado tana jin wasu hawayen suna zuwa mata. Ita ba jimawan da yai a waje bane damuwarta, abinda bai tab’a yi ba shine katse kiranta.. Kuma har sau biyu ya katse balle tace kuskure ne, gashi bai kuma kiranta back ba.. Wann abin duk yafi sanyar mata da jiki. Tai lamo cikin Gadon tana jiran taji shigowarsa.
Ya turo k’ofan d’ankin nata a hankali, nan ya hangeta kwance saman gado. A nasa tunanin bacci take sai bai shiga d’akin ba Bai tasheta ba ya wuce nasa d’akin.
Peck ya manna mata a gefen kumatu yana mai matsar da bakinsa saitin kunnenta, cikin sigan rad’a ya furta “Wait for me right here kinji koh.” Yai maganar murya a dashe.
Ya mik’e yana duba agogon dake d’aure hannunsa ya nuna 10:30pm. Lokaci guda yake furta “Safeenah needs me now.. Zamuyi magana idan na dawo kinji koh.”
Bata iya amsa sa ba sai nanata abinda yace cikin zuciyarta take. Wai Safeenah ke buk’atarsa.. A cikin daren nan.? toh meke faruwa kenan.? Ji tai jikinta yayi mugun sanyi. A hankali ta kuma nitsewa cikin gadon tana janyo bargo Ta rufa akanta. Har lokacin zuciyarta bai daina tsinkewa ba. Safeenah tana buk’atarsa cikin daren nan? Abinda fah ya fad’a mata kenan.. Sai nanata kalmar take cikin zuciyarta . Ta lumshe idanunta a hankali tana k’ok’arin nitsa zuciyarta. Har lokacin ta Kasa ficewa daga cikin gadon.
**
Yana isowa gidan ya tadda Safeenah ita kad’ai a parlor sai kuka take tana fad’in mararta da bayanta ciwo suke mata. Aiko tana ganin Mu’azzam ta kuma fashewa da wani irin kuka tana ciza labb’anta. Sai yarfe hannu take alamun tana jin jiki.
Ya k’araso cikin sauri ganin ita kad’aice a parlorn. Ya duk’o cikeda kulawa yana dubanta “Tun yaushe ne Bakida lafiya.. Kuma duk gidan nan a rasa mai kaiki asibiti.?”
Cikin yanayi na kuka take fad’in “Musaddiq Bai dawo gida ba.. Ba driver ko d’aya dake kwana a gidan nan yanzu. Meema kuma tun last week ta tafi sch a hostel take zama. (Meema ta samu gurbin karatu a Nile University dake birnin tarayya).
Safeenah taci gaba da kuka tana fad’in “And Mommy yanzu bata iya tuk’i musamman da dare.. Kuma Mommyn da Kiki duk sunyi bacci.. Ni kad’ai aka bari a nan, na tashi zan tafi d’aki naci marata da bayana sun rik’e ko tafiya bazan iya ba.” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya.
Ya d’an girgiza kansa kad’an yace “Tashi muje.. Zaki iya tashi..?”
Ta kuma fashe masa da kuka tana girgiza kai lokaci guda take furta “Bazan iya tashi ba.. Ciwo yake mun..”
D’an sunkuyowa yai yana k’ok’arin kai hannunsa jikinta, sai kuma yaji tana kuma sakin k’ara babu shiri ya tallafota yana fad’in suje.
Safeenah ta Kasa tafiya sai Sabon kukan da ta sakar masa tana kuma d’ingile k’afarta alamun bazata iya tafiya ba.
D’aukanta yai cak ya nufo downstairs da ita. Bai wata wata ba ya sakata a mota yana mata sannu ganin yanda taketa ciza baki tana dafe bayanta da cikinta.
Asibitin da Ta soma ganin Dr tai masa umarni suje.. Suna zuwa kaw Dr d’in yai attending nasu.. Ya duba Safeenah ya bata magunguna.. Mu’azzam ya tambayi ko Babyn na lafiya.. Dr yace yana lafiya amma a dinga kulawa, dama dole zata dinga jin irin wad’ann pains d’in lokaci zuwa lokaci musamman dake cikin k’arami ne ga kuma yanayin da yazo dashi na had’arin ficewa ko wani lokaci.. Abu k’ank’ani zai iya sa cikin ya salwanta.. Saidai a dinga kula.
Mu’azzam yai masa godiya yana jinjina kai ”Za’a kula in sha Allah Dr..”
Sukai masabaha had’ida sallama, Mu’azzam yai masa godiya.
Da k’yar Safeenah ta mik’e tana jan k’afarta, Mu’azzam na biye da ita dan gani yake kaman zata iya fad’uwa k’asa tsaban yanda take taka k’afarta da k’yar. A haka suka isa mota, Safeenah sai raki take tana kuma narke masa.
Suna tafe saman kwalta sukazo Shige DownTown Take away.
Safeenah tace Shawarma take son ci. Parking yai yana tambayarta ko akwai abinda take so bayan Shawarma. Ta girgiza masa kai kad’an alamun a’a.
Wallet d’insa kurum ya d’auka ya fice, ya mance wayarsa nan cikin motar.
Safeenah ta dubi wayar tana tab’e baki kad’an, hannunta Takai saman wayar ta d’an Shafa hasken wayar ya bayyana. Ta murmusa cikeda jin dad’in yanda time ya tafi, har kusan k’arfe 12:30pm. Bata janye idanunta daga barin duban wayar ba taji wayar na vibrating. Ta duba mai kira taga an rubuta _Beautiful_ Dogon tsaki Safeenah taja dan tasan shegiyar can ce mai kira. Katse kiran tai. Nan kiran ya kuma shigowa Safeenah ta kuma katsewa tana murmushi take furta “Wann lokaci na ne yarinya.. Sai lokacin da naga dama ya koma miki.. Yanzu ne zakiyi danasanin shiga tsakanina da My Halal har kiyi gangancin baje Koli a Gidana.” Ta murmusa kafin Ta jefa wayar nasa k’asan seat yanda zai kaman wayar ta fad’a wajen bai sani bane.
Ta hangosa yana rik’e da takeaway d’in. Nan ta kuma shigewa cikin kujera tana lumshe idanunta kaman mai bacci.
Duba d’aya Mu’azzam yai mata ya janye idanunsa, sai kuma ya k’ara dubanta yaga kaman bacci take gashi ta tak’ura cikin seat d’in.. D’an rank’wafowa yai yana k’ok’arin kwantar mata da kujeran dan taji dad’in kishingid’an nata.. Safeenah tana jin ya rank’wafo Sai ta fad’o jikinsa da gangan kaman batasan tayi hakan ba. Ya tsaya cak ya daina abinda yake k’ok’arin yi.. Cikin dabara ya janye Safeenah daga jikinsa kafin ya kwantar mata da kujeran. A hankali ya daidaita nasa zaman cikin kujeransa kafin ya soma driving.
Cikin Zuciyar Safeenah fal annashuwa, ta kula yanda yake driving d’in ma cikeda kulawa ne dan kar wani abu ya samu Babynsu.
A haka har suka iso gida. Ya d’an bubbuga kujeran da take zaune bisa “Feenah wake up now.. We are here.”
Ta bud’e idanunta da k’yar kaman mai baccin gaske.
Ta yunk’ura Zata tashi ta d’an saki k’ara kad’an tana fad’in “My back still hurts..”
Sannu ya dinga mata yana fad’in ta k’ok’arta ta fito. Haka Safeenah ta fito daga cikin motar kaman mai koyon tafiya. Mu’azzam ya rik’o sauran tarkacan, danginsu maganinta da takeaway d’in.
Iya dake jiransu dan sanda zasu fice sun had’u da ita Mu’azzam d’in ya sanar da ita zai kai Safeenah asibiti. Nan take masu sannu da dawowa tana tambayar jikin Safeenah.
Har d’aki Mu’azzam ya rakata, ya d’auko ruwa ya bata maganin yace tasha. Babu musu Ta amsa tasha tana kuma narke masa.
Saida ya tabbata tasha maganin kafin ya mik’e yana zira hannayensa cikin aljihun jeans d’insa. D’an shafa aljihun yai yana duba wayarsa yaji bata nan. Nan yai tunanin k’ila a mota ya barta.
Safeenah na hankalce dashi Ta fahimci wayarsa yake nema. Ta marairaice fuska tana fad’in “Yanzu tafiya zakayi..?”
Ya d’an dubeta sai kuma yace “Is there something you need..?”
Tai rau rau da idanu tace “Yanzu idan naji ciwo cikin dare fah..? You heard what the Dr said ai.” Cikin shagwab’a take maganar.
D’an shafa fuskarsa yai yana fuzar da fuci kad’an “Feenah bazai yuwu kiyi amfani da cikin jikinki ki zaunar dani a nan ba.. Kar wann tunanin ya shiga kanki kin fahimta.” Ya k’arashe yana d’an bud’e idanunsa.
Cikin yanayi mai ban tausai ta jinjina kai tace “Na Sani.. I know my place.. You don’t need to remind me.. Nima dan Ina cikin ciwo ne shiyasa na kiraka kuma dan babu wanda zan kira ne..” Ta k’arashe kaman zata saki kuka.
Ya d’an furzar da huci kad’an yace “Ki kwanta ki huta haka nan.. Ni zan wuce.. Allah ya baki lafiya.. And please ki kula..”
A hankali ta jinjina masa kai tana mai binsa da kallo har ya fice.. Ji tai kaman ta nufesa a guje ta rungume bayansa sabida tsananin kewar kasancewa tare dashi da tai. Ta lumshe idanunta hawaye masu zafi suka gangaro mata.
Shiko Mu’azzam agogon dake manne Parlorn k’asa yake duba har kusan k’arfe 12:am Wato shabiyu na dare.
Duban Iya dake rakub’e gefe yai tana gyangyad’awa alamun fitowarsa take jira. Mu’azzam yai mata sallama cikeda kulawa kafin ya fice.
Mommy tana jin fitarsa ta mik’e ta nufi d’akin Safeenah.
**
A b’angaren Sadiya kaw katse kiranta da yai har sau biyu shine babban abinda yafi d’aga mata hankali gashi har shabiyun dare ta gauta bai dawo ba. Wasu irin k’walla ne taji suna ciko idanunta. Maike shirin faruwa da ita da aurenta..? Tambayar da ya tsaya mata kenan a zuciyarta wanda yasa tuni taji k’walla sun ciko idanunta.
SameenaAleeyou📚
*GIDAN ARO*
*62*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Ta jima sosai zaune a parlorn ko zataji zuwansa amma shiru bai K’araso ba. Jiki a sanyaye ta koma d’aki tai zaune bakin gado had’ida rapka uban tagumi. Wata zuciya tana tuhumarta ‘Kika sani ko ya maida auren Safeenah ne..? Toh amma Maiyasa zaiyi rejecting call d’inta.?’ Tai saurin lumshe idanunta tana San yakice tunanin koma menene cikin zuciyarta. Tashi tai ta d’auro alwala tai sallah raka’a biyu tana addu’an Allah ya sassauta ma zuciyarta. Duk k’alubalen da jarabawa da zata fuskanta a gidan aurenta Allah ya bata juriya da hak’urin cinye wann jarabawar. Tinda aure dama ibada ne. Kuma dik abinda akace ibada ne Toh kuwa dole a fuskanci k’alubale cikinsa. Ta ida addu’o’inta ta mik’e ta haye Gado idanunta kan agogo tana sauraren ko zataji an bud’e gate.
Can taji shigowarsa, maimakon ta mik’e ta nufo parlor sai ta kuma nitsewa cikin gado tana jin wasu hawayen suna zuwa mata. Ita ba jimawan da yai a waje bane damuwarta, abinda bai tab’a yi ba shine katse kiranta.. Kuma har sau biyu ya katse balle tace kuskure ne, gashi bai kuma kiranta back ba.. Wann abin duk yafi sanyar mata da jiki. Tai lamo cikin Gadon tana jiran taji shigowarsa.
Ya turo k’ofan d’ankin nata a hankali, nan ya hangeta kwance saman gado. A nasa tunanin bacci take sai bai shiga d’akin ba Bai tasheta ba ya wuce nasa d’akin.