Sashe 100
Gidan Aro Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanci tashi babu wuya wajen Allah saida su Mu’azzam suka kwashe sati garin yana tarairayar matarsa had’ida bata wani irin kula na musamman, wata rayuwa ce da suke addu’an inama su tabbata cikinta babu yankewa.
Dukda tsananin son sake kusantarta da yake bai bari yayi hakan ba, dan gani yake sam kaman bata warke ba. Saidai kusan koda yaushe suna nan mak’ale da juna tana zuba masa shagwab’a san ranta yana tarairayarta. Sannan su Umma kusan kullum sai sunyi waya taji lafiyarsu. Wayar Aunty Larai take kira dan bata faye samun na Umman ba. Tasan yanzu haka Umman ce bata son suke wayar tinda tarewarta kenan. Ta murmusa a hankali tana jinjina lamarin Ummanta.
Yau tinda ta shiga sahen Inne bata fito ba, nan ta tadda Ajidde wajen Mamy, ta taimaka ma Ajidde suka bawa Mamy magani tare.
Mama Hindu ta shigo tana tambayar idan sun gama bata maganin zata shiryata.
Sadiya ta dubi Mama Hindu tace “Mama Hindu zan so na taimaka miki da shirya Mamy koda da gyaran sumarta ne.” Tai maganar cikin tsananin son ta taimaka.
Mama Hindu ‘yaruwarsu ce sann tun auren farko da tayi mijin ya rasu nata sake aure ba take zaune nan gidan Inne hakan yasa take kulada Aunty Nuratun.
Murmusawa Mama Hindu tai tace “Allah Sarki sai kika tuna min da marigayiya Ikram.. So tari kikan tuna mun ita.. Kunada wani yanayi mai shigen kama.. Itama haka nan idan naje can Abuja gidansu Ina kula da mahaifiyar tata musamman lokutan da take makaranta bata samun lokacin kula da mahaifiyar sai ta ce mun Mama Hindu ki barni na sami albarkan Mamy koda da gyaran sumarta ne.. Sosai kika tuna mun Ikram a yau..” Ta k’arashe k’walla na ciko idanunta.
Murmusawa kad’an Sadiya tai k’walla na ciko idanunta itama, a hankali Ta furta “Allah sarki.. Allah yasa tana Aljannah.. Ubangiji yasa ladar jinyar mahaifiyarta da tayi ya risketa har cikin makwancinta..”
Mama Hindu ta amsa da Ameen tana duban Mamyn. Lokaci guda take ci gaba da furta “Bata sani ba.. Bata San cewa d’iyarta ta rasu ba.. Zata farka ne ta tadda babu Ikram idan Allah ya nufa jinyar bana tafiya bane..” Ta k’arashe tana goge hawayenta.
Sadiya daketa duban Mamyn itama goge nata hawayen tai kafin Ta jinjina kai tace “In sha Allah Mamy zata sami lafiya.. Kuma Allah zai d’agata... Allah zai sanya mata hak’uri da dangana cikin zuciyarta.. Zataima Ikram addu’a wanda zai bita har makwancinta.” Ta k’arashe tana mai dafa hannun Mamyn.
Mama Hindu ta murmusa kad’an kafin tace “Allahu yashaa Sadiya.. A lokacin da Aunty Nuratu zata farka zata tadda babu d’iyarta Ikram amma zata tadda sabuwar d’iya Allah ya bata bayan ya amshe Ikram daga gareta.. Shi d’in shine mafi kyawun kyauta da kuma jin k’ai..”
Sadiya ta murmusa tana dubanta daidai sanda Ajidde ta k’araso da ruwa da towel Sadiya na warware dogon gashin Aunty Nuratu da yake bak’ik’irin mai sulb’i da shek’i.. Wani ikon Allah duk tsawon lokacin nan da tai tana jinya sam sumarta bai cinye ba, yana nan da tsawonsa saidai abinda baza’a rasa ba.
A tare suke gyara mata sumar itada Ajidde gwanin ban sha’awa Sadiya na nuna ma Ajidde abinda zata taimaka mata dashi, Yai tsaye daga bakin k’ofa yana dubansu yanda suke gyara mahaifiyarsa. Sai yaji wani abu can k’asar zuciyarsa na tsargar masa.. For the first time da yaji tsanar da yake ma Ajidde cikin zuciyarsa ya ragu.. Bai shiga ba haka nan bai tankasu ba sai gudanar da al’amaransu suke kaman wani Sun jima da sanin juna.
Ya tuna kalaman Musaddiq cewa Wai yana son yarinyar kuma zai aureta.. A hankali ya janye idanunsa yana jin wayarsa dake aljihu tana vibrating.
Abokinsa Assad ne mai kira. Saidai kafin ya d’aga kiran yaji Ta katse..
Yai tunanin ko network hakan yasa ya kuma danna kiran layin Assad d’in.
Har saida wayar ta kusan tsinkewa kaman bazai d’aga ba sai kuma ya d’aga cikin yanayi na rashin kuzari.
Daga yanayin da Mu’azzam ya jisa ciki ya fahimci akwai matsala, snn a ‘yan kwanakin ya kula Assad yana avoiding wayarsa, dan tinda yazo garin zai iya k’irga sau nawa sukai waya ba kaman da ba da ko yaushe suna nan suna waya da juna yana bawa Mu’azzam d’in updates.. Toh amma wnn karon gaba d’aya abokin nasa ya canza amma sai ya alak’anta hakan da cewar Assad d’in space yake basa yaci angwancinsa da kyau..Yasan tsiyar Assad yanzu haka wnn dalilin na iya Sa ya d’an janye masa k’afa har ya gama kwanakinsa a garin.
“Ina jinka Wai meke damunka ne..?” Mu’azzam d’in ya tambaya yana ficewa waje.
Assad ya d’an tamke idanunsa yana k’ok’arin daidaita bugun zuciyarsa. Lokaci guda ya d’an kuma fuzar da fuci kad’an kafin yace “It’s nothing.. Kayi enjoying hutunka kuma ka kula da Amarya.. Zan kashe wayar banjin dad’i ne..”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “Wait Assad don’t hang up.. Wai meye ne ke faruwa.. Meke damunka ne..?”
“I told you Babu komai... Stress ne kawai, zamuyi magana later ka gaida Amarya..” Yana ida fad’in haka ya datse wayar yana shafe goshinsa had’ida tattaro naman goshin.
Wallet d’insa ya bud’e hoton d’iyarsa mai shekaru biyu a duniya ya bayyana. Take yaji wasu irin k‘walla na ciko idanunsa. Ya lumshe idanu ya sumbaci hoton, lokaci guda yake furta “Zaki girma cikin mutunci da muntatawa.. Bazan tab’a shafawa rayuwarki bak’in fenti ba bayan wanda mahaifiyarki ta Shafa miki.. Nayi alk’awarin b’oye miki dalilin rabuwata da mahaifiyarki cewa na kamata ne da wani.. Maiyasa zan bari wad’ann hotunan su watsu a duniya wanda za’a ajiye miki har girmanki.. Tarihi Ta kuma nuna miki cewa ga abinda mahaifinki ya aikata.. Tabbas ka girma ka tadda iyayenka mutanen kirki ne Dattawan K’warai ba k’aramin rahama bane da Allah zaiwa Bawa. Ban taso na tadda d’aya daga cikin iyayena mutumin banza ba bazanso ke ki taso ana nunaki ana fad’in ga abinda mahaifinki ya aikata ba. Idan har zan rufe miki abinda mahaifiyarki ta aikata Tabbas zan rufe miki wann.. Sweetheart inada zab’i ne guda biyu.. Kodai ki girma ki tadda mahaifinki na kurkuku kan laifin da bai aikata ba.. Ko kuma ki girma ki riski bak’in labari da zai shafi martabarki da sunan ki kan kuskuren da mahaifinki sam shima bai aikata ba..” Muryarsa yaci gaba da rawa yana jinjina kai yake duban hoton d’iyar tasa “Tsakani biyu dole na zab’i d’aya.. Dole na zab’i d’aya..!” Ya k’arashe yana kuma lumshe idanu a hankali.
**
A b’angaren Mu’azzam kaw koda yai ta kiran Assad d’in bai d’aga ba yasan dole akwai abinda ke faruwa. Sann yanayin da ya masa magana ciki ya kuma tabbatar masa akwai abinda ke damun Assad d’in.
Fuzar da fuci yai kad’an yana tunanin kiran layin Yusuf ya tambayesa abinda ke faruwa. Bai ida tinanin ba wayar Assad ya kuma shigo masa. Cikin sauri ya d’aga cikeda zak’uwa yana son jin meke wakana da Assad d’in.
Daga d’aya b’angaren Assad yace “Mu’azzam.. There’s something I need to tell you..”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “Ehen go ahead ina sauraronka..”
Assad ya kuma shafe fuskarsa yana mai fuzar da fuci a hankali “You see.. Bana so na b’ata maka wann lokaci mai mahimmanci na rayuwarka.. But I guess banida zab’i Mu’azzam..!” Ya kuma fuzar da fuci a hankali.
Mu’azzam da yai shiru yana sauraronsa ya girgiza kai yace “Tell me Brother.. Meke faruwa, kar ka damu you can just tell me..”
Ya d’an rintse idanunsa kad’an kafin ya bud’e yace “It’s... You see maganar bata waya bace.. I think zaifi kyau idan muka had’u.. But kar ka katse tafiyarka.. Idan ka dawo sai mu tattauna..”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “No.. You sound serious Assad.. Zan dawo sai muyi maganar.”
Assad yai k’ok’arin dakatar dashi amma Mu’azzam d’in bai saurari hakan ba, Assad d’in yasan bazai saurari hakan tinda yace zai dawo zai dawo d’in..
Zama Assad yai yana mai fad’awa cikin kujera k’irjinsa na masa nauyi. Ya dafe kansa yana fad’in “What have you done Assad..?” Lumshe idanunsa ya kuma yi kansa na masa wani irin nauyi.
A hankali ya jinjina kai yana furta “Our job however, required us to put our minds over our fears. I must do this.. I have to do this..!”
**
Misalin k’arfe 9:00pm suna zaune parlor, kanta saman cinyarsa tayi matashi da cinyar nasa hannunsa saman sumarta yana shafawa a hankali yayinda Sadiyar ke ci gaba da labarta masa barkwancin Ajidde da yanda take jin dad’in labarunta. Nan dai taga kaman hankalinsa baya wajen.
Ta d’an mirgino tana dubansa “Are you alright..?” Ta tambaya tana dubansa.
Ya saki miskilin murmushi a hankali yana mai jan hancinta kad’an da yatsun hannunsa “Why wouldn’t I bayan kina taredani.. Ga kuma Mamy na a nan ga Inne.. Mataye guda uku da sukeda matuk’ar mahimmanci a rayuwata..”
Ta murmusa kad’an jikinta na kuma yin sanyi jin bai ambato Safeenah ba, ko maganarta bai tab’a yi ba tinda sukazo garin.
Ta d’an gyara kwanciyarta sosai tana kuma dubansa “Safeenah fah..? Dan Allah bazakayi hak’uri haka nan ka maidata ba.. Kaga fah babu abinda ya faru babu wanda ta harba.. Dan Allah ka mata afuwa haka nan..”
K’uri yai mata yana dubanta, sai kuma ya d’auke kansa kad’an “Kar ki sake mun zancen Safeenah..!” Abinda ya fad’i kawai kenan cikin tsananin tsimewa wanda har saida ya koma mata tamkar Mu’azzam d’in da ta soma sani.
Jikinta ya d’anyi sanyi, ta maida kanta Ta kwantar, sai kuma ta dubesa kad’an ganin yanda ransa ya b’aci sosai. A hankali ta furta “Kai hak’uri bazan sake ba.”
Bai ce mata komai ba Sai k’urama waje guda idanu da yai, al’amarin Musaddiq da Assad na kuma Yawo a kwanyarsa. Tun bayan data masa maganar Safeenah ta lura walwalarsa ya d’auke.. A nata zaton kan maganar Safeenah da tai ne ya maidasa haka saidai batasan cewa abubuwa ne da dama k’unshe cikin zuciyar mijin nata ba. Har wajajen k’arfe 11pm bai shigo ya kwanta ba, tana nan kwance k’walla tab idanunta tana tinanin kodai fushi ne yayi da ita..? Maiyasa bai shigo ba..? Can taji shigowarsa yana waya wanda takeda tabbacin da mutanesa na wajen aiki ne.
Dukda tsananin son sake kusantarta da yake bai bari yayi hakan ba, dan gani yake sam kaman bata warke ba. Saidai kusan koda yaushe suna nan mak’ale da juna tana zuba masa shagwab’a san ranta yana tarairayarta. Sannan su Umma kusan kullum sai sunyi waya taji lafiyarsu. Wayar Aunty Larai take kira dan bata faye samun na Umman ba. Tasan yanzu haka Umman ce bata son suke wayar tinda tarewarta kenan. Ta murmusa a hankali tana jinjina lamarin Ummanta.
Yau tinda ta shiga sahen Inne bata fito ba, nan ta tadda Ajidde wajen Mamy, ta taimaka ma Ajidde suka bawa Mamy magani tare.
Mama Hindu ta shigo tana tambayar idan sun gama bata maganin zata shiryata.
Sadiya ta dubi Mama Hindu tace “Mama Hindu zan so na taimaka miki da shirya Mamy koda da gyaran sumarta ne.” Tai maganar cikin tsananin son ta taimaka.
Mama Hindu ‘yaruwarsu ce sann tun auren farko da tayi mijin ya rasu nata sake aure ba take zaune nan gidan Inne hakan yasa take kulada Aunty Nuratun.
Murmusawa Mama Hindu tai tace “Allah Sarki sai kika tuna min da marigayiya Ikram.. So tari kikan tuna mun ita.. Kunada wani yanayi mai shigen kama.. Itama haka nan idan naje can Abuja gidansu Ina kula da mahaifiyar tata musamman lokutan da take makaranta bata samun lokacin kula da mahaifiyar sai ta ce mun Mama Hindu ki barni na sami albarkan Mamy koda da gyaran sumarta ne.. Sosai kika tuna mun Ikram a yau..” Ta k’arashe k’walla na ciko idanunta.
Murmusawa kad’an Sadiya tai k’walla na ciko idanunta itama, a hankali Ta furta “Allah sarki.. Allah yasa tana Aljannah.. Ubangiji yasa ladar jinyar mahaifiyarta da tayi ya risketa har cikin makwancinta..”
Mama Hindu ta amsa da Ameen tana duban Mamyn. Lokaci guda take ci gaba da furta “Bata sani ba.. Bata San cewa d’iyarta ta rasu ba.. Zata farka ne ta tadda babu Ikram idan Allah ya nufa jinyar bana tafiya bane..” Ta k’arashe tana goge hawayenta.
Sadiya daketa duban Mamyn itama goge nata hawayen tai kafin Ta jinjina kai tace “In sha Allah Mamy zata sami lafiya.. Kuma Allah zai d’agata... Allah zai sanya mata hak’uri da dangana cikin zuciyarta.. Zataima Ikram addu’a wanda zai bita har makwancinta.” Ta k’arashe tana mai dafa hannun Mamyn.
Mama Hindu ta murmusa kad’an kafin tace “Allahu yashaa Sadiya.. A lokacin da Aunty Nuratu zata farka zata tadda babu d’iyarta Ikram amma zata tadda sabuwar d’iya Allah ya bata bayan ya amshe Ikram daga gareta.. Shi d’in shine mafi kyawun kyauta da kuma jin k’ai..”
Sadiya ta murmusa tana dubanta daidai sanda Ajidde ta k’araso da ruwa da towel Sadiya na warware dogon gashin Aunty Nuratu da yake bak’ik’irin mai sulb’i da shek’i.. Wani ikon Allah duk tsawon lokacin nan da tai tana jinya sam sumarta bai cinye ba, yana nan da tsawonsa saidai abinda baza’a rasa ba.
A tare suke gyara mata sumar itada Ajidde gwanin ban sha’awa Sadiya na nuna ma Ajidde abinda zata taimaka mata dashi, Yai tsaye daga bakin k’ofa yana dubansu yanda suke gyara mahaifiyarsa. Sai yaji wani abu can k’asar zuciyarsa na tsargar masa.. For the first time da yaji tsanar da yake ma Ajidde cikin zuciyarsa ya ragu.. Bai shiga ba haka nan bai tankasu ba sai gudanar da al’amaransu suke kaman wani Sun jima da sanin juna.
Ya tuna kalaman Musaddiq cewa Wai yana son yarinyar kuma zai aureta.. A hankali ya janye idanunsa yana jin wayarsa dake aljihu tana vibrating.
Abokinsa Assad ne mai kira. Saidai kafin ya d’aga kiran yaji Ta katse..
Yai tunanin ko network hakan yasa ya kuma danna kiran layin Assad d’in.
Har saida wayar ta kusan tsinkewa kaman bazai d’aga ba sai kuma ya d’aga cikin yanayi na rashin kuzari.
Daga yanayin da Mu’azzam ya jisa ciki ya fahimci akwai matsala, snn a ‘yan kwanakin ya kula Assad yana avoiding wayarsa, dan tinda yazo garin zai iya k’irga sau nawa sukai waya ba kaman da ba da ko yaushe suna nan suna waya da juna yana bawa Mu’azzam d’in updates.. Toh amma wnn karon gaba d’aya abokin nasa ya canza amma sai ya alak’anta hakan da cewar Assad d’in space yake basa yaci angwancinsa da kyau..Yasan tsiyar Assad yanzu haka wnn dalilin na iya Sa ya d’an janye masa k’afa har ya gama kwanakinsa a garin.
“Ina jinka Wai meke damunka ne..?” Mu’azzam d’in ya tambaya yana ficewa waje.
Assad ya d’an tamke idanunsa yana k’ok’arin daidaita bugun zuciyarsa. Lokaci guda ya d’an kuma fuzar da fuci kad’an kafin yace “It’s nothing.. Kayi enjoying hutunka kuma ka kula da Amarya.. Zan kashe wayar banjin dad’i ne..”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “Wait Assad don’t hang up.. Wai meye ne ke faruwa.. Meke damunka ne..?”
“I told you Babu komai... Stress ne kawai, zamuyi magana later ka gaida Amarya..” Yana ida fad’in haka ya datse wayar yana shafe goshinsa had’ida tattaro naman goshin.
Wallet d’insa ya bud’e hoton d’iyarsa mai shekaru biyu a duniya ya bayyana. Take yaji wasu irin k‘walla na ciko idanunsa. Ya lumshe idanu ya sumbaci hoton, lokaci guda yake furta “Zaki girma cikin mutunci da muntatawa.. Bazan tab’a shafawa rayuwarki bak’in fenti ba bayan wanda mahaifiyarki ta Shafa miki.. Nayi alk’awarin b’oye miki dalilin rabuwata da mahaifiyarki cewa na kamata ne da wani.. Maiyasa zan bari wad’ann hotunan su watsu a duniya wanda za’a ajiye miki har girmanki.. Tarihi Ta kuma nuna miki cewa ga abinda mahaifinki ya aikata.. Tabbas ka girma ka tadda iyayenka mutanen kirki ne Dattawan K’warai ba k’aramin rahama bane da Allah zaiwa Bawa. Ban taso na tadda d’aya daga cikin iyayena mutumin banza ba bazanso ke ki taso ana nunaki ana fad’in ga abinda mahaifinki ya aikata ba. Idan har zan rufe miki abinda mahaifiyarki ta aikata Tabbas zan rufe miki wann.. Sweetheart inada zab’i ne guda biyu.. Kodai ki girma ki tadda mahaifinki na kurkuku kan laifin da bai aikata ba.. Ko kuma ki girma ki riski bak’in labari da zai shafi martabarki da sunan ki kan kuskuren da mahaifinki sam shima bai aikata ba..” Muryarsa yaci gaba da rawa yana jinjina kai yake duban hoton d’iyar tasa “Tsakani biyu dole na zab’i d’aya.. Dole na zab’i d’aya..!” Ya k’arashe yana kuma lumshe idanu a hankali.
**
A b’angaren Mu’azzam kaw koda yai ta kiran Assad d’in bai d’aga ba yasan dole akwai abinda ke faruwa. Sann yanayin da ya masa magana ciki ya kuma tabbatar masa akwai abinda ke damun Assad d’in.
Fuzar da fuci yai kad’an yana tunanin kiran layin Yusuf ya tambayesa abinda ke faruwa. Bai ida tinanin ba wayar Assad ya kuma shigo masa. Cikin sauri ya d’aga cikeda zak’uwa yana son jin meke wakana da Assad d’in.
Daga d’aya b’angaren Assad yace “Mu’azzam.. There’s something I need to tell you..”
Mu’azzam ya jinjina kai yace “Ehen go ahead ina sauraronka..”
Assad ya kuma shafe fuskarsa yana mai fuzar da fuci a hankali “You see.. Bana so na b’ata maka wann lokaci mai mahimmanci na rayuwarka.. But I guess banida zab’i Mu’azzam..!” Ya kuma fuzar da fuci a hankali.
Mu’azzam da yai shiru yana sauraronsa ya girgiza kai yace “Tell me Brother.. Meke faruwa, kar ka damu you can just tell me..”
Ya d’an rintse idanunsa kad’an kafin ya bud’e yace “It’s... You see maganar bata waya bace.. I think zaifi kyau idan muka had’u.. But kar ka katse tafiyarka.. Idan ka dawo sai mu tattauna..”
Girgiza kai Mu’azzam yai yace “No.. You sound serious Assad.. Zan dawo sai muyi maganar.”
Assad yai k’ok’arin dakatar dashi amma Mu’azzam d’in bai saurari hakan ba, Assad d’in yasan bazai saurari hakan tinda yace zai dawo zai dawo d’in..
Zama Assad yai yana mai fad’awa cikin kujera k’irjinsa na masa nauyi. Ya dafe kansa yana fad’in “What have you done Assad..?” Lumshe idanunsa ya kuma yi kansa na masa wani irin nauyi.
A hankali ya jinjina kai yana furta “Our job however, required us to put our minds over our fears. I must do this.. I have to do this..!”
**
Misalin k’arfe 9:00pm suna zaune parlor, kanta saman cinyarsa tayi matashi da cinyar nasa hannunsa saman sumarta yana shafawa a hankali yayinda Sadiyar ke ci gaba da labarta masa barkwancin Ajidde da yanda take jin dad’in labarunta. Nan dai taga kaman hankalinsa baya wajen.
Ta d’an mirgino tana dubansa “Are you alright..?” Ta tambaya tana dubansa.
Ya saki miskilin murmushi a hankali yana mai jan hancinta kad’an da yatsun hannunsa “Why wouldn’t I bayan kina taredani.. Ga kuma Mamy na a nan ga Inne.. Mataye guda uku da sukeda matuk’ar mahimmanci a rayuwata..”
Ta murmusa kad’an jikinta na kuma yin sanyi jin bai ambato Safeenah ba, ko maganarta bai tab’a yi ba tinda sukazo garin.
Ta d’an gyara kwanciyarta sosai tana kuma dubansa “Safeenah fah..? Dan Allah bazakayi hak’uri haka nan ka maidata ba.. Kaga fah babu abinda ya faru babu wanda ta harba.. Dan Allah ka mata afuwa haka nan..”
K’uri yai mata yana dubanta, sai kuma ya d’auke kansa kad’an “Kar ki sake mun zancen Safeenah..!” Abinda ya fad’i kawai kenan cikin tsananin tsimewa wanda har saida ya koma mata tamkar Mu’azzam d’in da ta soma sani.
Jikinta ya d’anyi sanyi, ta maida kanta Ta kwantar, sai kuma ta dubesa kad’an ganin yanda ransa ya b’aci sosai. A hankali ta furta “Kai hak’uri bazan sake ba.”
Bai ce mata komai ba Sai k’urama waje guda idanu da yai, al’amarin Musaddiq da Assad na kuma Yawo a kwanyarsa. Tun bayan data masa maganar Safeenah ta lura walwalarsa ya d’auke.. A nata zaton kan maganar Safeenah da tai ne ya maidasa haka saidai batasan cewa abubuwa ne da dama k’unshe cikin zuciyar mijin nata ba. Har wajajen k’arfe 11pm bai shigo ya kwanta ba, tana nan kwance k’walla tab idanunta tana tinanin kodai fushi ne yayi da ita..? Maiyasa bai shigo ba..? Can taji shigowarsa yana waya wanda takeda tabbacin da mutanesa na wajen aiki ne.