← Book details Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 171

Sashe 72

Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kwance take rub da ciki saman gadon ta,dake dan karan dakin nata na cikin gida Anty ta,
Tana saye da wani dogon riga baki mai yar hannun shimi, har kasa rigar tie ce ta mastse ta ta tsakiya inda tadan cire top din rigar ta aje saman kujerar ta,
Dakin yasha gyara dan har wani kyali ties din kasan dakin keyi gawani kamshi dake ta shi ,
Takardun ta ke nazari tana kuma dan rubuto a gefe guda, daga kwancen,
Wayar ta, touching kiran ardriod tana gefe guda saman gadon sai waka ke tashi,
Wankan Fadar bege, inda yake wakarshi mai take, Sarki Jiran Halittu, mijin juwairah,
Tanayi tana dan maming din wakar daga kwance,
Issalam ce ta shigo dakin da gudun ta tana rataye da jakar makarantar ta a baya,
Sai kokarin cire takalman ta takeyi kuma tana kallon kofar shigowa gida tana dariya,
Maryam sam bata kai hankalin ta ga abinda yarinyar ke yi ba,
Sallama yakara yi cikin kwantar da harshe kamar a mafarki taji muryan, nashi,
Don dai baji Anty ta na zancen zowan shi ba kamar yadda ta saba yi,indan zai zo,
Dammm gaba ta yabayae wanda batasan dalilin faduwar gaban ba ,
A hankali ta sauko daga saman gadon cikin sanda, tana mai karba sallaman,
Sam ta manta cewa yar rigace a jikin ta saida taga ya kauda kai yana mai komawa baya,
Tai saurin komawa cikin dakin tadauko hijab din ta tayafa,
Zaune yake a saman kujera yana mai dafe da kan shi da hannu guda alamar gajiya, atare dashi ga kuma su Assalam nata faman mashi surutu,
Sannu da zuwa ta iya furtawa ta wuce wurin da fridge yake dan dauko mai ruwa,
Tai mamaki kwarai dataga cewa ya,shaye duk gora guda na ruwan da ta aje mai don ko cup bai dauka ba,
A kunyace maryam ta gaishe shi,
Inda ya karba mata ba wani sakin fuska kamar kullun,
Ta juya zata wuce don kiran anty a wayan ta, don ta,tafi gurin barka a makwabta,
Kamar daga sama taji yakira sunan ta, a wani murya na kasalance,
A tsorace maryam ta juyo, sai yanzu ta kula da kalar kayan jikin shi,
Wani yadine na maza fari mai taushi kamar lece,
Sai kyalin fari yadin keyi har yana kashe ido,
Saidai duk da tadan ta takure dan zaman motar da yadan yi,
Kanta ta maryam kasa don jin abinda zaice mata, saboda bazata iya jure kallon shi,,,
Muryan shi taji yana cewa ya jikin mama hope taji sauki sosai,
Tana wasa da yatsun hannunta ta hada su wani cikin wani
Tace taji sauki sosai yanzu Alhamdullah, ba,a magane cewa tayi ciwo ai,
Masha Allah yace,
Tana kokarin barin gurin kuma sai taji yana cewa, ga keys pls a shigo ma anty da kaya ciki,
Kayan tsarabane sosai kamar yadda yasaba kawowa yazo da su, Manja, Irish, sai Doya gudan mai yawa,
Almajirai tasa suka kwaso zuwa cikin gidan su inda Anty Dije ta samay su akofa gida tsaye tana sallamar yaran,
Tare suka shigo inda Anty take mai, korafin rashi sanar da ita, zuwan shi,
Kayan da tagani yasa tai tsai da maganar ta, takasa karasawa,
Wai kai Yusuf baka gajiya da dawainiya haka kulun,
Kai ya langabar kamar yaro karami yace ana gajiya da yiwa dan uwa dawainiya ne Anty, ?
Taji dadin maganar shi har cikin ranta sosai, don yadda yake nuna cewa shi nadu kamar yadda minin Anty yai mai nasiha bayan musuluntar shi,
Dacewa yadauke su tankar jini guda don yin haja zai sa yarage wa zuciyar shi radadi,
Sanan kuma mutum bai zama baida yan uwa aduniya
Don haka yazama yana sake jikin shi dasu har zuwa lokacin da yan uwanshi zasu huce dashi,
Abinci suke kokarin gabatar mashi amma sai ya, dakatar da su dace bazai iyaci ba don yana jin ciwon kai a halin yanzu
Daga Anty har maryam a lokaci guda suka waigo shi
Maryam wace sai, yanzu ta lura da cewa tun da yashigo yake dafe gishin shi wanda ita tadauka ba komai bane,
May ke da,muwar ka Yusuf, ?
Lafiya kalau nafito amma sai naji kawai na kusa shigowa Minna kai,na yai,wani sarawa,
Sannu suka dinga mai gaba dayan su har yaran yana amsawa a hankali,
Masaukin shi ya nufa don yaje ya dan watsa ruwa ya huta,.
Amma sai yaji kan nashi kamar yana karuwa ne,
Ibrahim yakira don tare suka zo dashi cikin sauri ya,samay shi,
Saidai yadda ya samay shi din ya bashi tsoro sosai don wani irin yake ji, a kan nashi,
Ga wasu jijiyoyin sun fito mai rada, rada a lokaci guda saman goshin shi,
Ibrahim yakira mahaifin shi, ya sanar dashi abinda ke faruwa,
Ba bata lokaci Abdulsamad ya iso masaukin na Yusuf inda kallo guda yai mai yafahinci ko may ye,
Sosai rashin lafiya Yusuf yake cigaba, a dan kan kanin lokaci,
Asibiti suka tafi cikin daren nan, don yadda yaje ji tankar kan shi zai tsage a lokaci guda,
Bayan yan "yan tambayoyi da likita yai mashi sai kuma su ka bashi magani da,sauran yan shawarwari,
Kamar kar su dawo masaukin shi abin sai kuma yafi da karfi,
Sai wani kugi yakeyi, yana tallabar kan shi ko kuma ha dinga bugawa kamar zai fasa,
Wayar shi ce tai kara don haka Ibrahim ya dauka dan ganin mai kiran don yasan cewa ba zai iya daga wayan ba, shi Yusuf din,
Anty Dije yaga anrubuta,,,
Muryan wani taji yadauka alokacin da take kokarin yi mashi sallama,
Ji tayi yana cew sorry mai yawan baya da lafiya saboda sanin dayayi kowaye anty dije ga Yusuf,
Cikin rudewa take ce wa subbahanallah, tambayar shi ta yi cewa yana ina, yanzu,?
Nan dai Ibrahim ya sheda mata gidan da Yusuf ke sauka a wani Lolo, Ested, dake GRA,
A motar kanin Illiya costume suka zo gaba, dayan su,
Maryam wace ke dauke da Abubakar a kafadar ta ta, da kuma wani basket,
Cikin rudewa anty dije ke fadar umm,uhmm subbahanallah,
Wanan wani irin ciwo ne haka, acikin dan lokaci guda,
Gaskiya wanan ciwon yakamata a san abin yi akai bawai abarshi a haka ba
Don dare ake ma gudu, kada abin yafi nan worse, ko ya kukagani,
Ibrahim yace ai yaga mahaifinshi yace yana zuwa yafita,
Bai fi minti biyu ba da fadar haka sai ga malm, Abdulsamad da mahaifin Jibrin sun shigo,
Tundafa nesa mahaifin Jibrin ke cewa subbahanallah a,a,a
Wani malami suka shigo dashi dan matashi ba wai wani babbba ba,
Tun bai taba Yusuf ba yace akwai matsala fa aciki,
Rukiya yai mashi sai,gashi yai wani irin atishawa mai karfi,
A, hankali yafara mai,da numfashin shi, guda guda daga haka sai barci yadan dauke shi,
Su Anty sunkai wani lokaci a tsatsaye suna kallon ikon Allah,
Saida dare yadan yi malam Abdulsamad yace ai su tafi gida har zuwa safe, su dawo,
Tunda zuwa yanzu yasamu barci insha Allah komai zai zo da sauki ai,
Duk kan su jiki ba wani kuzari suka iso gida zuciyar su fam da tambayoyi,
A lokaci guda yakoma wani dan feyau, dashi duk ya zube yawani je may ,
Kwance yake yawani dunkule guri guda, kamar jariri, aciki,
Mafarki yayi da wasu na binshi da wasu irin makamai masu cutar wa,
Da gudu suka biyu shi sai da zo gaban wani mutum mai wasu kaya shudi,shudi sai tsaya inda ke binshi a baya baya,
Kamar zai fadi sai ce La ilaha illah ant subbaha nika in,ni kun,tu minal zalimin,
Da karfi ya furta a fili yazabura ya mike zaune, wani iri yaji akan shi lokaci guda,
Zaune ya mike tana mai dafe kan shi sai wani zufa yake yi,kamar yana acikin ovon,
Addu,oi sosai suka dinga mai har zuwa rukiyar da karatun alkur,ani mai tsarki,
Barcin da yasamu wanan karon yadan yi nauyi so sai fiye dana farko,

Washegari tunda safe anty ta hada mai abin kari a cikin basket,
Amma sai maryam tace ai masa kunun kamu da kosai, don wata,kila zaifi son su da ruwan tea din,,
Ita kadai anty tabawa abin karin nashi takai don ita, babu motar da,zai zo da ita,yanzu,
Sai da gari yawaye ya haska sosai yasamu farkawa daga barcin,
Inda yai yar madifar rashim tashe shi da ba,ayi ba da guri har gari ya waye haka,
Zaune yake ya takure wuri daya can kuryan daki
Dai,dai kwanar wani dan standing drower dake a cikin dakin,
Falo ta tsaya ta aje kayan sai kuma ta ja tai saye guri guda,
Tana kallon Ibrahim wanda ke kokarin aje kayan saman dan dining table din da,ke dakin,
Ibrahim ne daga inda yake tsaye yake mata magana cewa, ta shiga aiyana nan zaune,
A nutse ta rika takawa har zuwa cikin dakin,inda yake,
Duk da baida lafiya sanyin A, C ne ya gauraye dakin, sai kamshim turaren shi da yake yawan shafawa akai a kai, watau turaren THE,,,
Babu kowa a dakin sai shi kadai,
Jin sallamar Maryam yasa shi dago kai a hankali, ya kalle ta, yana mai ansa mata sallamar ta,,,
Ban garen da yake zaune a takure idon shi a lumshe,
Yabude su a hankali ya sauke su ida tak ke tsaye a bakin kofa
Maryam ta kalla, shi sai, taji wan irin tausayin shi ya kamata lokaci guda,
A marairaice kamar mai shirin kuka maryam tace ina kwana, Uncle
Kamar yadda taji su Assalam naki ranshi da sunar,
Tace mai ina kwana ya jikin,
Kanshi yadago yakalle ta saida taji gaban ta ya fadi don yadda idon shi sukayi wani irin ja,
A hankali kamar mai jin zafin furta magana ya ansa mata da cewa lafiya Maryam,
Ya anty da yaran suke, wani iri taji lokacin dayake maganar don dagani yana jin jikin shi so sai,saidai daurewa da yakeyi irin ta maza,,,,

ZEEEE. ,MAKAWA
[3/12, 10:47 PM] ‪+234 813 139 5577‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
4⃣7⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

Rubutun novel tankar wani fadakawa ne ga al,uma,
Duk novel dole akwai sakon da yake isar wa zuwaga al,uman,hausawa da musulmai, baki daya,
Don haka mu fahintar da matasan mu alheri a ko yau,she ba mu koya masu yadda rayuwa zata gurbace ba,,
Allah yasa mu dace baki dayan mu Allahuma Ameen 👏👏👏👏👏
Chapter 72 · 0% Book details