Sashe 126
Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru suka yi gaba daya dakin kowa da irin abin da, yake sakawa a,zuciyar shi,
Gama ga maryam wace ke sauke ajiyan zuciya akai akai
Safiya ta kau da shirun da cewa ki tashi ki gyara jikin ki ki sake rayuwan ki tankar bake ce a haka ba,
Sai a lokacin maryam tai dan murmushi jin abin da safiya tace ,
Abincin rana da Anty ta,gama ne ta aiko masu da shi a daki,
Maryam tafito da kan ta ta daukan masu ruwan sha, a cikin fridge,
Sun fara cin abinci ba da wani dadewa ba suka tsinkayo muryan Yusuf a falo,
Anty Dije wace yan kan nen nata duk sun dagular mata lissafinta,
Saboda sun tayar mata da hankali, shi Yusuf yana fushin a kan anty taki yarda,ya,sai masu mota,
Ita ko maryam taurin kai kamar mutanen farko da basu yarda da sakonin su ba,
Safiya ce taiwa maryam inkiya da cewa taje tai ma Yusuf sannu da zuwa,
Ruwa yake kokarin tsiyayawa a cup don yasha,
Maryam wace ta fito saye cikin dinkin buje da riga na wani material lace, ja colour mai yan fararen duwatsu, ajikin shi,
Dinkin shi kamar maternity ya karbi jikin ta so sai yai mata kyau,
Kusan kwanaki ke nan rabo da ya sata a idon shi tun ranan da suka dawo unguwa a tare,
Cikin ladabi ta gaida shi ruwa ya ke tsiyayawa amma sai da mamakin gaisuwar da tai mai ya kama ta,
A nutse ya karba mata don zaka ce ai ba shi ba ne take gayar wa,
Sanin halin maryam da safiya tayi yasa ta fitowa ita ma daga dakin cikin fara,ar ta,
Tana gashe shi da shigowa tana kuma kokarin samun gurin da zata zauna a daya daga cikin kujerun falon,
Maryam wace duk a ta kure take saboda tana ganin cewa duk step din da tayi kamar a idon Yusuf yake,
Kitchen ta nufa gurin da Anty ke kokarin shirya mai a bincin shi,
Karban aikin tayi a hannun anty taci gaba da zuba mai,
A falon su ukune zaune a ciki Yusuf kewa Anty Dije, bayani akan tafiyar mahaifin su kasa mai tsarki,
Magana yake wa Anty dije a zahiri amma acikin zuciyar shi tunanen yakeyi maryam ce yake kallo a lokacin wace ke tafe ,
Ba komai yasa yake son yarinyar nan ba sai zaman ta irin macen da yake burin aure a rayuwar shi,
Kunya natsuwa, kamun kai, rikon Addini tarbiya da kuma sanin darajan mutane,
Itako maryam zancen da taji na tafiyan su baba shine ya ja hankalin ta,
Badon komai ba sai saboda adduan mahaifin su ke nan a kullun shi dai yatafi makka ya gano kabarin Annabi da Abubakar da nana fatima,
Duk addua sai kaji yasako wanan addu,an yau gashi Allah ya nufe shi da zuwa wanan shekaran,
Allah sarki baba ashe Yusuf ne mutumin da,zai yi sanadin sauke faralin ka
Tire din da ta dauko na abincin shi ta dire mai a gaban shi tare da kokarin jawo mai table din a gaban shi,
Nagode maryam ya ce a takaice tare da cigaba da zancen shi,
Wanan hali irin na godiyan Yusuf komai kamai kan,kantar abinda kai mai sai yayi ma godiya,
Muryan maryam ce ya dakatar da shi daga bayanin da yake wa anty, ta
A zuba ma ne ko ba yanzun zaka ci ba ta tanbaya cikin dukar da kai kasa,
No, barshi kawai na gode ya ce yana mai daga mata hannu,
Ta mike a hankali ta juya zuwa kitchen don ta rufo kofan da tabari a bude,
Ido Yusuf ya kara binta da shi yana kara mata kallo azuciyar shi ya na,addua Allah yasa haduwar su ya, zama alheri a rayuwar su da haka yadan lumshe idon shi,
Safiya wace ke gefe kuma tana nazarin duk halin da Yusuf din ke ciki ta dan murmusa daga gefe, batare da,sanin kowa ba,
Maryam wace a lokacin tadawo cikin falon tana kokarin shigewa daki safiya ce ta dan jawo ta da fira,
Tace maryam wayan nan naki ko yana yi yanzu ya daina hooking din da yake yi,
Tafida hakan cikin rashin nuna wani abu a fuskanta,
Sam mutum zai dauka cewa bada wani manufa tayi zancen, ba,
Wanan maganar na safiya yadan sa maryam din dawo wa falon
Gurin da safiya take a zaune ta nufa tana mai cewa cikinnmuryan nan na ta tankar ansa ta magana,dole ne,
Kinsan yanzu kira kawai nakeyi da shi sai kuma received din called, kawai,
Anty Dije ta mike a hankali tana cewa barin dan shiga cikin gida kafin ka gama yanzu zan dawo zan tura yaro can gidan mu gurin babane,
Anty dije tana fita gidan sai Safiya tace au na fa manta da cewa za,a kirani nabar waya daki cikin sauri ta mike zuwa dakin,
Tafiyan safiya yasa akabar su su biyu sai dan shiru ya ziyarci gurin abincin shi yake ci hankali kwance abinshi,
Jin shiru ya dan ratsa gurin yasa lokaci guda Yusuf ya juyo yana fuskantar ta,
Ba tare da yakalleta ba yana mai ci gaba da cin abincin shi yace,
Maryam kwana biyu lafiya kike ko ?
A bazata maryam taji maganar a lokacin hankalinta nagurin wayar ta da ke a hannun ta,
A hankali tadago kanta sai taga cewa ai su kadai ne agurin kawai,
Ko bakya magana ne kina tsoron kada na gudu dake tunda ba ki san koni waye ba ko, ?
Ita dai maryam murmushi kawai ta dan sake wanda iyakar shi iya fuska, batare da tayi magana ba,
Shima Yusuf di kamar yadda tai murmushin hakan ya yi nashi,
Dukawa yayi yaci gaba da,cin abincin shi a hankali kamar yadda yake yi tun farko,
Sai da ya kurba ruwa yadan jawo tissue yadan goge bakin shi ,
Sanan yace maryam nasan cewa kina mai jin zafin abinda A,A dinki yai maki ,
Maryam duk abinda babba zai hango yaro ba zai taba hango shi ba,.
Don haka kibar wa Allah al,amarinki gare shi yafi duk wani tashin hankali da zaki saka kan ki a cikki,
Ni har ga Allah idan zancen baba bai maki ba zan iya hakkuri da maganar Allah zai ban wata,
Duk da nasan cewa nadade ina mai rokan Allah akan yaban mata daidai ni ,
Bako wani irin rayuwa nake bukata daga mace ba akwai wasu hallaiya danake son macen da zan aura ta kasance dasu,
Sai ga shi ubangiji ya nufi baba da alkawaranta min
Da na diba sainaga cewa aiduk wanan abin da nake bukata kina dasu har ma kin zarta wanda nake bukatan,
Maryam kafin lokacin da baba zai bukaci jin hukuncin da muka yanke akai
Idan har kinsan cewa bakya sona ko kuma kinada wani still wanda kike so ,
To ki fada min tun zancen baiyi nisa ba saboda ni mutum ne da bani son inwa babba karya ko yaudara,
Dan shiru ne ya kara ziyartan gurin shiko Yusuf yana saurarenta ne ko za tai magana akan tambayar da yai mata,
Amma sai yaga alamar baza tai magana ba ba zata ce wani abu ba sai wasa da wayan hannun ta da takeyi,
Maryam yakara kiran sunan ta cikin wani yanayi da yasa ta rikicewa amma sai tadaure tana mai dago kai ta dan dube shi ,
Yanayin da tagani ga fuskanshi ba wasa aciki a lokacin don haka tai saurin dukar da kanta kasa tana sauraron shi,
Ki daure ki fada min ra,ayinki a ganay dani amna dan girman Allah ina rokon ki da ki fada min gaskiyar abin dake zuciyar ki,
Kada ki duba abinda ke tsakanin mu da baba ko Anty Dije,
Saboda nayi alkawari bazan taba auren macen da bata so na ko wace bana ra,ayina ba,
Ni mutum ne da bani da ra,ayin yin aure ,aure a rayuwa na,
Don haka sai wace nasan cewa tana sona ina son ta zan aura bawai don ra,ayin wani ba can daban,
Pls kada kuma kiji kunyar gaya min gaskiya don nasan ba dadi ka kalli mutun face to face kace mai baka ra,ayin shi,
Amma ni agare ni gara hakan da ka yaudari mutun kafada mai karyan don kawai yaji dadi,
Don haka maryam ina sauraren ki ki fada min ra,ayinki agamay dani pls ?
Maryam wace kanta ke aduke lokacin a cikin zuciyar ta hakika maganganun uncle gaskiyane,
Amma kuma taya zata fada mashi cewa yanzu ta amince dashi kai tsaye ya yarda da ita,
Bayan yana sane da irin yadda akai ta kwasa da ita akan shi,
Dakuma irin yadda son A,A ya ke azuciyar ta har bata iya boye,
Tambayar ta ya karayi sai taga ai kawai tafada maigaskiya zai fi,
Abin mamaki kuma sai taji bakinta yai nauyi ta furta mai ko wani irin kalma,
Saidai kuma i zuwa yanzu karyane tace bataji wani abu akan Yusuf din ba ,
Saidai tana kokarin karyata haka din da takeji a kan shi tun bayan dogon sharhin da safiya ta zaunar da ita tai mata,
Gashi kuma ya tsure ta da idon ta rasa yadda zatai magana har ta fada mai gaskiya,,
Ganin baida niyar kauda idon shi gare ta dole ta daure ta ce ma wani abu saboda tasan yin shirun nata baida mafita,
Kasa,kasa yaji muryan ta tana cewa kasan ai aure nufin Allah ne idan har Allah yakardara ni matar kace kamar yadda mahaifina ke bukata to,,,, sai kuma tai shiru batare da kara cewa komai ba,
Murmushi Yusuf din yayi yadan gyara zaman shi yace Uhum maryam kifitar da duk wani kunya da shakku kiya magana don har yanzu banji kinyi maganar da nake son ji ba
Tabbas maryam nasan aure nufin Allah ne, amma ni abin da nake son in ji shine Yusuf ina sonka ko kuma a, a yusuf bana sonka,
Da sauri tadago kanta dake duke takalle shi shima din ita yake kallo sai yadan daga mata gira yace yes,haka din ne mana gaskiya,
Hmmm kawai tace saine kuma tace, amma dai ai nayi maka bayani ko ?
Tuna dai abin da kikace a baya kawai kince Aure nufin Allah kuma mahaifinki ke bukantan kiyi,
Don haka kenan bake ke bukatan aurena ba har yanzu maganar mahaifinki ne kawai kike bi,
Cikin sauri tadago kanta don jin abindayace tare da saurin cewa Injiwa ?
Amsan da taba shiya dan sa shi dariya dan haka sai ya mike tsaye daga inda yake zaune,
Gurin da take nufa kamar daga sama taji hannunshi acikin nata saikuma taga yakai tsugune agaban ta yace,
Will you marry me ?
Gama ga maryam wace ke sauke ajiyan zuciya akai akai
Safiya ta kau da shirun da cewa ki tashi ki gyara jikin ki ki sake rayuwan ki tankar bake ce a haka ba,
Sai a lokacin maryam tai dan murmushi jin abin da safiya tace ,
Abincin rana da Anty ta,gama ne ta aiko masu da shi a daki,
Maryam tafito da kan ta ta daukan masu ruwan sha, a cikin fridge,
Sun fara cin abinci ba da wani dadewa ba suka tsinkayo muryan Yusuf a falo,
Anty Dije wace yan kan nen nata duk sun dagular mata lissafinta,
Saboda sun tayar mata da hankali, shi Yusuf yana fushin a kan anty taki yarda,ya,sai masu mota,
Ita ko maryam taurin kai kamar mutanen farko da basu yarda da sakonin su ba,
Safiya ce taiwa maryam inkiya da cewa taje tai ma Yusuf sannu da zuwa,
Ruwa yake kokarin tsiyayawa a cup don yasha,
Maryam wace ta fito saye cikin dinkin buje da riga na wani material lace, ja colour mai yan fararen duwatsu, ajikin shi,
Dinkin shi kamar maternity ya karbi jikin ta so sai yai mata kyau,
Kusan kwanaki ke nan rabo da ya sata a idon shi tun ranan da suka dawo unguwa a tare,
Cikin ladabi ta gaida shi ruwa ya ke tsiyayawa amma sai da mamakin gaisuwar da tai mai ya kama ta,
A nutse ya karba mata don zaka ce ai ba shi ba ne take gayar wa,
Sanin halin maryam da safiya tayi yasa ta fitowa ita ma daga dakin cikin fara,ar ta,
Tana gashe shi da shigowa tana kuma kokarin samun gurin da zata zauna a daya daga cikin kujerun falon,
Maryam wace duk a ta kure take saboda tana ganin cewa duk step din da tayi kamar a idon Yusuf yake,
Kitchen ta nufa gurin da Anty ke kokarin shirya mai a bincin shi,
Karban aikin tayi a hannun anty taci gaba da zuba mai,
A falon su ukune zaune a ciki Yusuf kewa Anty Dije, bayani akan tafiyar mahaifin su kasa mai tsarki,
Magana yake wa Anty dije a zahiri amma acikin zuciyar shi tunanen yakeyi maryam ce yake kallo a lokacin wace ke tafe ,
Ba komai yasa yake son yarinyar nan ba sai zaman ta irin macen da yake burin aure a rayuwar shi,
Kunya natsuwa, kamun kai, rikon Addini tarbiya da kuma sanin darajan mutane,
Itako maryam zancen da taji na tafiyan su baba shine ya ja hankalin ta,
Badon komai ba sai saboda adduan mahaifin su ke nan a kullun shi dai yatafi makka ya gano kabarin Annabi da Abubakar da nana fatima,
Duk addua sai kaji yasako wanan addu,an yau gashi Allah ya nufe shi da zuwa wanan shekaran,
Allah sarki baba ashe Yusuf ne mutumin da,zai yi sanadin sauke faralin ka
Tire din da ta dauko na abincin shi ta dire mai a gaban shi tare da kokarin jawo mai table din a gaban shi,
Nagode maryam ya ce a takaice tare da cigaba da zancen shi,
Wanan hali irin na godiyan Yusuf komai kamai kan,kantar abinda kai mai sai yayi ma godiya,
Muryan maryam ce ya dakatar da shi daga bayanin da yake wa anty, ta
A zuba ma ne ko ba yanzun zaka ci ba ta tanbaya cikin dukar da kai kasa,
No, barshi kawai na gode ya ce yana mai daga mata hannu,
Ta mike a hankali ta juya zuwa kitchen don ta rufo kofan da tabari a bude,
Ido Yusuf ya kara binta da shi yana kara mata kallo azuciyar shi ya na,addua Allah yasa haduwar su ya, zama alheri a rayuwar su da haka yadan lumshe idon shi,
Safiya wace ke gefe kuma tana nazarin duk halin da Yusuf din ke ciki ta dan murmusa daga gefe, batare da,sanin kowa ba,
Maryam wace a lokacin tadawo cikin falon tana kokarin shigewa daki safiya ce ta dan jawo ta da fira,
Tace maryam wayan nan naki ko yana yi yanzu ya daina hooking din da yake yi,
Tafida hakan cikin rashin nuna wani abu a fuskanta,
Sam mutum zai dauka cewa bada wani manufa tayi zancen, ba,
Wanan maganar na safiya yadan sa maryam din dawo wa falon
Gurin da safiya take a zaune ta nufa tana mai cewa cikinnmuryan nan na ta tankar ansa ta magana,dole ne,
Kinsan yanzu kira kawai nakeyi da shi sai kuma received din called, kawai,
Anty Dije ta mike a hankali tana cewa barin dan shiga cikin gida kafin ka gama yanzu zan dawo zan tura yaro can gidan mu gurin babane,
Anty dije tana fita gidan sai Safiya tace au na fa manta da cewa za,a kirani nabar waya daki cikin sauri ta mike zuwa dakin,
Tafiyan safiya yasa akabar su su biyu sai dan shiru ya ziyarci gurin abincin shi yake ci hankali kwance abinshi,
Jin shiru ya dan ratsa gurin yasa lokaci guda Yusuf ya juyo yana fuskantar ta,
Ba tare da yakalleta ba yana mai ci gaba da cin abincin shi yace,
Maryam kwana biyu lafiya kike ko ?
A bazata maryam taji maganar a lokacin hankalinta nagurin wayar ta da ke a hannun ta,
A hankali tadago kanta sai taga cewa ai su kadai ne agurin kawai,
Ko bakya magana ne kina tsoron kada na gudu dake tunda ba ki san koni waye ba ko, ?
Ita dai maryam murmushi kawai ta dan sake wanda iyakar shi iya fuska, batare da tayi magana ba,
Shima Yusuf di kamar yadda tai murmushin hakan ya yi nashi,
Dukawa yayi yaci gaba da,cin abincin shi a hankali kamar yadda yake yi tun farko,
Sai da ya kurba ruwa yadan jawo tissue yadan goge bakin shi ,
Sanan yace maryam nasan cewa kina mai jin zafin abinda A,A dinki yai maki ,
Maryam duk abinda babba zai hango yaro ba zai taba hango shi ba,.
Don haka kibar wa Allah al,amarinki gare shi yafi duk wani tashin hankali da zaki saka kan ki a cikki,
Ni har ga Allah idan zancen baba bai maki ba zan iya hakkuri da maganar Allah zai ban wata,
Duk da nasan cewa nadade ina mai rokan Allah akan yaban mata daidai ni ,
Bako wani irin rayuwa nake bukata daga mace ba akwai wasu hallaiya danake son macen da zan aura ta kasance dasu,
Sai ga shi ubangiji ya nufi baba da alkawaranta min
Da na diba sainaga cewa aiduk wanan abin da nake bukata kina dasu har ma kin zarta wanda nake bukatan,
Maryam kafin lokacin da baba zai bukaci jin hukuncin da muka yanke akai
Idan har kinsan cewa bakya sona ko kuma kinada wani still wanda kike so ,
To ki fada min tun zancen baiyi nisa ba saboda ni mutum ne da bani son inwa babba karya ko yaudara,
Dan shiru ne ya kara ziyartan gurin shiko Yusuf yana saurarenta ne ko za tai magana akan tambayar da yai mata,
Amma sai yaga alamar baza tai magana ba ba zata ce wani abu ba sai wasa da wayan hannun ta da takeyi,
Maryam yakara kiran sunan ta cikin wani yanayi da yasa ta rikicewa amma sai tadaure tana mai dago kai ta dan dube shi ,
Yanayin da tagani ga fuskanshi ba wasa aciki a lokacin don haka tai saurin dukar da kanta kasa tana sauraron shi,
Ki daure ki fada min ra,ayinki a ganay dani amna dan girman Allah ina rokon ki da ki fada min gaskiyar abin dake zuciyar ki,
Kada ki duba abinda ke tsakanin mu da baba ko Anty Dije,
Saboda nayi alkawari bazan taba auren macen da bata so na ko wace bana ra,ayina ba,
Ni mutum ne da bani da ra,ayin yin aure ,aure a rayuwa na,
Don haka sai wace nasan cewa tana sona ina son ta zan aura bawai don ra,ayin wani ba can daban,
Pls kada kuma kiji kunyar gaya min gaskiya don nasan ba dadi ka kalli mutun face to face kace mai baka ra,ayin shi,
Amma ni agare ni gara hakan da ka yaudari mutun kafada mai karyan don kawai yaji dadi,
Don haka maryam ina sauraren ki ki fada min ra,ayinki agamay dani pls ?
Maryam wace kanta ke aduke lokacin a cikin zuciyar ta hakika maganganun uncle gaskiyane,
Amma kuma taya zata fada mashi cewa yanzu ta amince dashi kai tsaye ya yarda da ita,
Bayan yana sane da irin yadda akai ta kwasa da ita akan shi,
Dakuma irin yadda son A,A ya ke azuciyar ta har bata iya boye,
Tambayar ta ya karayi sai taga ai kawai tafada maigaskiya zai fi,
Abin mamaki kuma sai taji bakinta yai nauyi ta furta mai ko wani irin kalma,
Saidai kuma i zuwa yanzu karyane tace bataji wani abu akan Yusuf din ba ,
Saidai tana kokarin karyata haka din da takeji a kan shi tun bayan dogon sharhin da safiya ta zaunar da ita tai mata,
Gashi kuma ya tsure ta da idon ta rasa yadda zatai magana har ta fada mai gaskiya,,
Ganin baida niyar kauda idon shi gare ta dole ta daure ta ce ma wani abu saboda tasan yin shirun nata baida mafita,
Kasa,kasa yaji muryan ta tana cewa kasan ai aure nufin Allah ne idan har Allah yakardara ni matar kace kamar yadda mahaifina ke bukata to,,,, sai kuma tai shiru batare da kara cewa komai ba,
Murmushi Yusuf din yayi yadan gyara zaman shi yace Uhum maryam kifitar da duk wani kunya da shakku kiya magana don har yanzu banji kinyi maganar da nake son ji ba
Tabbas maryam nasan aure nufin Allah ne, amma ni abin da nake son in ji shine Yusuf ina sonka ko kuma a, a yusuf bana sonka,
Da sauri tadago kanta dake duke takalle shi shima din ita yake kallo sai yadan daga mata gira yace yes,haka din ne mana gaskiya,
Hmmm kawai tace saine kuma tace, amma dai ai nayi maka bayani ko ?
Tuna dai abin da kikace a baya kawai kince Aure nufin Allah kuma mahaifinki ke bukantan kiyi,
Don haka kenan bake ke bukatan aurena ba har yanzu maganar mahaifinki ne kawai kike bi,
Cikin sauri tadago kanta don jin abindayace tare da saurin cewa Injiwa ?
Amsan da taba shiya dan sa shi dariya dan haka sai ya mike tsaye daga inda yake zaune,
Gurin da take nufa kamar daga sama taji hannunshi acikin nata saikuma taga yakai tsugune agaban ta yace,
Will you marry me ?