← Book details Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 143 OF 171

Sashe 143

Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A hankali ta sako daga kan gadon ta,, ta na kokarin taka, kasa, amma tankar ansa ta takawa dole ne saboda irin yadda take jin tafin kafar ta yai mata nauyi,
Toilet ta fada ta watsa ruwa saboda nauyin da take jin jikin ta yai mata,
Daga haka ta dauro awala tazo zuwa gabatar da sallah,
Bayan idar da sallah takai wani lokaci, a gurin zaune a takure, sai ta baka tausayi,
Wani tunane ya a zuciyar ta, nan da nan gaban ta ya fadi tawani runtse idanun ta,
Yanzu ita ya zata iya rayuwa da Yusuf a. matsayin mijin ta
Wani irin taji a zuciyar ta. Inda ta runtse idon ta cikin jin kunan a zuciyar ta,
Ita da wani ido zata kalle shi wai mijin ta yau, ita ya zata zauna da shi a matsayin zaman rayuwar aure,
Ita ya zatai zama da yan uwan Yusuf kafirai arna a matsayin yan uwan miji dangin miji,
Ya kuma zata kwashe da yan matan shi da tun ba,a kai ko ina ba har sun fara kai mata hari,
Hawayen da ya taru tun farko a idon nata sune suka samu hanyar sulalowa,
Bayan hannun ta tasa ta dan share hawayen a hankali,
Dago kan da zatayi sai sukayi ido biyu da Anty ta wace ke tsaye tana kallon ta, cikin daure fuska,
Inda take zaune tanufa ta samu saman stol din gado dake gefe ta zauna cikin damuwa ,
Maryam ban san may zan fada maki ba wanda zai sa ki yarda ki daina wanan halin,
Maryam tadago indon ta da sukai jajajir tace dagani taci kuka, har ta gaji,
Idan zakiyi hakkuri kiyi maryam kiroki Allah yasa hakan yafi zama maki alheri,
Amma ba ki zauna kina ta rusa kuka har ki jawa kanki matsalar rayuwa,
Still hannun ta ta kara sawa tagoge fuskan ta da yakoma kamar kamfanin fanfo,
Saman jikin anty ta fada tana ta rusan kuka har sai da tasa duk daurewan Anty itama saida tai kukan,
Ya illiya mijin Anty Dije ya katse masu kukan inda ya kira wayan yana tambayar matar yadda abubuwa ke guda na,
Daga karshe yace abashi maryam din yana da magana da ita,
Yace maryam ta ansa da naam cikin muryan kuka wanda yasa har saida yaji wani irin tausayin ta yakama shi,
Maryam bana son wanan kukan da kikeyi pls, ki saurareni da kyau ki kwantar da hankalin ki, kiji abinda zan fada maki,
Don dole badon taso ba tai shiru tana sauraren abinda mijin yar nata ke ce mata,
Sai kai take kadawa alamar to ya cigaba da mata nasiha,,
Nasiha masu ratsa jigi ya ya iliyan yai mata wanda don dole badon taso ba tai shiru, saboda maganganun sun bi jikin ta,
Sosai maganar shi tasa maryam dan sakewa don daren ranan har taci abinci kadan,
Sai dai rashin kuzarin da bata dashi don ta kasa sake jikin ta,
Safiya ce ta fado mata a rai don duk wanan tashin hankalin da take ciki alamu ya nuna safiya din bata da labari akai,
Kira guda gana biyu ta dauki wayan tana cewa yar halas kin ki ambato yanzu umma ke tambayar kwana biyu wai baki shigo ba,
Jin shiru yasa safiya din cewa hello, muryan maryam kawai ya tabbatar mata ba lafiya,
Cikin kuka maryam tace Safiya baba yadaura min aure yau,
What inji Safiya tace wa maryam cikin daga sautin tambayam ta,
Shehekan kukan da taji maryam din nayi ya tabbatar ma da maganar gaskiya maryam din ke yi,
Duk da dare ya soma a lokacin hakan bai hana Safiya neman izini gurin mahaifiyar ta ba,
Kwatsa sai ganin ta sukayi tayi sallama, a gidan
Lokacin maryam wace ta dunkule a cikin bargo saboda sanyin da takeji ga ruwan sama an lema agarin,wuri ya dauki sanyi,
Anty ce take mamakin ganin safiya ciki dare saboda bata saba,zuwa a wanan lokacin ba,
Amma kuma sai ta nasa cewa ai kila safiya din ta samu labarin abinda ya faru da aminiyar ta,
Bayan sun gaisa ne Anty dije din tace wa safiya sai kikaji labari kwatsam ko,
Ki shiga tana ciki ai don haka safiya, ta shige dakin su maryam din cikin damuwa,
Ganin yadda yaga maryam din a kwance yasa ta karasa gurin ta da,sauri tadan dafa goshin kan ta,
Sai a lokacin maryam din ta bude idon ta ganin safiya ce yasa ta,saurin rungumota zuwa jikin ta,
Nan suka dan yi kukan su suka,share hawayen su saboda kukan bashine mafita ba,

Tun da gari yawaye yake ta faman aiwatar da,duk wasu abubuwan da yake da bukatan yi don ya samu ya koma Abuja ,
Abinda yafi bashi mamaki shine rashin kiran shi da,su KB basu yi duk cikin wanan lokacin shima dai share su yayi ya kama abinda ke agaban shi,
Jirgn yamma yabi zuwa Abuja don haka acikin dare ya isa Abuja,
Driver shi yazo yadauke shi zuwa gida duk da agajiye ya ke bai hana shi daga waya ya kira mahaifin shi ba,
Don yaji lafiyan jikjn shi saboda yakira kafin ya taso akace yana barci ai,
Yanzu da yakira bayan shigan shi gida ko daki bai shiga ba yakira don yaji,
Inda yai sa,a ance yana zaune don haka aka bashi waya don su gaisa da mahaifin na shi,
Maganar farko da Mr Emanuel yayi shi ne, Joseph are you married with a hausa girl,?
Daddy just relax iam coming home tomorrow insha Allah,
Jin haka yasa Mr Emanuel's saurin kashe wayan,
Yusuf wanda yadda mahaifin nashi yai mai ya san cewa a kwai magana agaba,
Saidai yana mai rokon Allah akan duk abinda zai faru Allah yakawo mai sauki,
Daga haka ya haura zuwa sama don ya watsa ma jikin shi ruwa huta,
Daga haka bai kara saukowa kasa ba don yana bukatan hutawa a tare da shi,

Tunda safe babane ke sallama akofan gida jin muryan shi yasa kowa dake gidan tsinkewa saboda, ansa da akwai abinda ya kawo shi,
Daguda guda suka dinga fitowa har Safiya din wace ta kwana gidan don taya aminiyar ta jamame,
Sun gashe shi a cikin mutunci da kuma girmamawa irin yadda diya kewa iyayen su,
Baba wanda yake tsaye daga kofan shigowa yadan jim
Can ya kalli inda maryam take tsugune cikin zumbulelen hijabi, yace,
Maryam , maryam wace jin an kara kiran sunan ta yauma din tadago takai kallonta gare shi a cikin girmamawa tace Na,am Baba,
Yace Allah yai maki albarka kin ji Allah ya sa wa auren ki Albarka ,
Sai kuma yai shiru can yace ina Dije ?
Anty Dije takarba dacewa Na,am baba
Baba yace ban so ance jiya wanan yarinyar ta kwana gidan nan ba naso ace ta kwana adakin mijin ta,
Gaba dayan su suka dago kai suna kallon mahaifin nasu,
Yace na tuntubi shi malam mudi yace min abari har yaron yazo gari a ji ta bakin shi,
Don haka sai ki zauna da shirin yar uwar taki akan duk ranan da mijin ta yazo zata tare a dakin ta ne
Dafatan kin fahinci abinda nake nufi akan zance na,
Anty Dije ta gyada kan ta tare da cewa eh baba shiru yadan yi yana kallon su yace
Allah yai maku albarka Allah yabaku zuri,a masu albarka,
Daga haka yasa kai zai wuce, sai kuma ya juyo gurin da Anty Dije take yadan juya yace bani son samun wani matsala,
Anjima zandawo don muyi maganar dan abinda za,a sai mata,
Sai a lokacin Anty Dije ta samu bakin magana tun shigowar baba gidan,
Tace to amma baba bisa ga hukuncin da naji ka yanke na cewa da yazo ranan zata tare ,
Sai naga cewa ba,a fa yi wani shiri ba akan tarewan
Don may baza a dan dakata harzuwa lokacin da za a shirya,
Ke inji baba cikjn muryan da har saida ta dan razana yace,
Ni komai nawa na dogora ga Allah wani shirine can,
Abinda Allah ya hore min shi zamu kai mata tayi hakkuri yadda kowa yayi,
Ina fatan kun fahinta da magana na don kadaazo ace min ga kara ka itace,
Daga haka yasa kai ya wuce nan ya barsu a cikin tashin hankali,
Daki maryam ta fada sai kawai ta ji hawaye ya na silalo, mata daga idon ta saboda hukuncin da baba ya yanke a kan ta,
A daki maryam ce da aminiyar ta tana bata shawara akan tayi hakkuri da kaddaran ta,
Shawarwari da dama Safiya din ta dinga ba maryan har taji hankalinta ya dan kwanta,
Ànty Dije tun da tashirya tafita zuwa gidan wata aminiyar ta da suke siri
Duk da matar ta girmay ta sosai sai amma suna siri da mutunci a tsakanin su,
Saida taima matar bayanin abinda baba yazo masu da shi yau da safe,
Na akan lalai sai dai maryam ta tare duk randa mijin ta yazo garin,
Matar tai dariya tace wa dije wanan ai baika na ta da hankali ba,
Don haka yanzu zan dan fita in je in fara samo hakki bakin daji,
Anty Dije tace kai haba ke da anyi zance saiki maganar akan zancen gyaran harka,
Nizancen abinda zan wa maryam na gyaran gida da dakina ke magana,
Kai, matar ta kada tace aikin banza Dije, ai wanan abin shine babban tsaraba da yadace mugyara yafi wanan kayan banzan da kike zance,
Saboda ai shi kayan daki babu inda sunna yace an halattawa mutun shi ko ?

ZEEE MAKAWA YALWA
[5/3, 10:49 AM] ‪+234 706 262 3470‬: 🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
8⃣5⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI

Bazan iya matawa da ku ba masoya wanan novel din kaunar da shi tankar a gare ni ne nagode nagode nagode Allah yakara rufa asiri a rayuwa,,,,
Chapter 143 · 0% Book details