Sashe 53
Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ZEEE MAKAWA
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
3⃣4⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,
Barkan da jumma,a yan ,uwa Allah ubangiji yasada mu da alherin dake cikin wanan ranar mai albarka,👏👏👏
Maganar da Abdulsamad ya fadawa Yusuf gamay da mahaifin shi ya tsaya mai arai, sosai,
Don haka yasan cewa ko shi bai tsira ba ke nan don mahaifin nashi zai iya yin fiye da haka akan church din nasu,
Don haka ya sa a,zuciyar shi cewa, dole ya dauki duk wani mataki wanda yasan cewa ,za,a iya kawo mai hari akai,
Washe gari ya kasance ranar jumma,a ce, don haka tunda zai fito ya fito da kayan da zai shirya kanshi a ciki
Don barci kawai yakaishi gidan su cikin dare sai dai ya kula da cewa kamar an,masa bincike a dakin,
Murmushi yake yayi shi kadai a cikin dakin, don haka duk wani abin da yake bukata ya hada su guri guda,
Tunda safe da zai fita yakwasa sai gidan, Ànty shi Dije itace yakai wa ajiyar kayan shi masu muhinmanci, dake gidan nasu,
Maryam wace ke zaune a lokacin gaban mirrow tana make-up,
Taji muryan shi ya na ta kwada sallama akofar shigowa gidan ,
Haka kawai taji zuciyar ta ya tsinke mata, kamar mai tsoro,
Zubur ta dan yi ta mike a gaban mirrow saboda ta sheda ko muryan waye, ke sallamar,
Saidai, yau ta tsinci kanta da dan jin nauyin ansa mai sallamar tashi,
Saboda irin yadda tai hating din shi a matsayin shi na Christian a da,
A,ciki ciki ta ansa mai sallamar tashi, kamar wace ke rowar magana,
Dankwalin da tafara daurawa rike a hannun ta tadan leko tawaje don tabashi izinin shigowa ciki,
Saboda Anty Dije tana bayi gurin wanka alokacin,
Ido biyu sukayi dashi, yana saye da wata riga mai hannu iya damtsen hannu, sai wani dan ado da akaiwa hannun rigar kamar kwalar riga ta wuya,
Shima wuyar rigan irin hannun rigar ce akai yi ta,
Sannu da zuwa ta furta acikin muryan ta makama da ta rowa kullun,
Sai kuma can tace tadan shiga wanka yanzu zata fito
Abinda kawai ta iya fada ke nan a darare, kamar mai jin tsoro,,
Fuskan shi a natse kamar kulun yace ba matsala ga wanan pls ki bata ta aje min zan je in dawo,
Sigar da yake maganar shiya sata dan dukar dakai don komai nashi a kasaice yakeyin shi,
A, hankali yatako har, gaban,ta ya mika mata jarka
Wace batasan ko tamaye ba,ita,dai ta karbane kawai,
Har yabar gidan tana tsaye a inda ya barta rike da jarkar da ya miko mata,
Karar rufe kofar shiga gidan ce tasa,
Da sauri ta juya zuwa ciki, sai yanzu ma taji haushin fitar da tayi da tasani ma kawai ta amsa mai ata cikin daki,
Turus tayi a folon ganin, Ànty Dije zaune tana shiri abinta acikin natsuwa,
Anty ce tace tomay zance tunda kin ce masa na shiga wanka ko,
Inda take ta nufa da jakar ta aje saman wani kujera tafita batare da tai wani magana ba,
Yusuf kuwa yana barin gidan su Anty, kasuwa yatafi
Abinda yaksi shi kawai shine yasamu shago babba mai kyau yasaya,
Allah yabashi sa,a yasamu shago irin wanda yake so,
Ba bata lokaci akai komai yasa hannu ya biya,
Kafin tabar gurin har cikin IBO dake layin sun sheda wa mahaifin shi cew gashi a kasuwa yana diban shago,
Ganin lokacin sallah jumma,a yana gabatowa shiyasa yai haramar komawa, gidan su Anty
Tafe yake yana shawara a,ranshi cewa gobe zai tafi gurin mahaifinshi,yasanar dashi,
Cewa ya sai ma Abdulsamad shago saboda Allah da Annabi
Saboda duk irin halin kuncin da ya jefa Abdulsamad din saboda akidar addini yasani,
Don haka zai fara sanar dshi cewa sun san mugun halinshi akan wanda duk ya canza addini daga cikin su,
Yasan idan har yafada mai garan dagaran zai samu saukin duk wani kulli da zasuyi mai,
Yana cikin shawarar ne azuciyar shi har ya kawo kofar gidan Anty Dije,
Wanda kawo,war yai dai,dai da lokacin da A,A shima yake kokarin aje motar shi don sauke maryam,
Da ya dauko daga school, don yau jumma,a bata wani dadewa, a school din
Sun,na zaune acikin mota, suna dan taba hira saidai kafarta guda yana a tawaje da sauran jikinta,
Hikimar yin haka gareta shine kare zargin yan unguwa masu sa ido a masu zama da maza cikin mota suna masu suna,
Kallo guda yai masu ya,kauda kai, gefe, guda batare da yakara ba,
Don yarasa komay yasa sam baya son yagan su atare da wanan guy din,
Yasamu Anty ta aje mai abin karyawa a falon ta bayan sun gaisa ta gabatar mai da abin kari, kumallo,
Sai yaji wani irin kara girmamata yashige shi shiyasa yake son al,amarin ta, don tana saurin fahintar shi,
Muryan ta yaji tana cewa, tasan cewa baici komaiba har yazu saidai tana gani abincin yai sanyi ko zuwa yanzu,
Ya zauna ke nan da niyar fara ci maryan tashigo gida cikin takon takalmanta da ke fidda sauti,
Tundaga kofa tai arba dashi cikin sauri takawar da kanta gare ahi adaidai, lokacin da yake kokatin zuba ruwan zafi a cup
Duk da takwaso nata kalar yunwa baisa ta tsaya don ta,karya ba sai shigewar ta tayi kawai aciki
Anty Dije ce tasa mata kira don tasan cewa itama bataci komai ba tau tabar gidan
Alokacin maryam harta cire hijab dinta daga ita sai wani English wear buje da riga masu kamar son shagewa a jikin mutum,
Sam har ta manta da cewa akwai mutun a gidan nasu,
Don haka bata tsaya sa wani hijab ba kawai falon ta fado
Duk yadda taso ta tare jikinta hakan bai yi ba saboda kayan sunyi mata masifar kyau,
Shiko Yusuf kallo daya yai mata yakauda, kan shi gare ta
Abinda baka ra,ayi ko ya yake bazaka sahi arayuwa,ba,
Tunda bawai wani abune atsakanin su ba baiko dauki ganin ta haka dayayi dawata manufa ba, shi,
Itako sai kokarin kamay,kamay takeyi, don kada yakalli surar jikin ta,
Wayar shi ce ta sa kara alamar kira,,
Aisha ya furta a hankali, sai kuma alamar yar murshi dayayi alokacin
Hakan ya,tabbatar masu gabadayan su cewa da Aisha yake wayar,
Maryam ta juya bayan tace wa Anty ba ta jin yunwa,,
Tashige abinta batare da tatsaya jin kwam ba awayar da yake yi,
Bai wani dade ba yai ma anty dije sallama yace zai je ya shirya yazo tadauki Assalam su tafi, massalaci,
Shiga,sosai yayi na Muslims farar shadda ce dinkin ta,zarce
Wani hula yasa mai ruwan, siminti, sai takalma shige hular kan shi,
Kamshi agurin shi ba,a maganar, yana rike da wani bakin tasbaha kiran China,
Bai wani tsayawa ba don yana sauri, luckily ya samu an shirya Assalam ko, suka tafi,
Maryam wace ke tsaye daidai kofa ta sauke wani sanyayar ajiyar zuciya,
Ta waiga ida anty take tace cikin tabe baki yayi sa,a gaskiya da Allah yanufe shi yakarba kira,
Murmushi Anty Dije taimata tace abin ai daga Allah ne maryam,
Shiyasa mutum idan kasan farkon shi aibakasan karshen shi ba,
Sun isa massalaci anata zuba sahun a ko wani bangare,
Tareda Abdusamad sai jibrin da KB da suka uso da ranan nan, sai Ibrahim da yake acikin su,
Ido akan su caaaa wasu duk da a cikin massalacine harda leke sukeyi idan an nuna masu shi,
Hakan sai bai wa Yusuf dadi ba saboda irin yadda ake mai babu ko boyo, aciki,
A, cikin zuciyar shi yace, to komay kuma ya yi da ake mai haka,
Don shi ai tsan mani yayi za,ai farin ciki da kasancewar shi acikin wanan massallacin mai,albarka wanda yatara dinbi musulmai,
Duk da ana sallah amma wasu yan gulma idon su yana kan shi don suga yaya zaigi sallah shi,
Bayan an sallamay sai kawai sukaji ana, musuluntar nashi a she mahaifin jibrin ne yabada wanan sanar wan
Aiko mutane sai nunafarin cikin su sukeyi don dama andade ana rade radi,
Da kyat suka samu su kabar harabar massalacin don yawan jama,a masuyi mashi barka,
Labari ya iske Mr Ema cewa ga abinda yafaru a massalaci wanda wasu musulman mune suka kwarmatawa wasu daga cikin Ibon garin,
Mr Ema shida yan tawagar church har mada na wasu churches din sukayo kwamiti zuwa gidan Sarkin Sudan, cikin fada,
Don su azaton su, zadu ita shawo kanshi, jira sukeyi su gama aiwatar da shirin su,
Sai gashi anyi anoucement, a massalacin jumma,a cewa ya musulun ta,
Sarki yasa aka tare su, cikin dan mutunci,
Inda yasa sugabatar da abinda,ke tafe dasu
Rankashidade, muna karan wasu yaran musullumine gurinka cewa su ja yalon mu zuwa ciciin Muslims,
Batare da bakin mahaifinci ba,
Eheh, shine munzo mu fada ma,ka, shewa, muna son abamu yalonamu, afido dashi daga shikin isalama,wanda ya ciga,,,
Bayan mai martaba yagama jin korafin su ne, yadan magana da galadima,da waziri,
Galadima ya ari bakin mai sudan yai masu bayani kamar haka,
Muna son kuzo da yaron na ku nan don muji ta bakin shi, sanan, a kira wa,yanda suka maidashi ciki,
Fita sukayi daga wajen fadar maimartaba Sarki Sudan
Suna ta kus,kus ta yadda zasuyi su kawo Joseph gurin sarki,
Shi Mr Ema dakanshi, ya kira Joseph da wayar shi, kira daya ana biyu ya dauka,
Joseph come nd meet me in mai Sudan palace now,now
Yusuf wanda ke tare dasu KB suna wani estimate, din kaya,
Abin yabashi mamaki ya kalli su KB yace masu cikin bacin rai wai Dad dina ne fadar mai sudan,
Duk kan su cikin mamaki, sukace gurin mai Sudan fa,?
Sun so su bi shi sutafi tare amma yusuf din yace su bari kawai zai iya zuwa,
Mr, Ema tare dasu Ekewa, da su Barnabas Mr Ema wanda ke zaune cikin damuwa ya saye da wani rigar yadi mai hoton giwa, dajan colur, sai wani jar hula dayasa akan shi,
Yana rike da sanda a hannun shi,,maikama da kan gunki
Kallo guda zakai ai kane cewa yau rayuwar shi ba tada dadi sam,
Su na ganin shi sukayo kanshi caaa kamar zasu ciye shi danye acikin yare suke magana suna cemai, ya taimaki rayuwar shi kada ya bari wasu su rude shi,
Kowa daga cikin su da abinda yake fadi, don dai kawai ya amsa cewa bai musulunta ba,
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
FUREN JUJI
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
3⃣4⃣
ZAINAB IDRIS MAKAWA,,,
Barkan da jumma,a yan ,uwa Allah ubangiji yasada mu da alherin dake cikin wanan ranar mai albarka,👏👏👏
Maganar da Abdulsamad ya fadawa Yusuf gamay da mahaifin shi ya tsaya mai arai, sosai,
Don haka yasan cewa ko shi bai tsira ba ke nan don mahaifin nashi zai iya yin fiye da haka akan church din nasu,
Don haka ya sa a,zuciyar shi cewa, dole ya dauki duk wani mataki wanda yasan cewa ,za,a iya kawo mai hari akai,
Washe gari ya kasance ranar jumma,a ce, don haka tunda zai fito ya fito da kayan da zai shirya kanshi a ciki
Don barci kawai yakaishi gidan su cikin dare sai dai ya kula da cewa kamar an,masa bincike a dakin,
Murmushi yake yayi shi kadai a cikin dakin, don haka duk wani abin da yake bukata ya hada su guri guda,
Tunda safe da zai fita yakwasa sai gidan, Ànty shi Dije itace yakai wa ajiyar kayan shi masu muhinmanci, dake gidan nasu,
Maryam wace ke zaune a lokacin gaban mirrow tana make-up,
Taji muryan shi ya na ta kwada sallama akofar shigowa gidan ,
Haka kawai taji zuciyar ta ya tsinke mata, kamar mai tsoro,
Zubur ta dan yi ta mike a gaban mirrow saboda ta sheda ko muryan waye, ke sallamar,
Saidai, yau ta tsinci kanta da dan jin nauyin ansa mai sallamar tashi,
Saboda irin yadda tai hating din shi a matsayin shi na Christian a da,
A,ciki ciki ta ansa mai sallamar tashi, kamar wace ke rowar magana,
Dankwalin da tafara daurawa rike a hannun ta tadan leko tawaje don tabashi izinin shigowa ciki,
Saboda Anty Dije tana bayi gurin wanka alokacin,
Ido biyu sukayi dashi, yana saye da wata riga mai hannu iya damtsen hannu, sai wani dan ado da akaiwa hannun rigar kamar kwalar riga ta wuya,
Shima wuyar rigan irin hannun rigar ce akai yi ta,
Sannu da zuwa ta furta acikin muryan ta makama da ta rowa kullun,
Sai kuma can tace tadan shiga wanka yanzu zata fito
Abinda kawai ta iya fada ke nan a darare, kamar mai jin tsoro,,
Fuskan shi a natse kamar kulun yace ba matsala ga wanan pls ki bata ta aje min zan je in dawo,
Sigar da yake maganar shiya sata dan dukar dakai don komai nashi a kasaice yakeyin shi,
A, hankali yatako har, gaban,ta ya mika mata jarka
Wace batasan ko tamaye ba,ita,dai ta karbane kawai,
Har yabar gidan tana tsaye a inda ya barta rike da jarkar da ya miko mata,
Karar rufe kofar shiga gidan ce tasa,
Da sauri ta juya zuwa ciki, sai yanzu ma taji haushin fitar da tayi da tasani ma kawai ta amsa mai ata cikin daki,
Turus tayi a folon ganin, Ànty Dije zaune tana shiri abinta acikin natsuwa,
Anty ce tace tomay zance tunda kin ce masa na shiga wanka ko,
Inda take ta nufa da jakar ta aje saman wani kujera tafita batare da tai wani magana ba,
Yusuf kuwa yana barin gidan su Anty, kasuwa yatafi
Abinda yaksi shi kawai shine yasamu shago babba mai kyau yasaya,
Allah yabashi sa,a yasamu shago irin wanda yake so,
Ba bata lokaci akai komai yasa hannu ya biya,
Kafin tabar gurin har cikin IBO dake layin sun sheda wa mahaifin shi cew gashi a kasuwa yana diban shago,
Ganin lokacin sallah jumma,a yana gabatowa shiyasa yai haramar komawa, gidan su Anty
Tafe yake yana shawara a,ranshi cewa gobe zai tafi gurin mahaifinshi,yasanar dashi,
Cewa ya sai ma Abdulsamad shago saboda Allah da Annabi
Saboda duk irin halin kuncin da ya jefa Abdulsamad din saboda akidar addini yasani,
Don haka zai fara sanar dshi cewa sun san mugun halinshi akan wanda duk ya canza addini daga cikin su,
Yasan idan har yafada mai garan dagaran zai samu saukin duk wani kulli da zasuyi mai,
Yana cikin shawarar ne azuciyar shi har ya kawo kofar gidan Anty Dije,
Wanda kawo,war yai dai,dai da lokacin da A,A shima yake kokarin aje motar shi don sauke maryam,
Da ya dauko daga school, don yau jumma,a bata wani dadewa, a school din
Sun,na zaune acikin mota, suna dan taba hira saidai kafarta guda yana a tawaje da sauran jikinta,
Hikimar yin haka gareta shine kare zargin yan unguwa masu sa ido a masu zama da maza cikin mota suna masu suna,
Kallo guda yai masu ya,kauda kai, gefe, guda batare da yakara ba,
Don yarasa komay yasa sam baya son yagan su atare da wanan guy din,
Yasamu Anty ta aje mai abin karyawa a falon ta bayan sun gaisa ta gabatar mai da abin kari, kumallo,
Sai yaji wani irin kara girmamata yashige shi shiyasa yake son al,amarin ta, don tana saurin fahintar shi,
Muryan ta yaji tana cewa, tasan cewa baici komaiba har yazu saidai tana gani abincin yai sanyi ko zuwa yanzu,
Ya zauna ke nan da niyar fara ci maryan tashigo gida cikin takon takalmanta da ke fidda sauti,
Tundaga kofa tai arba dashi cikin sauri takawar da kanta gare ahi adaidai, lokacin da yake kokatin zuba ruwan zafi a cup
Duk da takwaso nata kalar yunwa baisa ta tsaya don ta,karya ba sai shigewar ta tayi kawai aciki
Anty Dije ce tasa mata kira don tasan cewa itama bataci komai ba tau tabar gidan
Alokacin maryam harta cire hijab dinta daga ita sai wani English wear buje da riga masu kamar son shagewa a jikin mutum,
Sam har ta manta da cewa akwai mutun a gidan nasu,
Don haka bata tsaya sa wani hijab ba kawai falon ta fado
Duk yadda taso ta tare jikinta hakan bai yi ba saboda kayan sunyi mata masifar kyau,
Shiko Yusuf kallo daya yai mata yakauda, kan shi gare ta
Abinda baka ra,ayi ko ya yake bazaka sahi arayuwa,ba,
Tunda bawai wani abune atsakanin su ba baiko dauki ganin ta haka dayayi dawata manufa ba, shi,
Itako sai kokarin kamay,kamay takeyi, don kada yakalli surar jikin ta,
Wayar shi ce ta sa kara alamar kira,,
Aisha ya furta a hankali, sai kuma alamar yar murshi dayayi alokacin
Hakan ya,tabbatar masu gabadayan su cewa da Aisha yake wayar,
Maryam ta juya bayan tace wa Anty ba ta jin yunwa,,
Tashige abinta batare da tatsaya jin kwam ba awayar da yake yi,
Bai wani dade ba yai ma anty dije sallama yace zai je ya shirya yazo tadauki Assalam su tafi, massalaci,
Shiga,sosai yayi na Muslims farar shadda ce dinkin ta,zarce
Wani hula yasa mai ruwan, siminti, sai takalma shige hular kan shi,
Kamshi agurin shi ba,a maganar, yana rike da wani bakin tasbaha kiran China,
Bai wani tsayawa ba don yana sauri, luckily ya samu an shirya Assalam ko, suka tafi,
Maryam wace ke tsaye daidai kofa ta sauke wani sanyayar ajiyar zuciya,
Ta waiga ida anty take tace cikin tabe baki yayi sa,a gaskiya da Allah yanufe shi yakarba kira,
Murmushi Anty Dije taimata tace abin ai daga Allah ne maryam,
Shiyasa mutum idan kasan farkon shi aibakasan karshen shi ba,
Sun isa massalaci anata zuba sahun a ko wani bangare,
Tareda Abdusamad sai jibrin da KB da suka uso da ranan nan, sai Ibrahim da yake acikin su,
Ido akan su caaaa wasu duk da a cikin massalacine harda leke sukeyi idan an nuna masu shi,
Hakan sai bai wa Yusuf dadi ba saboda irin yadda ake mai babu ko boyo, aciki,
A, cikin zuciyar shi yace, to komay kuma ya yi da ake mai haka,
Don shi ai tsan mani yayi za,ai farin ciki da kasancewar shi acikin wanan massallacin mai,albarka wanda yatara dinbi musulmai,
Duk da ana sallah amma wasu yan gulma idon su yana kan shi don suga yaya zaigi sallah shi,
Bayan an sallamay sai kawai sukaji ana, musuluntar nashi a she mahaifin jibrin ne yabada wanan sanar wan
Aiko mutane sai nunafarin cikin su sukeyi don dama andade ana rade radi,
Da kyat suka samu su kabar harabar massalacin don yawan jama,a masuyi mashi barka,
Labari ya iske Mr Ema cewa ga abinda yafaru a massalaci wanda wasu musulman mune suka kwarmatawa wasu daga cikin Ibon garin,
Mr Ema shida yan tawagar church har mada na wasu churches din sukayo kwamiti zuwa gidan Sarkin Sudan, cikin fada,
Don su azaton su, zadu ita shawo kanshi, jira sukeyi su gama aiwatar da shirin su,
Sai gashi anyi anoucement, a massalacin jumma,a cewa ya musulun ta,
Sarki yasa aka tare su, cikin dan mutunci,
Inda yasa sugabatar da abinda,ke tafe dasu
Rankashidade, muna karan wasu yaran musullumine gurinka cewa su ja yalon mu zuwa ciciin Muslims,
Batare da bakin mahaifinci ba,
Eheh, shine munzo mu fada ma,ka, shewa, muna son abamu yalonamu, afido dashi daga shikin isalama,wanda ya ciga,,,
Bayan mai martaba yagama jin korafin su ne, yadan magana da galadima,da waziri,
Galadima ya ari bakin mai sudan yai masu bayani kamar haka,
Muna son kuzo da yaron na ku nan don muji ta bakin shi, sanan, a kira wa,yanda suka maidashi ciki,
Fita sukayi daga wajen fadar maimartaba Sarki Sudan
Suna ta kus,kus ta yadda zasuyi su kawo Joseph gurin sarki,
Shi Mr Ema dakanshi, ya kira Joseph da wayar shi, kira daya ana biyu ya dauka,
Joseph come nd meet me in mai Sudan palace now,now
Yusuf wanda ke tare dasu KB suna wani estimate, din kaya,
Abin yabashi mamaki ya kalli su KB yace masu cikin bacin rai wai Dad dina ne fadar mai sudan,
Duk kan su cikin mamaki, sukace gurin mai Sudan fa,?
Sun so su bi shi sutafi tare amma yusuf din yace su bari kawai zai iya zuwa,
Mr, Ema tare dasu Ekewa, da su Barnabas Mr Ema wanda ke zaune cikin damuwa ya saye da wani rigar yadi mai hoton giwa, dajan colur, sai wani jar hula dayasa akan shi,
Yana rike da sanda a hannun shi,,maikama da kan gunki
Kallo guda zakai ai kane cewa yau rayuwar shi ba tada dadi sam,
Su na ganin shi sukayo kanshi caaa kamar zasu ciye shi danye acikin yare suke magana suna cemai, ya taimaki rayuwar shi kada ya bari wasu su rude shi,
Kowa daga cikin su da abinda yake fadi, don dai kawai ya amsa cewa bai musulunta ba,