← Book details Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 105 OF 171

Sashe 105

Furen Juji Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Wanan wayar da sukayi yakawo karshen nauyi da kunyar da kowan su ke faman dako a cikin zuciyar shi,
Da sannu suka dan fara sakewa da junar su kamar yadda suke a da, indan yai waya da kowan su, zai gaisai,
Wanan shigowar ba karamin shigowa yusuf yayi ba don yashigo da shirin auren Naimat,
Sosai jama,a ke murna da zuwan shi saboda irin yadda mutane ke a cikin matsuwa,
Baida wani hutu atare da shi kasan cewar shine uban amarya da ango gaba daya,
Gida na musan man ya sai masu inda ya mallakawa Ibrahim shi a kyata,
Anty Dije ita ce uwar amarya don itace komai na amarya,
Sosai take gyaran amarya irin gyaran mutanen kasar kwantagora na asali bawai na zamani ba,
Don ita da kanta tasa a samo mata ganye don yin hadin da kanta,
Kamar yadda ko wace amarya yar asali take zama yayin zaman lalai haka itama Naimat ta koma inda tasha wankan lalai da turare sai sheki takeyi,
Su maryam da safiya da wata sister din mijin anty sune a matsayin abokan amarya,,
Sai zirga zirga sukeyi akan duk wani abin da ya dace suyi,
Shigar wasu shadda maryam tayi masu ruwan pink colour,
Sai wani farin lece da akai mai ado dashi kamar flower,
Farin gyale ne tadan yafa a kan,ta da takalmi farare masu dan tsini a baya,
Daga gurin sayen kayan da zasu rabawa friends din su da suka gaiyata suke tare da safiya amma safiya tadan tsaya sayen wasu kayan
A gajiye ta shigo falon hankalin ta a kwance tana mai cewa wassshhh wallahi anty nagaji ga mai manshin din da na hau yana ta tsula gudu da,,,,,
Makalewa maganar tai mata don ganin Yusuf wanda ke zaune,a falon su biyu zaune shi da Anty Dije
Sam bata tsan manci ganin shi ba a folon don motar shi bata gurin balle tagane cewa yana cikin gidan
Daganin ya na yin zaman su ,kasan cewa magana sukeyi mai muhinman ci ,
A tsakanin su don Naimat ma bata gurin alokacin,
Tun bayan wancan rikicin, sai yau sukayi ido biyu da junar su shi, da ita,
Kamar ta juya baya ta koma amma sai ta daure, kawai tasa kai ta shiga,
A sanyaye ta yi sallama ta shigo falon idanun ta sunyi, wani lub da su saboda kwaliyar da tayi,
Fuskanta babu yabo babu fallasa, ta,gaishe su a cikin girmamawa,
Yusuf ne ke cewa daga ina take haka take cewa ana gudu da ita a mashin,
Maryam ba kyaji ko ?
Har yanzu baki bar hawan mashin ba ko a dinga wulwulaku a titi,
Yakarasa zancen shi a cikin nuna bacin rai
Juyawa yayi inda anty take yana mai facing din ta ya ce,
Anty ku koyi tukin mota mana pls a , aje maku mota a gida yafi hakan ?
Dariya ma maganar shi ya ba Anty a lokacin irin yadda ya hakikance yana faman fada,
To Yusuf in banda abinka abinda mutum bai,dashi ai sai ya yi hakkuri,
Maryam na jin yadda yake ta faman sababi sai kawai ta juya, zuwa dakin su,
Duk sauran zancen da sukeyi a kai maryam wace ke ta ciki tana jin su duk ranta abace,
Don dai ko A,A wanda zai aure ta ai ba zai zake yana mata irin wanan masifan ba,
Shigowar safiya a dakin ita agajiye yasa ta dan sakewa ta daina kumburin da takeyi,
Sosai suka baje kayan da suka sayo don na su irin sha,anin suna dibawa, gaba dayan su har anty,
Muryan Anty ce maryam taji tana kiran ta bayan sun gama kallon kayan da arranging din komai,
Da sauri maryam din tace naam Anty,
Bata kara cewa komai ba sai kuma tai shiru tana mai kurawa kaunar naya ido,
Kamar mai tunanen wani abu can sai tace, wa maryam din,
May yasa dazun Yusuf yana maki fadan hawa mashin kika wuce ki ka barshi batare da kin tsaya ba,
Wani irin tsoro ne ya lullube maryam din don jin an anbaci sunan Yusuf wai kuma tai mashi laifi,
A hankali maryam ta janye hannunta asaman wani kwalin sweet da tadora akai,
Kanta ta dukar kasa tana dan wasa da yatsun ta a saman ties,
Karo na biyu takara kiran su nan ta tace, kina jina kuwa,
Maryam sam bana son ki nunawa Yusuf wani mugun tsana wanda har zai zaci ko kyamar,shi kike ji kamar yadda yake zato,
Dan juyawa Anty ta yi inda Safiya take tana mai,cewa don Allah dai safiya idan mutum,
Ya nuna cewa ya damu da kai a matsayin dan uwa ko kuma wani nashi can,?
May ya kamata kai kayi mashi a lokacin,
Safiya tace kai ma kabashi kulawa mana fiye da yadda ya nuna ma,
Masha Allah, inji Anty amma ita kinga sam bata gane hakan ba a rayuwar ta,
Kin gani yadda ki kayi dazun sam wallahi bai yi daidai ba
Hakan zai iya fusata shi yadauki zancen da baba yayi akan ku bilhakki da gaskiya,
Kin ko san cewa baba zai iya yin komai ba tare da amincewar ki ba,
Tagumi maryam tayi tana sauraron Antyn nata acikin natsuwa,
Inda Anty da safiya sukaci gaba da kawo mata musalai kala,kala akan zama da mutane
A sake murya a raunane tace yanzu yaya zanyi anty in kaucewa gudun magana,
?
Abinda anty ke son ji ke nan dama sai tadan gyara zaman ta tace,
Ki nuna mai cewa ke yanzu baki da dan uwan da ya wuce shi,
Shawaran ki, ki dinga sanar da shi don jin ra,ayin shi
Kissa dai irin ta mata zaki dinga gwada mai tankar ba komai a tare da zuciyar ki,
Kinga koda baba zai kara waiwayan zance shi Yusuf din da kanshi zai nuna wa baba rashin dacewar hakan a tsakanin ku,
Cikin sauri maryam ta daga kai takalli anty dije tace,
Amma anty baki ganin idan baba yaga haka zai zaci cewa ko na yarda ne,
Murmushi anty dije takarayi tace, ai shi Yusuf din sam bazai yarda har hakan yafaru ba,
Ke wayo fa za muimasu shi da baba din , ke dai iyaka kiyi kokarin nuna mai cewa ba komai na jin kyama a tsakanin ku,
A sanyaye maryam tai ajiyan zuciya tace nagode anty,
Wallahi har naji wani sanyi a zuciya ta
Anan sukaci gaba da hiran duniya saiko ga Naimat wace ta shiga family house din su mijin Anty ta shigo gida,
Duk hiran da sukeyi ita maryam hankalinta na can tana tunanen yadda zata fara bullowa Yusuf din,,,
Chapter 105 · 0% Book details