Sashe 72
Bakin Haure Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ya jikin nata?" Kallon kayan jikinshi yayi kafin ya ce mata. "Da sauki." "Kace anan kake zaune?" "Eh!" "Ayya to dama ina babu wanda ya mutu?" Banza ya bawa ajiyarta, ya cigaba da tafiya. "Kai kurma ne ina magana kayi banza dani." Uffan bai ce ba. " Yau ga lalacewar duniya, kai yanzu ina magana kayi banza dani don kaga na tako inda kake? Yanzu don."
"Me kika ce ne?" Ya juya yana me tambayarta da sigar renin hankali. "Uwarka Sa'adatu da ta haifi ɗan karuwi." Murmushi yayi tare da cigaba da tafiya, tana kuwa bin shi, tana zagin shi. Sai kallonsu ake shi kuwa ko a jikinshi. Yana isa kofar office din shi ya ce mata. "Idan kin gama jarabararki, na gode sai ko wuce gida domin na fito na same ki wallahi ni kaɗai nasan me zan dirka miki a asibitin nan." Ware idanu tayi tana faɗin "yanzu don baka da imani sai kayi min wani abu? Tambayarka nake sai kayi min wani abu!"
Hango wata nurse yayi ya ce mata. "Ki kawo min babban sirinjin allura tare da maganin nan, yanzu." "Ke dan uwarki kika kawo wani abu, sai na saka an kore ki a asibitin nan, kafira me kama da fatalwa. Kai kuma zamu gamu da juna, mara mutunci dan banza me kama da gwaggon biri "
Murmushi yayi ya rufe kofar shi, domin yasan Nana da dan banza tsoro, kuma bai zama dole ta kuma dawowa ba, murmushi yayi shi kaɗai, har ya gama sauya kaya. Ya fito dakin Hajiya, ya samu ta farka sai kuka Anisah take Nana sai surutu take ta musu da sababi. Safar hannu ya saka tare da haɗa kayan aikin ya cire ruwan daya kusan karewa, ya saka wani sannan ya zuba mata allura a ciki. Yana kallon yadda take kallonshi kamar irin ta farka daga cutar makanta, ya sani tana mamakin yadda aka yi babu abin da ya same shi. Sai da ya gama sannan ya dawo gabanta ya riko hannunta, ya saka a fuskarshi."Hajiyana nine Majid Mamman Ba'are gani nan lafiyana lau, ki kwantar da hankalinki." Murmushi me had'e da hawaye ta sake tana kallonshi har barci yayi nasarar gaba da ita. "Nana muje na kai ki gida kinji." Kallonshi tayi a kaikaice irin zata kafta mishi rashin mutunci. Yadda ya saka fuskar sojojin tuni hankalinta ya dawo jikinta, "hmmm muje!" Ta ce tana shirin mita. "Nisah kema idan ba da motarki kika zo ba, zo muje na ajiye ki kada na kuma ganinki tunda kuka zaki na mana asibitin. "
"Don Allah kayi hakuri ba zan kuma, na daina kukan." Ta fada tana k'amk'ame jikinta alamar ba zata fito ba, "ok muje ki ga jikin Aryan da Amaan." Mikewa tayi suka fita, har dakin a lokacin Aryan yana Sallah, yana idar da sallah. "Hamma Aryan?" Ajiyar zuciya ya sauke. "Ya jikinka?" Ta fada tana kuka, "Ya isa Auta, ba gashi naji sauki ba. Bar kuka ina fatan babu abinda ya same miki ko?" Girgixa mishi kai tayi tana share hawayen da yake zuba mata. "Bari na kai matar nan gida " "kaga matar nan a kofar dakinka, ni ba matar nan ba ce." Ta fada tana wani dauke kai, ita fa gara mata ma Majid da wannan me kalar zabiyar haushi yaƙe bata, balla mishi harara tayi. "Don kana gadara da Alhaji yana tsaye sai ka kashe min jikoki, dan banza me kama da mutanen boye." "Muje!" Majid ya faɗa mata, domin ya lura jaraba take nima. "Aikin banza kishiya da shashasha, da ka kafe ni da idanun kamar na mayu kurwana kur, idan ma ka kirkiro hatsarin ne don su mutu kaci kasonsu kayi karya, ina sane daku munafunkin banza munafikin wofi." Maganar Nana tayiwa Aryan tsauri amma kuma sai yayi murmushi ya ce mata. "Ai ke zan fara turawa lahira, domin na gaji wannan gwal din wuyarki." Wani dafe kirji tayi, tana nuna shi tare da kallon Majid. "Kaji ba, yana shirye shiryen turani lahira bayan ban ga matarka ba, dan bakin ciki wannan sarkan na matar Alhaji ne ko mutuwa nayi bata cikin gadona."
"Ai kuwa ki saka idanu sai kin garzaya barzahu bari a sallame ni, domin zan fara aikatar da aikina ne akanki."
"Wallahi baka isa ba, sai kotu da yan sanda sun shiga tsakaninmu, na rantse da Allah ba zan yarda ba, ko tuntube nayi Alhaji kai zaka nimo min lauya domin Ariyan ya shirya kisan kai, ya ga baya tow na rantse da Allah sai nayi fatalwa ko na mutu na kwaci hakkina."
"La fatalwa ma zaki zama?" "Kwarai don ba barin hakkin jinina zan yi ba." Ta fada tana hura hanci kamar ta doka mishi sandan hannunta. "Tsuhuwa lokacinki yayi, sai a fara shiri kafin na zo." "Alhaji kana jin shi ko." "Muje ki daina biye mishi, cinnaka Aryan ba zai kashe ba, balle dan mutum nayi mishi wannan shaidar tun daga duniya har lahira ba zai kashe wani ba."
"Au hatsarin da ya ja musu fa?"
"Muje a hankali zaki fahimci abin da yake faruwa." Haka ya fita da ita, " Nabeeha wai zan iya kashe ..." Hannu ta saka mishi a baki, "Tsakanin harshe da hakori ana samun sab'ani, haka tsakanin mutum da mutum ana samu, Aryan ban kowa a duniyarka ba, sai adalcinka har abada ba zaka b'ata hannunka da jinin kowa ba in sha Allah."
Ta fada tana kuka, tana son Mijinta kuma bata ji a ranta zata zarge shi ba. "Idan Hamma!" "Hamma Aryan, itama Nana gurbata mata tunani ake da zancen banza, muji da halin da Amaan da Jamilah suke ciki."
Shiru dakin ya dauka, babu wanda ya kuma magana, sannan Mijin Jamilah da dangin shi suna asibitin, hatsarinsu yasa videon Amaan ya mutu, sai aka koma labarin hatsarin domin abin ya faru ne da safen jiya, kuma kowa ya ga yadda abubuwan suka faru, sai aka shiga yayyata videon hatsarin da yadda abin ya faru, sama da labarin Hajiya da Amaan. Wannan al'amarin ya faru cikin kwana ɗaya, sai ya zama kome ya tafi kamar bai faru ba, don haka Majid shima yayi amfani da nashi kwarewar yasa aka binciko mishi wanda ya sake videon Amaan. Ai kuwa gayen yaci uban dokar sojoji.
* Tunda Majid ya bar Tani a ɗakinta har gari ya waye bata fito ba, koda Hajiya Fauziya tazo gidan a daki ta same ta, don ta kawo mata tsegumi ganin halin da take ciki yasa, bata iya bata labarin ba. Domin ta same ta ta birkita dakin tana niman abu.
"Tani lafiya?"
"Lafiyan kenan wayata nake nima." Kallonta Hajiya Fauziya tayi baki sake ta ce mata. "Ban gane wyaarki ba, wanene a gefen gadonki?" Juyawa tayi ta ganshi ta ce mata. "Ikon Allah, ban san yana wurin ba." Ta dauka da sauri har yana kokarin faɗuwa a hannunta, ta shiga kiran Sajjid..
"Dauka mana."
Katse kiran aka yi ta kuma kiranshi, sai da tayi bugu uku sannan aka ɗauka a make ya ce mata. "Dalla me zan miki?" "Idan kana cikin Niamey tow ka gaggauta barin garin nan, Majid na gaya maka Majid. Wallahi kafin wayewar gari nayi kashi ya kai sau goma maza ka bar garin nan ka kashe wayarka kada ka kunna sai nan da wata uku na gaya maka kada ka dawo Nijar "
"Babu inda zanje, ina garin nan wallahi."
"Na gaya maka kamar kare zai kashe ka, domin ko ya kashe ka babu abinda zai faru, ya fika gata ya fika kome ka kyale kome ka bar garin nan daga baya zamu yi magana don Allah." Ta fada a raunane, "Ni dai ban ji dadi ba, kawai zan tafi ne ba don ina da ra'ayi ba."
"Jeka don Allah da kuma ni." Kit ya kashe wayar yana mita. Itama zama tayi dabas da malmalan duwawunta tayi da kasa, a hankali ta sauke ajiyar zuciya me nauyi domin sai yanzu taji abu ya wuce mata, d'ago kai tayi a matuƙar gajiye ta kalli Hajiya Fauziya.
"Uwar me kika zo yi?"
"Hmmm! Hmm dama na gaya miki Aryan ya farfaɗo sannan an kama kama mutanen da suka yi ta."
"Je ki don Allah domin kin zama tauraruwa mai wutsiya, ganinki babu alkhairi domin nasan sharri ke tafe dake, don haka tafi wanda nake ciki ma ya ishe ni wallahi."
"Hmmm daga abin arziki, amma tunda bakya son na gaya miki shi kenan." Ta juya tana jin haushi kamar zata rufe Hajiya Tani da duka, don tazo da mugun labarin cewa an kama yaron da suka saka aiki. Don ba iya Sajjid yake mocking Amaan da yan uwanshi ba, har da taimakonsu....... *Kuyi hakuri babu yawa*
*₦300*
08130269641
#Mai_Dambu ce....
[4/17, 8:10 PM] Cutie cutie pie: *BAƘIN HAURE....🐾🐾*
"Me kika ce ne?" Ya juya yana me tambayarta da sigar renin hankali. "Uwarka Sa'adatu da ta haifi ɗan karuwi." Murmushi yayi tare da cigaba da tafiya, tana kuwa bin shi, tana zagin shi. Sai kallonsu ake shi kuwa ko a jikinshi. Yana isa kofar office din shi ya ce mata. "Idan kin gama jarabararki, na gode sai ko wuce gida domin na fito na same ki wallahi ni kaɗai nasan me zan dirka miki a asibitin nan." Ware idanu tayi tana faɗin "yanzu don baka da imani sai kayi min wani abu? Tambayarka nake sai kayi min wani abu!"
Hango wata nurse yayi ya ce mata. "Ki kawo min babban sirinjin allura tare da maganin nan, yanzu." "Ke dan uwarki kika kawo wani abu, sai na saka an kore ki a asibitin nan, kafira me kama da fatalwa. Kai kuma zamu gamu da juna, mara mutunci dan banza me kama da gwaggon biri "
Murmushi yayi ya rufe kofar shi, domin yasan Nana da dan banza tsoro, kuma bai zama dole ta kuma dawowa ba, murmushi yayi shi kaɗai, har ya gama sauya kaya. Ya fito dakin Hajiya, ya samu ta farka sai kuka Anisah take Nana sai surutu take ta musu da sababi. Safar hannu ya saka tare da haɗa kayan aikin ya cire ruwan daya kusan karewa, ya saka wani sannan ya zuba mata allura a ciki. Yana kallon yadda take kallonshi kamar irin ta farka daga cutar makanta, ya sani tana mamakin yadda aka yi babu abin da ya same shi. Sai da ya gama sannan ya dawo gabanta ya riko hannunta, ya saka a fuskarshi."Hajiyana nine Majid Mamman Ba'are gani nan lafiyana lau, ki kwantar da hankalinki." Murmushi me had'e da hawaye ta sake tana kallonshi har barci yayi nasarar gaba da ita. "Nana muje na kai ki gida kinji." Kallonshi tayi a kaikaice irin zata kafta mishi rashin mutunci. Yadda ya saka fuskar sojojin tuni hankalinta ya dawo jikinta, "hmmm muje!" Ta ce tana shirin mita. "Nisah kema idan ba da motarki kika zo ba, zo muje na ajiye ki kada na kuma ganinki tunda kuka zaki na mana asibitin. "
"Don Allah kayi hakuri ba zan kuma, na daina kukan." Ta fada tana k'amk'ame jikinta alamar ba zata fito ba, "ok muje ki ga jikin Aryan da Amaan." Mikewa tayi suka fita, har dakin a lokacin Aryan yana Sallah, yana idar da sallah. "Hamma Aryan?" Ajiyar zuciya ya sauke. "Ya jikinka?" Ta fada tana kuka, "Ya isa Auta, ba gashi naji sauki ba. Bar kuka ina fatan babu abinda ya same miki ko?" Girgixa mishi kai tayi tana share hawayen da yake zuba mata. "Bari na kai matar nan gida " "kaga matar nan a kofar dakinka, ni ba matar nan ba ce." Ta fada tana wani dauke kai, ita fa gara mata ma Majid da wannan me kalar zabiyar haushi yaƙe bata, balla mishi harara tayi. "Don kana gadara da Alhaji yana tsaye sai ka kashe min jikoki, dan banza me kama da mutanen boye." "Muje!" Majid ya faɗa mata, domin ya lura jaraba take nima. "Aikin banza kishiya da shashasha, da ka kafe ni da idanun kamar na mayu kurwana kur, idan ma ka kirkiro hatsarin ne don su mutu kaci kasonsu kayi karya, ina sane daku munafunkin banza munafikin wofi." Maganar Nana tayiwa Aryan tsauri amma kuma sai yayi murmushi ya ce mata. "Ai ke zan fara turawa lahira, domin na gaji wannan gwal din wuyarki." Wani dafe kirji tayi, tana nuna shi tare da kallon Majid. "Kaji ba, yana shirye shiryen turani lahira bayan ban ga matarka ba, dan bakin ciki wannan sarkan na matar Alhaji ne ko mutuwa nayi bata cikin gadona."
"Ai kuwa ki saka idanu sai kin garzaya barzahu bari a sallame ni, domin zan fara aikatar da aikina ne akanki."
"Wallahi baka isa ba, sai kotu da yan sanda sun shiga tsakaninmu, na rantse da Allah ba zan yarda ba, ko tuntube nayi Alhaji kai zaka nimo min lauya domin Ariyan ya shirya kisan kai, ya ga baya tow na rantse da Allah sai nayi fatalwa ko na mutu na kwaci hakkina."
"La fatalwa ma zaki zama?" "Kwarai don ba barin hakkin jinina zan yi ba." Ta fada tana hura hanci kamar ta doka mishi sandan hannunta. "Tsuhuwa lokacinki yayi, sai a fara shiri kafin na zo." "Alhaji kana jin shi ko." "Muje ki daina biye mishi, cinnaka Aryan ba zai kashe ba, balle dan mutum nayi mishi wannan shaidar tun daga duniya har lahira ba zai kashe wani ba."
"Au hatsarin da ya ja musu fa?"
"Muje a hankali zaki fahimci abin da yake faruwa." Haka ya fita da ita, " Nabeeha wai zan iya kashe ..." Hannu ta saka mishi a baki, "Tsakanin harshe da hakori ana samun sab'ani, haka tsakanin mutum da mutum ana samu, Aryan ban kowa a duniyarka ba, sai adalcinka har abada ba zaka b'ata hannunka da jinin kowa ba in sha Allah."
Ta fada tana kuka, tana son Mijinta kuma bata ji a ranta zata zarge shi ba. "Idan Hamma!" "Hamma Aryan, itama Nana gurbata mata tunani ake da zancen banza, muji da halin da Amaan da Jamilah suke ciki."
Shiru dakin ya dauka, babu wanda ya kuma magana, sannan Mijin Jamilah da dangin shi suna asibitin, hatsarinsu yasa videon Amaan ya mutu, sai aka koma labarin hatsarin domin abin ya faru ne da safen jiya, kuma kowa ya ga yadda abubuwan suka faru, sai aka shiga yayyata videon hatsarin da yadda abin ya faru, sama da labarin Hajiya da Amaan. Wannan al'amarin ya faru cikin kwana ɗaya, sai ya zama kome ya tafi kamar bai faru ba, don haka Majid shima yayi amfani da nashi kwarewar yasa aka binciko mishi wanda ya sake videon Amaan. Ai kuwa gayen yaci uban dokar sojoji.
* Tunda Majid ya bar Tani a ɗakinta har gari ya waye bata fito ba, koda Hajiya Fauziya tazo gidan a daki ta same ta, don ta kawo mata tsegumi ganin halin da take ciki yasa, bata iya bata labarin ba. Domin ta same ta ta birkita dakin tana niman abu.
"Tani lafiya?"
"Lafiyan kenan wayata nake nima." Kallonta Hajiya Fauziya tayi baki sake ta ce mata. "Ban gane wyaarki ba, wanene a gefen gadonki?" Juyawa tayi ta ganshi ta ce mata. "Ikon Allah, ban san yana wurin ba." Ta dauka da sauri har yana kokarin faɗuwa a hannunta, ta shiga kiran Sajjid..
"Dauka mana."
Katse kiran aka yi ta kuma kiranshi, sai da tayi bugu uku sannan aka ɗauka a make ya ce mata. "Dalla me zan miki?" "Idan kana cikin Niamey tow ka gaggauta barin garin nan, Majid na gaya maka Majid. Wallahi kafin wayewar gari nayi kashi ya kai sau goma maza ka bar garin nan ka kashe wayarka kada ka kunna sai nan da wata uku na gaya maka kada ka dawo Nijar "
"Babu inda zanje, ina garin nan wallahi."
"Na gaya maka kamar kare zai kashe ka, domin ko ya kashe ka babu abinda zai faru, ya fika gata ya fika kome ka kyale kome ka bar garin nan daga baya zamu yi magana don Allah." Ta fada a raunane, "Ni dai ban ji dadi ba, kawai zan tafi ne ba don ina da ra'ayi ba."
"Jeka don Allah da kuma ni." Kit ya kashe wayar yana mita. Itama zama tayi dabas da malmalan duwawunta tayi da kasa, a hankali ta sauke ajiyar zuciya me nauyi domin sai yanzu taji abu ya wuce mata, d'ago kai tayi a matuƙar gajiye ta kalli Hajiya Fauziya.
"Uwar me kika zo yi?"
"Hmmm! Hmm dama na gaya miki Aryan ya farfaɗo sannan an kama kama mutanen da suka yi ta."
"Je ki don Allah domin kin zama tauraruwa mai wutsiya, ganinki babu alkhairi domin nasan sharri ke tafe dake, don haka tafi wanda nake ciki ma ya ishe ni wallahi."
"Hmmm daga abin arziki, amma tunda bakya son na gaya miki shi kenan." Ta juya tana jin haushi kamar zata rufe Hajiya Tani da duka, don tazo da mugun labarin cewa an kama yaron da suka saka aiki. Don ba iya Sajjid yake mocking Amaan da yan uwanshi ba, har da taimakonsu....... *Kuyi hakuri babu yawa*
*₦300*
08130269641
#Mai_Dambu ce....
[4/17, 8:10 PM] Cutie cutie pie: *BAƘIN HAURE....🐾🐾*