Sashe 71
Bakin Haure Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
{Greed for Money is the roots of all evils🫀}
Arewabooks:maidambu41
Wattpad:Mai_Dambu
Mallakar:Mai_Dambu
*Alhamdulillahi na gode sosai, marubuta da makaranta Allah ya saka da alkhairi, musamman yan grp din Fitilar hikayar Dambuje, Allah ya bada lada naga kira da sakonnin ku. Allah ya karo dubun zumunci, Ubangiji ya jikan dukkan yan uwa musulmai da suke faɗin duniya, tare da iyayenmu bakiɗaya... Allahumma Amin*
035
_Yau kan babu editing 🥰_
Nad'e hannunshi yayi a kirji, yana kallonta yadda take gurfane a gabanshi. "Ba xance kada ki hana shi ba, amma tabbas nayi ido biyu da shi, sai dai Uwarshi ta kara haifar wani koda yake ina zao ganta. Amma ki saka idanu akan shi domin." Sake hannunshi yayi ya nufi kofar fita yana faɗin. "Duk yadda kika so, kiyi amma inuwar Ba'are da al'ummar gidan kada na kuma ganinku." Daga haka ya bar mata dakin da gidan bakidaya. Wani irin zufa ke karyo mata, yana fita da gudu ta mike ta ɗauki goran ruwan da yake gefen gadonta, sai da ta shanye goran bakiɗaya, sannan ta ajiye. Zirga zirga ta fara a cikin dakin tana jin kamar tayi ta kurma ihu, Hajiya Sa'a ta gaya mata magana akan haka, yanzu ma Majid ya kara gaya mata, haka yaná nufin sun san kome akanta, ita ce dai bata san kome akansu ba, wanda ta sani ma na bogi ne domin sune suka san wacece ita.
Hannu ta saka a kai, kafin ta koma ta zauna tana jin kamar ta tattara yan abin da take da shi ta gudu, domin zuwa yanzu da Majid yasan Sajjid ba dan Mamman ba'are ba ne, zai fi mata kyau tayi ta gudun hijira. Ai na Majid wasa ne akan na Sajjid don binne ta zai yi da ranta, matukar yaji wani labari mara daɗi akan waye shi, cikinta ne yayi wani irin murdewa a daddafe ta shiga toilet. Bata san ya aka yi ba, sai g kashi shaaaa cikinta ya tsinke. Wato Majid bala'i ne, idan ta sake wani abu ya kara had'a su. Binne kanta zata yi da ranta kafin Majid ya zo gare ta, don na Majid me sauki.
Koda ta fito daga ban dakin, a daddafe ta nime wuri ta zauna. Can cikin ya kuma murdeta, da sauri ta shiga banɗakin ta zauna akan wurin kashin.
A lokacin da ya bar gidan Tani, a hankali yake jin wani irin abu yana yawo a kanshi, har wani nutsuwa yake ji, Hajiya Tani ba ita daya ba ce akwai wasu a bayanta. Bari ya ga iya gudun Tani domin idan akwai wani a bayanta dole zai fito, don haka ya tab'a spot point. Lokacin da ya isa asibitin Hajiya tana barci, zama yayi na wani lokaci kafin ya mike ya nufi Office ɗinshi, bude drowe office din yayi ya ciro abin sallah da jallabiya, murmushi yayi domin yasan aikin Jami'ah da Aryan ne, sune zasu nishi haka.
Ban daki ya shiga yayi alola, ya fito ya shimfida abin sallah, tun ya fara sallah nan karfe uku bai tsaya ba sai da Masallacin asibitin aka kusan shiga sallah, ya sallame ya nufi masallaci. Bayan an idar da sallah ya zauna yana addu'a, sai da rana ta fito sannan ya wuce asibitin. Anan ya samu Anisah da Salamatu sun shigo. "Hammayo!" Ta kira sunanshi, bude mata gefen hannunshi yayi ta isa wurin tana kuka kamar ranta zai fita. "Hamma kayi hakuri." "Shiiii!" "Duk laifina ne, da na fada maka haka da bai faru ba." "Ya isa haka, kin yi barci kuwa?" Ya tambaye ta cikin kulawa, "Nayi su'ad ya saka ni nayi barci." Murmushi yayi ya ce mata. "Good girl, muje ki bani abinci naci don naga basket a hannun Mama Salamatu." Ya faɗi haka don ya kwantar mata da hankali. Har dakin da Hajiya take suka shiga, "ina zuwa ko" ya faɗa yana nufar dakinsu Aryan a can ya samu Matarshi tana ta kuka. "Ya isa haka, ya farka fa bari na duba shi." Ya faɗa yana shiga dakin,duba shi yayi yaga lafiya lau barci yake, bai tashe shi ba ya nufi wurin Amaan, ya shafa kanshi tausayin shi ya masifar cika mishi zuciya, duk da rashin jituwa da yake tsakaninsu, haka bai tab'a damunshi ba, domin yasan wata rana zai gane gaskiya, duba karin wurin yayi yana me saka mishi wani ruwan. Sannan ya wuce kan Aryan da yake ta motsi. A hankali ya isa kanshi, ya cigaba da dube-dube har ya farka. "Welcome back Mr Mamman Ba'are." "Anisah fa?" Tab'e baki Majid yayi, sannan ya ce mishi."Na zata matarka da Yaranka zaka tambaya." "Wani hali kanwata take ciki?" "Ina zan sani tunda ina tsaye akanku." "Hamma kasan bala'in da na gani jiya." "Ina zan sani ragon maza." Ya faɗa yana murmushi, d'ago shi yayi ya zauna. "Hamma!" "Guduma!" Ya faɗa yana murmushi, don ya gaji da maganar Aryan. "Hamma Abdul Majid."
"Anisah tana lafiya, wurin Hajiya matarka tana waje bari ta shigo." Ajiyar zuciya ya sauke, "Manyan mota biyu suka tasamu a gaba, Hamma dole na firgita." "Allah ya kiyayye na gaba." Ya faɗa yana ƙara duba shi. "Ina ke maka ciwo yanzu?" Ya tambaye. "Hakarkarina ke ciwo." Matsawa yayi ya d'aga mishi hannunshi, da sauri ya riko hannun Majid, "Hamma bari kawai." Sake hannun yayi yana dauki wani littafi yayi rubutu, sannan ya ce mishi. "Motar ya doke ku ne?" "Tsakiyarsu suka saka mu, wallahi ban san yadda aka yi aka ciro mu a ciki ba."
"Anjima zaa zo a kaika x-ray, mu ga wurin " inji Majid, juyawa Aryan yayi yana kallon Amaan, "bai farka ba ko?" Ya tambaye shi idanunshi cike da kwalla. "Ba shi ne matsalata ba, Jamilah tana da ciki, kuma har yanzu bata farka ba." Shiru ne ya gifta a dakin, dukkansu babu me kuzarin magana, fita yayi ya nufi ICU, inda aka kwantar da Jamilah. Yana shiga yaga yadda kome yake tafiya a cikin na'urar da aka saka mata, amma ya kasa tabuka kome dake ya samu wasu drs akanta, sai ya zama kamar dan kallo, haka ya juyo daga dakin ya gagara yin kome, a bakin kofar ya samu Mijinta, dasu Nanah.
Arewabooks:maidambu41
Wattpad:Mai_Dambu
Mallakar:Mai_Dambu
*Alhamdulillahi na gode sosai, marubuta da makaranta Allah ya saka da alkhairi, musamman yan grp din Fitilar hikayar Dambuje, Allah ya bada lada naga kira da sakonnin ku. Allah ya karo dubun zumunci, Ubangiji ya jikan dukkan yan uwa musulmai da suke faɗin duniya, tare da iyayenmu bakiɗaya... Allahumma Amin*
035
_Yau kan babu editing 🥰_
Nad'e hannunshi yayi a kirji, yana kallonta yadda take gurfane a gabanshi. "Ba xance kada ki hana shi ba, amma tabbas nayi ido biyu da shi, sai dai Uwarshi ta kara haifar wani koda yake ina zao ganta. Amma ki saka idanu akan shi domin." Sake hannunshi yayi ya nufi kofar fita yana faɗin. "Duk yadda kika so, kiyi amma inuwar Ba'are da al'ummar gidan kada na kuma ganinku." Daga haka ya bar mata dakin da gidan bakidaya. Wani irin zufa ke karyo mata, yana fita da gudu ta mike ta ɗauki goran ruwan da yake gefen gadonta, sai da ta shanye goran bakiɗaya, sannan ta ajiye. Zirga zirga ta fara a cikin dakin tana jin kamar tayi ta kurma ihu, Hajiya Sa'a ta gaya mata magana akan haka, yanzu ma Majid ya kara gaya mata, haka yaná nufin sun san kome akanta, ita ce dai bata san kome akansu ba, wanda ta sani ma na bogi ne domin sune suka san wacece ita.
Hannu ta saka a kai, kafin ta koma ta zauna tana jin kamar ta tattara yan abin da take da shi ta gudu, domin zuwa yanzu da Majid yasan Sajjid ba dan Mamman ba'are ba ne, zai fi mata kyau tayi ta gudun hijira. Ai na Majid wasa ne akan na Sajjid don binne ta zai yi da ranta, matukar yaji wani labari mara daɗi akan waye shi, cikinta ne yayi wani irin murdewa a daddafe ta shiga toilet. Bata san ya aka yi ba, sai g kashi shaaaa cikinta ya tsinke. Wato Majid bala'i ne, idan ta sake wani abu ya kara had'a su. Binne kanta zata yi da ranta kafin Majid ya zo gare ta, don na Majid me sauki.
Koda ta fito daga ban dakin, a daddafe ta nime wuri ta zauna. Can cikin ya kuma murdeta, da sauri ta shiga banɗakin ta zauna akan wurin kashin.
A lokacin da ya bar gidan Tani, a hankali yake jin wani irin abu yana yawo a kanshi, har wani nutsuwa yake ji, Hajiya Tani ba ita daya ba ce akwai wasu a bayanta. Bari ya ga iya gudun Tani domin idan akwai wani a bayanta dole zai fito, don haka ya tab'a spot point. Lokacin da ya isa asibitin Hajiya tana barci, zama yayi na wani lokaci kafin ya mike ya nufi Office ɗinshi, bude drowe office din yayi ya ciro abin sallah da jallabiya, murmushi yayi domin yasan aikin Jami'ah da Aryan ne, sune zasu nishi haka.
Ban daki ya shiga yayi alola, ya fito ya shimfida abin sallah, tun ya fara sallah nan karfe uku bai tsaya ba sai da Masallacin asibitin aka kusan shiga sallah, ya sallame ya nufi masallaci. Bayan an idar da sallah ya zauna yana addu'a, sai da rana ta fito sannan ya wuce asibitin. Anan ya samu Anisah da Salamatu sun shigo. "Hammayo!" Ta kira sunanshi, bude mata gefen hannunshi yayi ta isa wurin tana kuka kamar ranta zai fita. "Hamma kayi hakuri." "Shiiii!" "Duk laifina ne, da na fada maka haka da bai faru ba." "Ya isa haka, kin yi barci kuwa?" Ya tambaye ta cikin kulawa, "Nayi su'ad ya saka ni nayi barci." Murmushi yayi ya ce mata. "Good girl, muje ki bani abinci naci don naga basket a hannun Mama Salamatu." Ya faɗi haka don ya kwantar mata da hankali. Har dakin da Hajiya take suka shiga, "ina zuwa ko" ya faɗa yana nufar dakinsu Aryan a can ya samu Matarshi tana ta kuka. "Ya isa haka, ya farka fa bari na duba shi." Ya faɗa yana shiga dakin,duba shi yayi yaga lafiya lau barci yake, bai tashe shi ba ya nufi wurin Amaan, ya shafa kanshi tausayin shi ya masifar cika mishi zuciya, duk da rashin jituwa da yake tsakaninsu, haka bai tab'a damunshi ba, domin yasan wata rana zai gane gaskiya, duba karin wurin yayi yana me saka mishi wani ruwan. Sannan ya wuce kan Aryan da yake ta motsi. A hankali ya isa kanshi, ya cigaba da dube-dube har ya farka. "Welcome back Mr Mamman Ba'are." "Anisah fa?" Tab'e baki Majid yayi, sannan ya ce mishi."Na zata matarka da Yaranka zaka tambaya." "Wani hali kanwata take ciki?" "Ina zan sani tunda ina tsaye akanku." "Hamma kasan bala'in da na gani jiya." "Ina zan sani ragon maza." Ya faɗa yana murmushi, d'ago shi yayi ya zauna. "Hamma!" "Guduma!" Ya faɗa yana murmushi, don ya gaji da maganar Aryan. "Hamma Abdul Majid."
"Anisah tana lafiya, wurin Hajiya matarka tana waje bari ta shigo." Ajiyar zuciya ya sauke, "Manyan mota biyu suka tasamu a gaba, Hamma dole na firgita." "Allah ya kiyayye na gaba." Ya faɗa yana ƙara duba shi. "Ina ke maka ciwo yanzu?" Ya tambaye. "Hakarkarina ke ciwo." Matsawa yayi ya d'aga mishi hannunshi, da sauri ya riko hannun Majid, "Hamma bari kawai." Sake hannun yayi yana dauki wani littafi yayi rubutu, sannan ya ce mishi. "Motar ya doke ku ne?" "Tsakiyarsu suka saka mu, wallahi ban san yadda aka yi aka ciro mu a ciki ba."
"Anjima zaa zo a kaika x-ray, mu ga wurin " inji Majid, juyawa Aryan yayi yana kallon Amaan, "bai farka ba ko?" Ya tambaye shi idanunshi cike da kwalla. "Ba shi ne matsalata ba, Jamilah tana da ciki, kuma har yanzu bata farka ba." Shiru ne ya gifta a dakin, dukkansu babu me kuzarin magana, fita yayi ya nufi ICU, inda aka kwantar da Jamilah. Yana shiga yaga yadda kome yake tafiya a cikin na'urar da aka saka mata, amma ya kasa tabuka kome dake ya samu wasu drs akanta, sai ya zama kamar dan kallo, haka ya juyo daga dakin ya gagara yin kome, a bakin kofar ya samu Mijinta, dasu Nanah.