Sashe 19
Bakin Haure Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Murmushi tayi tana faɗin "taya ba zan kasance haka ba, ina tare da dai ga makiya sun rufa maka baya ta ko ina, ai lahu a gare ni na tsaya maka, don haka kada ka ji kome mijina."
***
Wurin karfe biyar na yamma Hajiya Sa'adatu tana kan abin sallah, tana lazimi Nabeeha matar Aryan ta shigo hannunta dauke da katon tire, bayan ta Aryan ne dauke da Kwando, "Assalamu alaikum Barka da maraice Hajajju." Sallamewa tayi tana kallonsu fuskarta dauke da murmushi ta ce musu. "Amin wa'alaikumus Salam, barkanku mutanen kirki." Gyara zama tayi tana faɗin. "Nawa ne ko na Hammanku?" Dariya sukayi. "Hajiya naki da nashi ne, muka ce bari a kawo mishi, duk da ban gaya mata da wuri ba." " Hajiya kinji ba yaki gaya min zai tawo da hamma kawai sai gashi nan yazo da zancen akwai bako." Nabeeha ta faɗa tana tura baki. "Baka kyauta ba, maza jeka dakinshi ka taso min shi."
"Tow Hajiya." Haka ya fita zuwa dakin Majid din da yake kwance, ya lullube kanshi da mayafi, dakin ya bada wani irin duhu. Kunna wutar dakin Aryan yayi, ya hango shi zaune ya jingina da allon gadon. Amma kanshi a lullube yake. "Baka da lafiya ne?" Janye lulluben yayi yana kallon Aryan. Dauke kai yayi yana me sake lullube kanshi. "Kazo falon Hajiya da yake sama Please."
"Me zan yi?" A yanayin rayuwarshi matukar ba'a wurin aiki ba,baka tab'a ganin fara'arshi, tashi yayi ya sauka daga gadon ya nufi ban daki. Sai da ya gama uzurinshi ya fito ya saka hula a kanshi ya fita. Zuwa falon hajiya domin sun fito daga ɗakinta, yana shiga ya same su a kan kafet sun baza abinci. "Matar Aryan ce ta maka abinci."
"Nagode sosai!" Ya fada yana gyara zamanshi a kafet ɗin, Aryan ya zuba mishi yana jan shi da hira. "Amma shirun da Hajiya Tani tayi babu magana a kasa?" "Allah yana sane kuma yafi mu sanin abinda yake zukatansu."
Inji Hajiya, tana cin abincin itama don ta lura Majid yaki cin ko loma daya ne, har yau yana shakkar cin abincin kowa, domin rufawa rayuwarshi asiri yasa ban da girkin Hajiya kai ko tea bai yadda ya ci wani abu daga wani wurin ba. Shi yasa a duniyarshi yake shakkar kaidin mace. Saboda kaf duniya babu wanda yasan cewa sanadin jinyar Mahaifinsu guba ce. A hankali ya tura abincin yana murmushi. "Bana son abincin da aka saka citta da tarfarnuwa, domin ina da allergy."
Sanin ba zai ci bane Aryan yayi maza y kare dan uwanshi. "Wayyo kayi hakuri, na manta na gayawa pretty baka cin citta da tarfarnuwa." Murmushi yayi ya mike, karshe abincin da bai ci ba kenan. Kuma ai Hajiya tasan ba zai ci ba. Ita tana ganin har yau Majid bai warke ba, pretend yake kamar mai lafiya amma a zahirin gaskiya bai da lafiya. Shi yasa take son yayi aure ko zai samu wacce zata jure matsalarshi,
"Kiyi hakuri haka yake, baya cin citta da tarfarnuwa ne, tun yana Yaro." Itama Hajiya ta fadi haka, shi kuwa gogan naku yana shiga dakin drower yaja ya Ciro kudi me yawan gaske, ya fito daga dakinshi kenan suka hadu da Amaan Mamman Ba'are,. Kallon kallo suka yiwa juna kafin kowa ya kame kanshi, akwai wannan rigimar na sako da sako, amma ita Hajiya bata taɓa kawowa al'amarin zai lalace har girman yaranta ba, a zahirin gaskiya tsanar da Amaan yakewa Majid tayi yawa da har sai da kowa yayi magana. Wani irin tsana ce irin na matukar na samu dama sai naga bayanka. Amma a bangaren Majid babu wannan tsanar kawai shi mutum ne da yasan ciwon kanshi da darajar kanshi,. Sannan bai kullaci Amaan har haka ba. Kamar yadda shi ya kullace shi, reni ne baya so kuma ya fahimci Amaan yana da reni da son abin duniya.
Kiyayyar tasu ta faro ne daga lokacin da Alhaji Mamman Ba'are, ya bar wasiyya akan cirewa kuri'arshi ya gadarwa Majid, sannan ko a halin jinya yadda Alhaji Mamman Ba'are yake ta rokon a nimo mishi Majid ya roke shi gafara kada ya mutu da hakkinshi ya kara tunzura dayawan mutanen dake jikinshi, bawan Allah nan har ya mutu da rokon a kira mishi Majid, don Allah ya yafe mishi.
Duk da akwai hakkin iyaye akan Yaransu, haka akwai hakkin Yara akan iyayensu, wannan al'amarin ya tab'a zuciyar kowa na jikin Mamman Ba'are musamman Hajiya Nana wacce idan taji yana cewa Majid ba zaka zo ba, Majid kana ina ne? Majid zan mutu ban ga fuskarka ba. Majid nasan na cuce ka, Majid kazo. Shi yasa bayan kome da ya warewa Majid, akwai wasu takardun da ya bawa abokinshi. Wanda babu wanda ya sani daga Hajiya sai Abokinshi Alhaji Abubakar Abzin, shima shahararren dan kasuwa ne da yake garin marad'i, kuma wani ikon Allah Alhaji Abubakar Abzin bai tab'a takowa zuwa Niamey ba, idan abubuwa suka shiga gaban Hajiya wurinshi take zuwa. Yanzu ma tunaninta kafin hutun Majid ya ƙare zata kai shi garin marad'i, su gana.
Wannan shine shirinta.
Sai da Majid ya jira Amaan ya shiga dakin, sannan shima ya shiga ya mikawa Hajiya kudin tare da mata magana da idanu, ta bawa Nabeeha. "Barka Hammayo." Inji Salaha matar Amaan, "Barka!" Ya fada a hankali, idan baka saka kunne ba, ba zaka ji me yace ba. Shigowar yara uku suna ihu, yasa shi juyawa. Sai wani guda daya da yake bakin kofar shiga falon Hajiya. "Appa kaga Shuraim ya dake mu ko?" Yaran suka nufi wurin Amaan, mikewa Amaan yayi tare da nufar Shuraim ɗin. Shima Aryan har zai mike Majid ya kalle shi, a fusace ya koma ya zauna yana kwafa. "Kai wato munafurcin da ka gada daga wurin wancan dan iskan Yaron shine zaka fara." Ya rike kunnen Yaron. Amadadin yaron ya fasa ihu, sai ga Amaan yana fasa ihu, babu wanda ya san me ya faru, sai yaron ne kawai ya san me ya faru. Daukarshi Majid yayi suka fita. "Daada taka mishi kafa kayi ko?" Ya rad'a mishi a kunne. "A'a" "Daada Allah yana kona me karya inji Ummina." Dakinshi ya shiga da shi, ya Ciro katon kwalin chocolate, ya mika mishi sannan ya kara dauko dayar ya ce mishi. "muje!" Haka ya riko hannunshi har falon Hajiya suka koma, zama yayi ya kira sauran Yaran, Yaran Amaan dake duk mata ne, tasowa suka yi duk da harara su da Amaan yake, haka suka tawo wurin Majid ya ajiye su a gefensu. Sannna ya mikawa yar karamar yar Aryan hannu da sauri ta taso. Ya ajiye ta" Kai Ayyan ka sammata a naka, Anum da Widad zan basu anan."
"A baco na Yaya!" Injin yarinyar. "Bushrah!" Babanta ya daka mata tsawa. D'ago kai Majid yayi ya watsa mishi harara. "Tow shi kenan tunda baki son na Yaya Anum a san mata?" Gyada kai tayi, ya bude musu kwalin ya ciro chocolate din ta ce mishi. "Dada a bacon na Anunu." Ta maida hannunta baya. Hajiya kuwa me zata yi ban da dariya ta ce mishi. " Ai yadda ka bawa sa'anta kwali itama haka zaka dauko mata kwali domin bata yarda a raba kansu da yan uwanta."
"Uwata taso muje." Ya dauki su Anum ya zaunar dasu a saman kujerar ya dauki Bushrah har dakinshi ya dauko mata nata, tun da ya bata, ta fara bashi labarin da Allah ya gani bai fahimci Yaren ba, har suka isa falon, bashi labarin take.
"Ja'ira mara kunya, dole ki bashi labari anya takwara haka zamu yi dake."
"Jiya babu luwana dake, ban baki cokulet dina ba " ta zauna ta yaga kwalin. Ya zube dukka. "Dada ashe min!" Wato ya kwashe mata, "abawa jiya." Ai kuwa Hajiya ta wafta ta ce. "Sai dai kada abawa gobe, amma jiya kan zan sha."
Haka aka yi ta hira har wani lokaci kafin lokacin magariba tayi duk suka tashi zuwa Masallaci..
*Sansanin gudun hijira*
#thedambuje
[2/16, 9:24 PM] Cutie cutie pie: *BAƘIN HAURE....🐾🐾*
{Greed for Money is the roots of all evils🫀}
Arewabooks:maidambu41
Wattpad:Mai_Dambu
Mallakar:Mai_Dambu
*010*
*Sansanin Yan gudun hijira*
Adamawan Kamaru.
***
Wurin karfe biyar na yamma Hajiya Sa'adatu tana kan abin sallah, tana lazimi Nabeeha matar Aryan ta shigo hannunta dauke da katon tire, bayan ta Aryan ne dauke da Kwando, "Assalamu alaikum Barka da maraice Hajajju." Sallamewa tayi tana kallonsu fuskarta dauke da murmushi ta ce musu. "Amin wa'alaikumus Salam, barkanku mutanen kirki." Gyara zama tayi tana faɗin. "Nawa ne ko na Hammanku?" Dariya sukayi. "Hajiya naki da nashi ne, muka ce bari a kawo mishi, duk da ban gaya mata da wuri ba." " Hajiya kinji ba yaki gaya min zai tawo da hamma kawai sai gashi nan yazo da zancen akwai bako." Nabeeha ta faɗa tana tura baki. "Baka kyauta ba, maza jeka dakinshi ka taso min shi."
"Tow Hajiya." Haka ya fita zuwa dakin Majid din da yake kwance, ya lullube kanshi da mayafi, dakin ya bada wani irin duhu. Kunna wutar dakin Aryan yayi, ya hango shi zaune ya jingina da allon gadon. Amma kanshi a lullube yake. "Baka da lafiya ne?" Janye lulluben yayi yana kallon Aryan. Dauke kai yayi yana me sake lullube kanshi. "Kazo falon Hajiya da yake sama Please."
"Me zan yi?" A yanayin rayuwarshi matukar ba'a wurin aiki ba,baka tab'a ganin fara'arshi, tashi yayi ya sauka daga gadon ya nufi ban daki. Sai da ya gama uzurinshi ya fito ya saka hula a kanshi ya fita. Zuwa falon hajiya domin sun fito daga ɗakinta, yana shiga ya same su a kan kafet sun baza abinci. "Matar Aryan ce ta maka abinci."
"Nagode sosai!" Ya fada yana gyara zamanshi a kafet ɗin, Aryan ya zuba mishi yana jan shi da hira. "Amma shirun da Hajiya Tani tayi babu magana a kasa?" "Allah yana sane kuma yafi mu sanin abinda yake zukatansu."
Inji Hajiya, tana cin abincin itama don ta lura Majid yaki cin ko loma daya ne, har yau yana shakkar cin abincin kowa, domin rufawa rayuwarshi asiri yasa ban da girkin Hajiya kai ko tea bai yadda ya ci wani abu daga wani wurin ba. Shi yasa a duniyarshi yake shakkar kaidin mace. Saboda kaf duniya babu wanda yasan cewa sanadin jinyar Mahaifinsu guba ce. A hankali ya tura abincin yana murmushi. "Bana son abincin da aka saka citta da tarfarnuwa, domin ina da allergy."
Sanin ba zai ci bane Aryan yayi maza y kare dan uwanshi. "Wayyo kayi hakuri, na manta na gayawa pretty baka cin citta da tarfarnuwa." Murmushi yayi ya mike, karshe abincin da bai ci ba kenan. Kuma ai Hajiya tasan ba zai ci ba. Ita tana ganin har yau Majid bai warke ba, pretend yake kamar mai lafiya amma a zahirin gaskiya bai da lafiya. Shi yasa take son yayi aure ko zai samu wacce zata jure matsalarshi,
"Kiyi hakuri haka yake, baya cin citta da tarfarnuwa ne, tun yana Yaro." Itama Hajiya ta fadi haka, shi kuwa gogan naku yana shiga dakin drower yaja ya Ciro kudi me yawan gaske, ya fito daga dakinshi kenan suka hadu da Amaan Mamman Ba'are,. Kallon kallo suka yiwa juna kafin kowa ya kame kanshi, akwai wannan rigimar na sako da sako, amma ita Hajiya bata taɓa kawowa al'amarin zai lalace har girman yaranta ba, a zahirin gaskiya tsanar da Amaan yakewa Majid tayi yawa da har sai da kowa yayi magana. Wani irin tsana ce irin na matukar na samu dama sai naga bayanka. Amma a bangaren Majid babu wannan tsanar kawai shi mutum ne da yasan ciwon kanshi da darajar kanshi,. Sannan bai kullaci Amaan har haka ba. Kamar yadda shi ya kullace shi, reni ne baya so kuma ya fahimci Amaan yana da reni da son abin duniya.
Kiyayyar tasu ta faro ne daga lokacin da Alhaji Mamman Ba'are, ya bar wasiyya akan cirewa kuri'arshi ya gadarwa Majid, sannan ko a halin jinya yadda Alhaji Mamman Ba'are yake ta rokon a nimo mishi Majid ya roke shi gafara kada ya mutu da hakkinshi ya kara tunzura dayawan mutanen dake jikinshi, bawan Allah nan har ya mutu da rokon a kira mishi Majid, don Allah ya yafe mishi.
Duk da akwai hakkin iyaye akan Yaransu, haka akwai hakkin Yara akan iyayensu, wannan al'amarin ya tab'a zuciyar kowa na jikin Mamman Ba'are musamman Hajiya Nana wacce idan taji yana cewa Majid ba zaka zo ba, Majid kana ina ne? Majid zan mutu ban ga fuskarka ba. Majid nasan na cuce ka, Majid kazo. Shi yasa bayan kome da ya warewa Majid, akwai wasu takardun da ya bawa abokinshi. Wanda babu wanda ya sani daga Hajiya sai Abokinshi Alhaji Abubakar Abzin, shima shahararren dan kasuwa ne da yake garin marad'i, kuma wani ikon Allah Alhaji Abubakar Abzin bai tab'a takowa zuwa Niamey ba, idan abubuwa suka shiga gaban Hajiya wurinshi take zuwa. Yanzu ma tunaninta kafin hutun Majid ya ƙare zata kai shi garin marad'i, su gana.
Wannan shine shirinta.
Sai da Majid ya jira Amaan ya shiga dakin, sannan shima ya shiga ya mikawa Hajiya kudin tare da mata magana da idanu, ta bawa Nabeeha. "Barka Hammayo." Inji Salaha matar Amaan, "Barka!" Ya fada a hankali, idan baka saka kunne ba, ba zaka ji me yace ba. Shigowar yara uku suna ihu, yasa shi juyawa. Sai wani guda daya da yake bakin kofar shiga falon Hajiya. "Appa kaga Shuraim ya dake mu ko?" Yaran suka nufi wurin Amaan, mikewa Amaan yayi tare da nufar Shuraim ɗin. Shima Aryan har zai mike Majid ya kalle shi, a fusace ya koma ya zauna yana kwafa. "Kai wato munafurcin da ka gada daga wurin wancan dan iskan Yaron shine zaka fara." Ya rike kunnen Yaron. Amadadin yaron ya fasa ihu, sai ga Amaan yana fasa ihu, babu wanda ya san me ya faru, sai yaron ne kawai ya san me ya faru. Daukarshi Majid yayi suka fita. "Daada taka mishi kafa kayi ko?" Ya rad'a mishi a kunne. "A'a" "Daada Allah yana kona me karya inji Ummina." Dakinshi ya shiga da shi, ya Ciro katon kwalin chocolate, ya mika mishi sannan ya kara dauko dayar ya ce mishi. "muje!" Haka ya riko hannunshi har falon Hajiya suka koma, zama yayi ya kira sauran Yaran, Yaran Amaan dake duk mata ne, tasowa suka yi duk da harara su da Amaan yake, haka suka tawo wurin Majid ya ajiye su a gefensu. Sannna ya mikawa yar karamar yar Aryan hannu da sauri ta taso. Ya ajiye ta" Kai Ayyan ka sammata a naka, Anum da Widad zan basu anan."
"A baco na Yaya!" Injin yarinyar. "Bushrah!" Babanta ya daka mata tsawa. D'ago kai Majid yayi ya watsa mishi harara. "Tow shi kenan tunda baki son na Yaya Anum a san mata?" Gyada kai tayi, ya bude musu kwalin ya ciro chocolate din ta ce mishi. "Dada a bacon na Anunu." Ta maida hannunta baya. Hajiya kuwa me zata yi ban da dariya ta ce mishi. " Ai yadda ka bawa sa'anta kwali itama haka zaka dauko mata kwali domin bata yarda a raba kansu da yan uwanta."
"Uwata taso muje." Ya dauki su Anum ya zaunar dasu a saman kujerar ya dauki Bushrah har dakinshi ya dauko mata nata, tun da ya bata, ta fara bashi labarin da Allah ya gani bai fahimci Yaren ba, har suka isa falon, bashi labarin take.
"Ja'ira mara kunya, dole ki bashi labari anya takwara haka zamu yi dake."
"Jiya babu luwana dake, ban baki cokulet dina ba " ta zauna ta yaga kwalin. Ya zube dukka. "Dada ashe min!" Wato ya kwashe mata, "abawa jiya." Ai kuwa Hajiya ta wafta ta ce. "Sai dai kada abawa gobe, amma jiya kan zan sha."
Haka aka yi ta hira har wani lokaci kafin lokacin magariba tayi duk suka tashi zuwa Masallaci..
*Sansanin gudun hijira*
#thedambuje
[2/16, 9:24 PM] Cutie cutie pie: *BAƘIN HAURE....🐾🐾*
{Greed for Money is the roots of all evils🫀}
Arewabooks:maidambu41
Wattpad:Mai_Dambu
Mallakar:Mai_Dambu
*010*
*Sansanin Yan gudun hijira*
Adamawan Kamaru.