← Book details Bakin Haure Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 138

Sashe 63

Bakin Haure Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Kusan shekara daya da rabi kenan, Umaimah ta kasa samo yarinyar da ya yanketa, yana tsoron kada sanadin wannan yankar ta mutu, domin yasan yadda irin wannan yanka yake, bakiɗaya jin shi yake sama-sama da zaran ya tuno da abinda ya faru. Sai yaji kamar yana da hannu a cikin abin da ya samu yarinyar tunda Umaima ta gaya mishi sun koma garinsu har anyi faɗa sun tashi amma taji labarin kamar faɗar da aka yi ya shafe ta, ko mutuwa tayi shi bai ma iya tuna abin ba, amma tabbas yaji Umaimah tana faɗin anyi faɗa a garinsu ga abinda ya faru, wani takurarren numfashi ya fesar, yana jin kamar bai kyautawa kanshi ba, na rashin ganin fuskar yarinyar amma ya rike muryarta, har a kwanan gobe ba zai manta da sassanyar murya mara amo da kwaramniya ba, shi fatan ma ya ga fuskarta ko sau daya ne, amma ina sai yanzu ne ma yake danasanin domin Umaima da ta gaya mishi, ita ce suka yi barci da ita a gado daya, a ranar da suka zo aikin ceto rayuwar sojojinsu, shafa kanshi yayi cikin tsananin damuwa da takaicin halin ko in kular shi, amma kuma a gefe guda sai yake ganin bai ga dalilin tunawa da ita ba. Meye hadinshi da ita? Meye matsalarshi da ita? Sam baya jin yana da wata alaƙa da zai saka shi tuaninta.
***
Yahunde. Cameroon,
Shashekar kuka take tana jin kamar zuciyarta zata buga, domin wani irin tukikin tashin hankali take ji a ranta, tana jin wani azazzben zafi da ciwo a ranta, ita kanta bata san iya adadin lokacin da ta dauka a gaban Mahaifinsu ba, kukan yayi yawa da yasa Yafendo tashi zuwa ɗakinta Sumee ce ta kasa hakuri ta ce mishi. "Ayya Ayya Datti haka zaka cigaba da kallonta, tana kuka abu biyu ta rasa fa, ta rasa miji da Yarta ai ba zaka zuba mata idanu har haka ba."
Yalwataccen murmushi ya saki, yana faɗin. "Bilkisu idan har Nafisah bata fahimce ni ba, ai ke ya dace ki fahimce ni. Iya su biyu mata Allah ya bani a tsakanin Ya'ya maza, Allah sai ya albarkaci rayuwarsu da jarabawa, idan ban gode mishi ba, me zan iya yi ? Alhamdulillahi Allah ya basu ikon cinye jarabawarsu."
Ya fada yana murmushin karfin hali, domin izuwa yanzu yasan yayi kuskure, ahalinshi sun yi kuskure da ya shafi bayansu. Kuskuren da yayi ba karamin kuskure ba ne, yayi watsi da Amanar da Allah ya bashi, ya watsar da Yaran dan uwanshi sannan ya rungume kashi.
A ina zai ga Isma'il da Aminatu? Ta haka zai gyara kuskuren da yake bibiyar Yaranshi mata da jikokinshi. Ace Yaranshi mata biyu, a wulakance ake aurar dasu, sannan mazajen su azabtar dasu da Yaransu. "Tashi ki tafi Allah ya kara miki hakuri da dangana, Ubangiji ya mata rahama, sannan ki rungumi Zaytoonah domin tana jin zafin hanata ganin mahaifinta, wannan ma wani jan aiki ne da dole sai kin yi da gaske. Allah ya kara miki hakuri."
"Baffayo." Sai kuma tayi shiru kafin ta fashe da wani irin kuka, "Sai hakuri idan har ka yi hakuri, akwai riba da fa'ida." Mikewa tai ta nufi cikin gidan, tana kuka har dakin Yafendo. D'ago kai Zaytoonah tayi tana kallon yadda take rusur kuka. Kauda kai tayi bata jin tausayinta ko kad'an, ta roke ta ta bata hakuri ta ce ta yanke mata kome, ita dai ta barta taje ta ga mahaifinta da Yayarta, amma taki sai yanzu zata yi wani kuka. Ita kuma da bata san shi ba fa? Ita da bata ji duminshi ba fa? Hmmm ita kukan dadi take tunda gata da nata iyayen ita kuma tayi mata asarar rashin ganin Ubanta. Ita yanzu ta tsani kowa ma banda Babynta, domin ba zata iya tsanar Babynta ba, tana son abinta kuma ba zata rabata da mahaifinta ba, domin ita nata rayuwar ta zama incomplete, tunda ta rasa inuwar uba, hatta zaman aure ya haramta a gare ta, domin abinda ya kashe mata aure har da gorin rashin uba. Haka kawai ta ja...
"Zaytoonah!" Mikewa tayi tare da ɗaukar yarta zata bar dakin. "Ki tsane ni babu laifi amma, idan kika nisance ni mutuwa zan yi. Da kewar shi xan ji ko da rashin yar Uwarki? Zaytoonah ina cikin wani yanayi da ban san mafarinsa ba, balle karshensa.....
#Mai_Dambu

```Hajiya ga kaya nan Masha Allah, Available price
Huluna da Mayafai, da na yara sai Wanda ranko yakeso gasunan kala kala, Hajiya muna dasu ba iya hulana da Mayafai ba, har da shadodin na fitar sallah, Hajiya domin hutar dake da fitar dake kunya na tanadi yadda ba zaku sha wahalar yawo kasuwa a cikin azumi ba, don haka kafin kishiyarki tazo ta sata au 🤣😹😂 kafin kishiyarki tazo ta saya na tayiwa mijinku shakara gara kizo ki sata au 😔🤣😹 baki ya saba gara kizo ki saya, barauniyar gida, kai Sarauniyar gida 😂😹 atow kayana na Uwaren gida da na Amare ne```
*TUNTUBE WANNAN NUMBER 08130269641*
Laces
ATAMFOFI
SHADODDI
Materials
Kayan yara
Veils
Huluna....etc
[3/7, 10:49 AM] Cutie cutie pie: *BAƘIN HAURE....🐾🐾*
Chapter 63 · 0% Book details