← Book details Ibtissam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 91 OF 146

Sashe 91

Ibtissam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

WASHE GARI�..

Pay your money into 2681892316 Aisha umar, zenith ban wai a turo da shaidar biya ta wannan number 07041879581.

https://chat.whatsapp.com/EiJWfeCdg234T6P0k5NU2Y

IBTISSAM
( A heart touching story of love and destiny)

Story & written
By
Mss Lee �

WATTPAD
https://www.wattpad.com/user/Msslee__

AREWA BOOK
https://arewabooks.com/book?id=652ff3a03fd6ffc37f68e4e2

___💕 BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM 💕___

BOOK 1
*PAID BOOK*
300 into 2681892316 Aisha umar, zenith bank . Sai a turo shaidar biya ta wannan number 07041879581.

S____25💞

WASHE GARI
Duk da yadda ‘kafafuwanta suke mata tsami hakan be hana ana kiran sallah asuba ta kasa farkawa ba, har wani lumshe idanuwa take sabida yadda baccin gabaki d’aya be isheta ba , da’kyar ta iya mi’kewa tayi Alwala tare da kabbara sallah , saida ta farayin nafilarta kamar kullum sannan tayi sallahr asuba d’inta , ko da ta idar bata Tashi akan daddumar ba sai datayi karatun Alqur’ani mai girma kafun ta tsaya yin addua , ta dad’e a kan daddumar nan tana addua har wasu ‘kwalla ne suke sakko mata a cikin idanuwanta musamman abunda su little sukayi mata , duk da basu san ko wacece ita ba sun jata a jikinsu kamar yar Uwarsu batare da damuwa da sanin asalin ko wacece ita ba , sosai tayi wa Allah Godiya akan canjin da ta samu arayuwa shiyasa ta d’auki al’kawarin kome suke bu’kata Indai zata iyayi musu shi toh tabbas zatayi shi koda hakan zai zamto akasin farın cikinta .

Big boss ne ya fad’o mata cikin rai musamman lokacin dayake lumshe idanuwansa, hakan da yake ba ‘karamun narkar mata da zuciya yake ba , taka sa gane dalilin da yasa duk lokacin da ta zauna ita kad’ai take Tuna’nın saba kamar yadda take yi a yanzu ,ganin bugun zuciyar ta na ‘ko’karin canzawa ne kamar yadda ya saba mata tun lokacin da ta fara ganinsa yasa tayi saurin ajje komai a gefe , ta fara gyara cikin d’akin tunda ynxu tasan yadda ake anfani da kayan sharan, Agogo ta kalla ganin ‘karfe 6:05am na safe yasa cikin sauri ta shiga toilet , shaf shaf tayi wanka bayan ta wanke toilet d’in, ko nutsuwa ta kasayi tanayi tana kallan time, cikin ‘kan’kanin lokaci ta Shirya cikin wata Doguwar riga Ash colour duk da bata Kai mata har ‘kasa ba sai wani black din wando da tasaka , hakan kuwa da tayi ko kusa babu inda jikinta ya fito ,kanta da yayi mugun cukurkud’ewa ta kalla gashi da uban tsaho da cikowa amma ita kanta bata iya wankeshi Sabida yadda yake da mugun yawa hatta ribbon sai dai a saka mata Inba haka ba gabaki d’aya sai ta cikurkud’e gashin nata , da Sauri ta yi rolling d’in ba’kin mayafin ta da gabaki d’aya ya rufe mata gashin kanta sai uban tudu da yayi na alamar gashi.

Iya kwana kinnan da Abla tayi ba’karamun canzawa skin d’inta yayi ba , farar fatar ta sosai ta fara washe wa daga duhu duhun da tayi , yadda take yin fresh sosai mutum sai ya d’auka wani mugun gyara take yiwa skin d’inta , ga farar fatar skin d’in ta da ya soma murjewa Sabida rashin aikin wahalar da bata yi yanzu, babu tension kamar lokacin baya da take aiki gidan uwar karuwai. Mood d’in fuskar ta ne ya soma canzawa Sabida kalmar uwar karuwai da ta tuna lokaci d’aya kuma da mutuwar Arwa da bazata ta’ba yafe Musu ba Sabida sun cutar dasu , su azabtar dasu kamar ba mutane ba , cikin Sauri ta share hawayen da suka zubo mata ganin time na wucewa .

A karo na biyu ta ‘kara kallan lokaci, da Sauri ta dafe ‘kirjinta ganin saura ‘yan mintuna 7 tayi,ga mugun tsoron da take ji musamman yadda take hango simba cikin idanuwan ta . Cikin Sauri Sauri , gudu gudu ta fito daga cikin d’akin, uban tilin kayan da ta gani a ‘kofar d’akin tane yasa ta ja burki tana binsu da kallo, ta gane kayan da suka siya jiya ne , ga time yana tafiya bata tsaya duba komai ba ta soma d’aukan ledojin tana shigar dasu cikin d’akin, saida ta saka komai gabaki d’aya taja kofar ta fita batare da ta ‘kara bi ta kansu ba .

** Babu kowa a falourn sai ‘kamshin turaran da ya cika ko ina, gashi gabaki d’aya falourn yayi fes babu alamar datti ko ‘kura , tana tsaye a falourn tana bin ko ina da kallo , kullum ta kalli falourn sai taga kamar ‘kara masa kyau ake , duk da yadda falourn ya d’auki shiru hakan be sa ta zauna kan kujera ba sai gyara tsayuwarta da tayi , gani take kamar tana zama za’ace mata ta tashi , gashi har yanxu ‘kafarta bata dena zafi ba sabida hawa da sauka da ta dunga yi jiya.

“Sister?”cewar little lokacin da yake fitowa daga cikin elevator, sanye cikin kayan motsa jiki black colour ga gyara gashin kansa da kullum ‘kara masa kyau yake ,itama martanin murmushin ta mayar masa da har saida dimples dinta suka motsa na both side � yaya little ina kwana ?�, A maimakon ya amsa mata sai ma wani murmushin da ya ‘kara sakar mata , sabida yanaso yaji tana kiransa da yaya little , inda take a tsaye ya mufa har lokacin da murmushi akan fuskarsa “sorry sister jiya mun barki a wajan yaya big boss� a hankali cikin siririyar murya Abla ta furta “bakuyi mun komai ba ai and nagode sosai da sosai�, kansa yayi mata knodding kafun ya furta � yanxu kenan kin saba da simba tun da kika iya kai masa abinci ko?�, a zabure Abla ta ja baya , ga tashin hankali da ya fito mata kan face d’inta , cike da tsoro little ya kalleta “Menene?� Abla kamar zatayi kuka ta furta � Namanta bankai masa ba , kuma ni tsoran sa nake ji� , lokaci d’aya little ya furta � Innalillahi, me yasa baki kai masa ba ? Kinsan yaya kuwa ? Yanxu 7:10 fa , taho mutafi kafin ya fito please� cikin Sauri Abla tabi bayansa dan ayanxu tafi tsoran hukuncin da big boss zaiyi mata akan sojojin da take gani a cikin gidan, dukda yau ta d’an wuce a raku’be bakamar sauran lokuta da sai su little sun kare taba .

Cikin Sauri Sauri little yake tafiya dan yasan idan big boss ya sakko bazata ji da dad’i ba , babban Tashin hankalinsu suna zuwa suka tarar da Victor ya kulle door d’in, little har zai soma magiya akan ya bud’e musu Victor ya sanar dashi umarnin big boss , 7:01am nayi na safiya za’a dunga kulle ‘kofar ,lokaci d’aya little ya tsure , Abla kuwa kwalla ce tabb ta cika mata cikin idanuwa musamman tuno punishment din da ya bata jiya. “Don’t cry bari na kira yaya bobo kinji?� Yana kai ‘karshen zancansa ya zaro phone d’insa tare da dialing number Bobo, ringing biyu kuwa bobo ya d’auki wayan , bansan me ya ce wa little ba sai d’an zaro nasa eye d’in da yayi shima yana kallan time , a hankali kamar zaiyi kuka ya furta � okay yaya am coming�, yana kashewa little ya kalli Abla � am sorry sister , yanxu yaya bobo yana kirana nima na makara wajan training , kuma idan yaya big boss ya ganmu zai hukunta mu,� cikin Sauri kuma ya furta � but karki damu insha Allah bazai miki komai ba kinji?� Kamar zatayi kuka tayi masa knodding kanta , da kansa ya rakata part d’insu kafun shima cikin Sauri ya wuce Wajan training.

Kamar wata mara gaskiya Abla ta soma sand’a cikin falourn tanasan guduwa d’aki Sabida kar tsautsayi yasa ta had’u da big boss , shiyasa a hankali take taka ‘kafarta yadda bazai bada sauti ba , daga sama taji sautin muryar prince � Little sister ?� A tsorace Abla ta juyo jikinta har ya soma rawa bata gama gane muryar ko wanene ba ta furta � Dan Allah kayi hakuri , anjima zan basa abincin�, kallanta prince yayi har yana d’an zaro mata idanuwansa , fuskarsa da mamaki ya furta � Baki bawa simba abinci ba ?�, Kanta ta jinjina masa kamar zatayi kuka , a fili Prince ya furta � Tashin sense , kinsan me yaya yafi tsana kuwa ?� Ya tanbayeta yana kallanta , itama a d’an tsorace ta furta � Ah, Ah �, ya tsani ya bada umarni mutum ya sa’ba masa , ki dunga kiyayewa kinji? And yanxu kinga yaya bobo yana jirana, kiyi sauri ki gudu d’aki kafun ya fito� yanxuma cikin kalar tausayi ta gyad’a masa kanta, yana barin wajan Abla ta turo bakinta a shagwa’be kamar zatayi kuka � sai yayi ta d’aurewa mutum fuska kamar tuwan Alkama , mutum ko fara’a bayayi fisabilillah, Dole adunga yayya fa maka ruwan Alwala�, sai kuma ta d’an ta’be baki tana kwaikwayar muryarsa. � 7:00am Kikai wa simba abinci, 3pm ki kaimasa, 8pm ma ki kai masa , bazaki kwanta ba sai kin had’a coffee , yen yen yen , yen yen yen , da zan samu bindiga da sai na harbe kan zakin nan , mugu kawai�.�,kalmar mugun ce ta tsaya ma ta cikin ma’kogwaranta lokaci d’aya ta zabura ta na to she bakın ta sa bi da ganin Wan da ba ta yi tsammanin ga ni ba.
Chapter 91 · 0% Book details