← Book details Ibtissam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 146

Sashe 22

Ibtissam Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

dunga kashemun ‘kishirwata to zakiji dad’in ki aduniyar nan zakiyi abunda kike so , abu d’aya nake so kawai ki bani kanki, ba wani dogan abu bane zamu dungayi fa , dad’in junanmu kawai zamu dungaji �, ta ‘karasa tana taunar le’banta, dogon tsaki Abla ta saki tayi wucewarta, batasan sau nawa zatayi musu magana ba , dole ne ? Mai yasa kowa bazai temake ta dan Allah ba sai ya saka zancan yana san jikinta ? Allah kai ne ga tana , Allah ka nesan tani da aikata wannan mummunar aikin da zan sa’ba maka �, gabaki d’aya wad’annan zantukan a zuciyarta Abla takeyinsu har ta ‘karasa shirgin store d’in da suke kira d’akinsu . A zaune ta tarar da Husna da Aneesa suna yin breakfast, � Abla na d’auka ba kya nan ai, ki zo muci abinci mana � girgiza mata kai Abla tayi tana zama kan kwalin da take kwana � Karki damu Anee na ‘koshi, ina ilham ? Banganta ba �, Aneesa zatayi magana aka turo ‘kofar toilet d’in d’akin , ilham ce ta Fito d’aure da zani da Alama wanka tayi tana ganin Abla tayi saurin ‘karasawa Wajan ta tare da hugging d’inta � kiyi hakuri Abla yanxu nake shirin zuwa wajan ki sai gashi kin shigo , Kinci abinci ?�, jinjina mata kai Abla tayi � nashigo d’akin d’azu amma banganki a cikiba, a ina kika kwana ?� Sun kuyar da Kai ilham tayi � kiyi hakuri abla na kwana a d’ayan store d’in ne Sabida kar su Zinariyya suce zasuyi mun wani abu ne �, okay kawai Abla ta ce mata , tana bin Husna da taja dogon tsaki da kallo, � ke komai sai kinyi shish shigi a ciki? Ina ruwanki da inda ta kwana ? Ko a shago taje ta kwana ina ruwanki? Idan ke bakyasan kiji dad’in rayuwarki ki ‘kyaleta mana ana dole ?�, cewar husna da tunda Abla ta shigo ta had’e ranta , amaimakon ran abla ya ‘baci sai ta sakar mata d’an guntun murmushi � husna kibi duniya a sannu, idan baki bita a sannu ba to tabbas ke zata koyawa hankali, Menene abun burgewa a sa’bawa mahalicci? Kina ganin wannan hanya ce me kyau da kike maganar jin dad’in rayuwa? Karki manta Allah da ya saki cikin wannan rayuwar ba mantawa yayi dake ba �, da Sauri husna ta d’aga Mata hannu � bani da lokacin jin wa’azin ki, in wa’azi zakije ki tafi masallaci, kin ganni nan yanxu na fara rayuwa , yanxu nasan dad’in rayuwa , jin dad’in rayuwa kuma yanxu na fara dan sai na tara dukiyar da duk inda nashiga za’a kalleni � d’auke dubanta Abla tayi ta mayar dashi kan Aneesa da tayi shiru tana binta da kallo kamar akwai abunda yake damun ta , amma itama batace mata komai ba shiyasa ta mi’ke ta nufi hanyar fita daga d’akin , tana jin muryar Husna da ke furta � munafuka komai zakiyi sai kin nuna mana kin fimu sanin Allah , ke ubanwa yasan me kike aikatawa da Alama ke tuni aka gana kwakuleki shine mu kike mana ba’kincikin kud’in da zamu samu�, lumshe idanuwanta abla tayi da suka soma yi mata yaji , tana fitowa babban falon gidan ta tarar da Zinariyya da yar shiga a zaune suna duba wasu hotuna , � ke � yar shiga ta daka wa Abla tsawa, banza Abla tayi musu dan ranta ya soma ‘baci yanxu , � dan uwarki ba dake nake magana ba � da Sauri rai a ‘bace Abla ta jiyo ta zuba mata eyes d’in ta , kallo d’aya tayi mata ta d’auke kanta har ta nufi hanyar fita da ga gidan gabaki d’aya . Kallan shila , Zinariyya tayi � Anya babe wannan yarinyar ba aljanune da ita ba ? Nifa wallahi tsoro take bani ko me kika ga inayi mata cikin ‘karfin haline kawai nake yi , musamman idan ta zuba maka wad’annan shegun idanuwan nata kamar na mayu , gashegen kyau kamar aljana �. Itama yar shila tsaki taja � ni kaina shegiyar nan wani lokaci tsoro take bani , amma ba aljana ba Wlh ko uwar aljanace sai na kashe ‘kishirwata akan ta , ki duba kiga ‘kirjinta , a cike yake tam ko ni da maza suke ta’ba nawa haryanxu basu kai nata girma ba , ga uban hips da take dashi , haushina ma yadda take saka hijab kullum bata bari ina ganinsu sosai Kema kinsa wallahi ba ‘karamin dad’i zatayi ba .”gabaki d’aya sai suka ajje hotunan da suke kalla suka soma zanjan Abla da surarta da irin sha’awar da suke mata .
Chapter 22 · 0% Book details