Sashe 21
Ibtissam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Misalin ‘karfe 3:00am na safe aka bud’e kofar store d’in da aka kulle Abla a ciki, wani ruwan datti me shegen wari Debeka ta watsawa Abla a jiki , a firgice ta farka bakinta na anbatan � HASBUNALLAHU WANI’IMAL WAKIL�, bakin ta da take adduar Debeka ta buge mata da bokiti da yasa Abla bud’e dara daran ash colour eyes dinta, duk da gari be gama wayewa ba hakan be hana kyawawan idanuwanta ‘kara fitowa sosai ba.kallan jikinta da aka watsawa ruwan datti tayi ga sanyi sanyin da ta fara ji lokaci guda Sabida sanyin ruwan, Debeka na tsaye sai faman hura hanci take tana girgiza ita kadai, cikin tsantsan tsanar da takewa Abla ta soma magana � Dan ubanki zaman me kike da bazaki mi’ke ki soma aikin kiba ? Shegiya me farar ‘kafa , na tsaneki! Na tsani duk wani me san ganin farincikin ki! Ni d’innan sai na zame wa rayuwarki kabari, Indai ina raye sai na Mayar dake karuwa , irin karuwar da kwanda kare a kanki, sai na lalata miki rayuwa gabaki d’aya , ki tashi stupid ki fara ayyukan ki dan yau gabaki d’aya ke zakiyi komai na gidan nan Dan ubanki � ta ‘karasa tare da sakar wa Abla rankwashi aka dayasa ta dafe wajan . Jiki a sanyaye tayi ‘ko’karin mikewa gabaki d’aya jikinta ba kwari musamman zazza’bi zazza’bin da taji yana ‘ko’karin kayar da ita, ganin yadda take tafiya a hankali yasa debeka cike da mugunta ta hankad’ata har saida ta fad’i , bata jira mi’kewar Abla ba ta jata a ‘kasa kamar kayan wanki har saida tafito da ita babban falon tukunna tayi wurgi da ita . “Hour biyu na baki ki share ko ina na gidannan, kije ki wanke komai da aka ‘bata sannan duk d’akin da kika shiga ki tattare mun condums d’in da sukai anfani dashi ki kawo mun, saura dan ubanki ki sa na zauna zaman jiranki,� tana kai ‘karshen zancanta ta buga tsaki tare da barin Wajan . Bin falon Abla ta somayi da kallo take tsoro ya fara shigarta ganin ba kowa a falon cikin dare sai ita , sabida tsabar mugunta irin ta debeka ga baki d’aya fitulun ta kashe sai wata mara Haske da ta bar mata gud’a d’aya . Karkarwar da jikinta ya somayi ne ya ta tsugunna, ga kayanta jikakku da sanyi ke faman ratsa ko ina na jikin ta, ga zazzafan zazzabin da ya fara rufeta , gefe d’aya ga cikinta da yake murd’a mata sabida yunwar da takeji . ‘Karar yunwa da cikinta ya ‘karayine yasa ta dafe cikin nata da duka hannayenta biyu , cikin rawar murya ta furta � la’ilaha illa anta subhanaka inni kuntun minazzalumin , ya Allah kaine kace muro’ke ka , Allah kaga halin da nake ciki , kafi kowa sanin abunda yafi dacewa dani , Allah na ro’kewa ka karemun zuciyata daga fad’awa cikin halaka, Allah na ro’keka kasa na zama me tawakkali da kawo kukana wajanka,Allah kai Arrahim ne , me rahma, Allah kasa ina cikin wannan rahama taka , Allah nagode maka a yadda Kayini, Allah na ro’keka ka kareni daga cikin Sharrin masu sharri,ka nesantani da aikata sa’ba maka �.muryarta da ta ‘kara dusasewa tayi shiru lokacin da cikinta ya ‘kara mund’a mata, yadda ta rungume shafaffen cikinta gwanin tausayi amma duk da haka babu ko d’igon kukan da ya sakko kan kyakkyawar fuskarta.a hankali ta ‘kara d’ago da dara daran idanuwanta tana bin ko ina da kallo kafun ta yun’kura ta mike tana tafiya a hankali tun lokacin da Debeka ta hankad’ata ‘kafarta ta rike amma a hakan ta fara gyara kaca kacan falo dake cike da kayan kwalabe, kwanukan abinci har kazantar da bai kamata a samu a falon ba , haka ta Samu ta gyara shi da ‘kyar sai faman nishi take . Tana gama gyarawa sama ta hau d’akin da babu mutane shima haka ta shiga ta gyarasu Saura kad’an amai ya kwace mata da kyar take shiga d’akin ko ina ta duba zaka condums ne da wasu abubuwan , a maimakon ta tarawa debeka abunda ta bu’kata sai gabaki d’aya ta zuba su a shara , ta gyara band’akunan da ya gama cika da ‘kazanta, d’akin da ta gyara na ‘karshe sai da amai ya kwace mata , gabaki d’aya ta galabaita jikinta yayi weak . Zuwa wannan lokacin 5:30 yadda a gogo ya nuna wa tahee and tabbas tasan debeka ta koma baccin da take, cikin Sauri ta nufi hanyar da zai sadata da d’akinsu, tana shiga komai a hankali take har ta kunna kwan d’akin shirgin dasuke kira d’aki yanxu . Tsayawa ‘karewa d’akin kallo Abla tayi ganin sabuwar babbar katifa da akasa a d’akin ga ledojin kayan ciye ciye da suka ci, su su ukune kwance akan katifar daga husna sai Arwa da Aneesa , mamakin inda ilham take a wannan lokacin Abla ta fara ganin bata da lokaci sosai yasa ta d’auki ragowar kayanta da ya rage mata , cikin Sauri ta fad’a toilet tayi wanka da ruwan sanyi me shegen sanyi tare da abun buhun da ya zame mata tamkar soso haka take sawa a jikinta dukda ba dadin anfani takeji dashi ba, sosai Abla ta wanke jikinta da tankad’addiyar kasar da ta zame mata tamkar sabulun wanka, sai data gamane idanta ya sauka kan wani guntun sabulun wanki kmar wacce akayi ba babbar kyauta haka ta samu ta ‘kara wanke jikinta sosai, kayan ta da debeka ta ‘bata mata ma ‘kasa ta samu ta wankesu sosai ta shanyasu bayan ta sakar ragowar yargalalliyar rigar da zata Iya du’kar ‘kirji take kayan ta ne , dogon hijab d’inta Amma debeka har dashi ta ‘bata mata , dogon mayafinta da shima ya gama kod’ewa ta yana a jikinta Daidai lokacin da ake kiran sallah, ‘kofar d’akin ta kulle kafun ta tayar da sallahrta, tana idarwa bata jira tayi addua ba Sabida kar mutanan falon su Fito su tarar da ita tana sallah, sallar isha’i da batayi jiya ba ta samu tayi tana raka’ar karshe zatayi sallama akan idan debeka da ta ‘kara farkawa , tahee na tahiyar ‘karshe da sauri debeka ta juya Adaidai lokacin da Abla ta idar da sallarta zata soma addua taji saukar abu meshegen zafi kamar katako a jikinta , ba abunda take sai � ko’karin kare jikinta da take yi yadda debeka ke jingarta kamar Allah ya aikota da muciya, Abla ko ihu ta saka ganin yadda su Arwa suke bacci gashi ko d’igon hawaye babu akan fuskarta saida debeka ga jibgeta sanranta kafun ta ‘kara janta kamar wata kayan wanki, a wannan karan kukan da takeso tayi ma ta kasa sai kukan zuci daya fi komai ta’ba zuciyar mutum, amma dukda haka Abla godewa Allah take ganin saida ta fara sauke abunda ke kirjinta na sallar da tayi, a zuciye debeka ta kalleta bayan ta jefata wajan wanke wanke � ki tabbata kin wanke komai da komai dake wajan nan , idan kika kuskura nazo na same ki baki kammala ba na lahira sai ya fiki jin dad’i, shegiya me kama da aljanu�, sai kuma ta juya fuuuuuu tabar Wajan. Kallan tunin uban wanke wanken da aka ‘bata tayi kamar wa’yanda sukai sati basayin wanke wanke amma tsabar ‘Kazan tace kawai , kafin ta mayar da kallanta kan klin din da aka bar mata kwalli d’aya da ko rabun wanke wanken bazai wanke su ba. Gugar rijiya ta d’auka , ta d’au tsawan lokaci tana d’ebo ruwan wanke wanken kafun ta soma had’a kwanukan, komai cikin ‘karfin hali take yinsa ganin jiri jiri na neman kwasarta ga uban yunwar da takeji kamar hanjin cikinta zasu fito waje , Arwa ce ta Fito tsakar wajan sanye da wani guntun hijab d’inta , tana ganin Abla tayi saurin ‘karasowa wajan wanke wanke , � Abla� ta furta a hankali , da Sauri Abla ta d’ago eyes d’inta da take ganin biji biji ta zubasu akan Arwa , itama murmushin Abla ta sakar mata � finally kin Tashi ko? Hope kinyi sallah �, wajan d’oraya Arwa ta ‘karasa kafun ta furta � Nayi Abla , bari na taya ki d’aure kwanukan sai muyi saurin gamawa �, a hankali Abla ta furta � nagode Arwa �, Arwa bata ce mata komai ba sai d’orayar da ta somayi mata , jefi jefi kuma suna d’an yin hira kad’an kad’an. Sai wajan ‘karfe 9:10am suka kammala wanke wanken lokacin sosai kuwa Abla ta jigata , ji take kamar kayan cikin ta zasu fito waje , kamo hannunta da Arwa tayi ne yasa ta mayar da dubanta zuwa wajanta, sai da arwa ta duba gefe da gefen ta gudun kar wani ya fito , kafin cikin ‘kasa ‘kasa da murya ta furta � Abla akwai abunda nake so na fad’a miki…�, kallan ta sosai Abla tayi ganin kamar akwai abunda yake damunta � shikenan inajin ki Arwa �, ‘kara maida dubanta Arwa tayi gudun karwani ya shigo wajan � Dama Abla �.� Bata ‘karasa zancenta ba taji taku da Sauri tayi shiru tana kallan hanyar shigowa , Zinariyya ce ta shigo wajan tana bunsu da wani shegen kallo , kafun ta tsayar da kallanta kan Arwa da jikinta ya fara rawa, a yatsine ta nuna mata hanya � kije ana kiranki yanxu �, kallan Abla , Arwa tayi kafun tayi saurin barin Wajan , “ke � Zinariyya ta dakawa Abla tsawa , kallanta abla tayi batare da tace mata komai ba dan magana ma wahala take mata yanxu � ga wanki na can kije ki kwasosu, idan kin d’akko ki biya ki d’akko na yar shila da na debeka, gabaki d’ayansu hour 1 na baki ki wanke su duka �, shareta Abla tayi zata wuce Zinariyya ta janyo hijabinta har saida ya yage, ta d’aga hannu zata mareta Abla tayi saurin rike hannun , a zuciye cikin disashewar murya ta soma magana � kashe ni kuke san kuyi ? Me nayi muku?Me nayi muku Haka da kuka tsaneni? Me kuke so a waje na ?Me na tsare muku haka ?�, a maimakon ta bata amsar tanbayoyinta sai ta soma bin jikinta da kallo � ke kyakkyawa ce,sannan duk Wanda ya ganki zaiso ya kashe ‘kishirwarki, ni na miki al’kawari Indai zaki