← Book details Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 145

Sashe 76

Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Allahumma ajirni fil musibatii, Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" ta faɗa ta sauri ƙirjinta na bugawa da ƙarfi kafin ta sake motsawa jiri ya kwashi ya kaita ƙasa, kanta ya daki jikin canter na parlourn. Ba ita ba shi kansa sai da ya ji kunyar yadda ta samesa tare da Surry, amma sai ya zame ko a jikinsa. Ta jima durƙoshe ko idanu ta kasa buɗewa sai duhu da ta ke gani kamar mai hawan jini. Sunayen Allah ta ke faɗa babu saurarawa, a hankali ta ɗauko tare da ƙara duban Surry wacce ke kwance jikin Adnan tana shafa gashin ƙirjinsa wanda da alama bai daɗe da yin wanka ba, ko ita bata samu damar yin haka ba, amma wata banza ce kwance jikin mijinta. Abin ka dame haƙuri wanda idan ya ta shi abu bai iya yinsa ba.

Duk da jirin da ke ɗau kanta haka tai kan Surry kamar mahaukaciya, yadda ta nufi Surry zaka ɗauka aljanu gareta. Tana zuwa ta damƙi wuyanta tana shaƙeta zafin shaƙar ya sa Surry sakin ƙara.
Hankali tashe Adnan ya yi kan Abra zai daka kafin ya ƙarasa Abra ta damƙe ƙirjin Surry wanda ya kewa Adnan iyayi dasu, wani ihu Surry ta kwarara tana faɗin.

"Wayyo Allah! Zata tsinka zata tsinka na shiga uku" ganin yadda Adnan yayu kanta gadan-gadan ya sanya ta ƙara fisgar ƙirjin Surry. "Wayyo uwata wayyo wallahi ta tsinka" da gudu Abra ta saki Surry ta koma part ɗin ta.
Tun kafin ta ƙarasa jikin gado jikinta ya fara rawa numfashinta ya fara fisga kamar mai Asthma idanunta rufe ya ɗauki Alkur'ani ta fara karatu da dukkan muryarta wacce ta kusa cika part ɗinta dana Adnan Aliyu Matawalle ɗin. A karatu ta ke da iya ƙarfinta tun tana yi da ƙarfi har numfashinta ya kasa jurewa, a hankali tai gaba tare da kifawa muryarta a sanyaye ta ce.

"Ka gani ko Faris?"
Cak kuma Numfashinsa ya tsaya. A haka rayuwar Adnan da Abra ta kasance tsayin sati biyu tun daga ranar kuma bata sake saka shi cikin idanunta ba.

Mami damuwa tai mata Abbi ya tsallake ya barta, babu Salman É—an da ake tutiyya da shi kullum gida shiru kamar mayya lokaci zuwa lokaci kewar Abra na damunta ko za ta ce za kici Ubanki Abra yau ta ji zamanta na É—auke mata kewa. Faris baya nemanta wani time É—in ta kira number Abra sai ace a kashe.

Cikin sati na uku mafarin faruwar komai tare da toshe da kuma asalin abin da zuciya ke É—auke da shi, mafarin rusa farin cikin wasu.
Iddar da sallarta kenan ta nufi bathroom tare da yin wanka, a hankali ta fito da ga cikin toilet ɗin ɗaure da ƙaramin towel wanda ya tsaya iya cinya ruwa na zuba a jikinta, ga gyaran jikin nan nata yana nan fata sai glowing ta ke. Tana cikin tsane jikinta ta ji an murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin kafin ta motsa ya shigo cikin bedroom ɗin, a hankali ya ke binta da kallo kamar wanda baya cikin hayyacinsa, hannunsa dafe da cikinsa wanda ya ke masa matsanancin ciwo har idanunsa sai da suka nuna alamar hakan. Fararen ƙafarta yabi da kallo zuwa hips ɗinta kana ya maida kallonsa zuwa sama. Kamar wanda ake fisga da mayan ƙarfe haka ya nufi inda ta ke, tsoran yanayinsa ya sanya Abra fara yin baya tare da ɗaga ƙafa zata gudu, domin tunaninta dukanta zai. Gaba ɗaya ta jita male-male a saman ƙirjinsa ya rungome ta tare da bata ƙyakkyawan ma sauki a ƙirjinsa. Bai zo da niyyar hakan ba amma gaba ɗaya a kallon farko tunaninsa ya tsaya, cikin ƙaramin lokacin abubuwa da suka faru suka zama abu mai matuƙar baƙin ciki a rayuwar Abra Khamal Khamis, domin babu imani cikin lamarin Adnan bata taɓa tunanin haka al'amarin ya ke ba, bai saurara mata bai nuna mata soyayya kulawa tare da tattali ba, bai barta ba sai daya tabbatar da ita matsayin cikakken mace wacce tabi layin saurin mata.
Wani zazzafan zazzaɓi ya rufe Abra jikinta sai rawa ya ke, haƙoranta na haɗewa a haka ya tsallake ya barta ya nufi nasa Part ɗin yana jin ciwon cikin ya lafa sai kansa da zazzaɓi shima daya saukar masa.

Duk inda kake tunanin azaba a wannan daren Abra ta shata, sai Subhi ta samu tai wanka tai sallah jiki na rawa ta koma ta kwanta tana jan numfashi, a hankali hawaye ya sakko mata tunanin kiss ɗin Faris ne ya faɗo mata, soyayya da ƙauna haɗi da kulawa sune ta ke gani cikin idanun Salmanun-faris a lokacin da ya ke sumbatar bakinta. Misalin 1:20 ya turo ƙofar ya shigo kamar ma ƙasar zai bari sai dube-dube ya ke alamar abu ya ke nema ko inda ta ke bai kalla ba. A hankali ta sauka da ga gadon ba zato ya ji ta riƙe masa ƙafafuwa tare da ɗora kanta a jikin ƙafar tasa, wani raunataccen kuka ya ƙwace mata cikin kuka ta ce.

"Kaji tsoran Allah ka daina azabtar dani da abin da bai san da shi ba,ka faÉ—a min laifina wallahi zuciyata zata buga,ina Soyayyar da kake min? Ina kulawar da ka ke faÉ—a min kayi min adaninta ko haka auren ya ke? Don darajar Allah da Manzonsa ka faÉ—a min abin da nai maka"

Kallon ta ya yi sai kawai ya juya zai fita da sauri ta ce. "Matar ka ce ni, har lahira da ke zanyi alfahari bani da kamarka a yanzu kai ne duniya ta, kai ne dangina kai ne komai nawa, ba danni ba ba dan na isa ba ka faÉ—a min abin da nai maka na san kana so na"
Murmushi ya yi tare da sunkuyawa ya ɗagota zuwa tsaye cije baki tayi sbd zafin da ta keji ko tsaiwa bata iyawa. Shoulder ɗinta ya riƙe tare da matsawa ya ce.
"You deceived yourself Abra Khamal Khamis, Adnan Aliyu Matawalle bai taɓa sonki ba, kuma bai taɓa sonki ba, infact mujiya ki ke a cikin idanuna" girgiza kai tayi bakinta na rawa ta ce "what... what do you mean by that? baka so na kake cewa" hannunsa ya sanya ya tallafo fuskarta ya ce. "Idan baƙin maciji ya sareki ina da tabbacin ki kaga baƙar leda cewa zaki shine, wallahi da naga fuskarki gwara na kalli mujiya, a duk lokacin da naji muryar ki ji nake kamar ana zuba min ruwan dalma a zuciya, idan kina kusa dani kowa ji nake kamar na saka hannu na shaƙeƙi na huta, babu abin da na tsana a duniya kamarki bana Sonki bana Sonki bana Sonki na tsaneki kamar yadda bana ƙaunar mutuwa ta a yanzu" baya Abra ta yi kamar zata faɗi tana riƙe ƙirjinta ɗakin ne ya shiga juyawa mata wani duhu na mamaye cikin idanunta gyara zaman hearing aid ɗin ta yi ko tunaninta ita ce bata ji daidai ba. "Baka so na mene yasa ka aureni?" "To take a revenge"

"Revenge? Me na yi maka ni? mene aikata maka da har zaka ɗauki Revenge akai na?" Murmushi ya yi kafin ya ce "Baki min komai ba, laifin da Ubanki ya yi min shi ne ya sanya zan ɗauki Revenge akanki, zan raba shi da farin cikin sa kamar yadda ya zama silar lalacewar nawa, ba zan taɓa yafe masa ba sai na tabbatar yaji Abin da naji this is my promise" Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wacce rana ce wannan me ya ke son faruwa da ita? Rarrafawa ta yi zuwa inda ya ke tana riƙe ƙafarsa ta ce "Me Abbina ya yi maka? Wallahi Abbina ba zai taɓa cutar da wani ba, idan ma ya yi sai dai kuskure kada ka cutar dani don girma Allah ban san komai ba" gyara tsaiwa Adnan ya yi ya ce "Ba muriƙinki nake magana ba, ba Abbinki ba Uba maifi wanda ya yi silar zuwanki duniya" "Abbine mahaifina bana da wani Uba sai shi shi ne mahaifina" dry Adnan ya sake yi kafin ya ce "Abra Khamal Khamis? To ba haka sunan naki ya ke ba, ke TSINTACCIYA ce, tsintar ki Abbi ya yi acikin jeji ya ɗauki tare da baki kulawa kamar ƴar cikinki, kuma ke ɗin bawai Shegiya bace mugun Ubanki shi ne yaja baki yadda ya rabani da farin ciki shima sai na raba shi da shi, zan ɗauki fansar abin da ya yi min akanki *REVENGE MARRIED* Sunan aurenmu" "bana da wani Uba wanda ya shige Abbi kai ma ka sani" hannunsa ya tsawa ya ce "bance ki yarda ba, amma ni da Abbin naki musan cewa ke ba ƴarsa bace kiyi tunani kaf dangin ku dawa ki ke kama? Just think bance ki yarda ba, amma zaki rayu a gidan nan tamkar baiwa!"
[10/13, 11:29 AM] Abk: Take jikin Hajiya Na'ima ya ɗau rawa, hannunta ya fara karkarwa, ta nemi guri ta zauna a gefen gado, wani irin gumi yana tsatstsafowa a goshinta, a hankali ta furta "Na shiga uku, mai yaron nan yake nufi dani ne?" Cikin azama ta miƙe, ta ɓoue takardar ba tare da ta nunawa kowa ba.

Sai ƙarfe takwas na safe sannan Adnan ya shigo gidan, shi ma bai shigo inda take ba, maganarsa ta jiyo a parlour suna gaisawa da waɗanda da suka kawo ta, hakan ya sa ta fita parlour'n da sauri, zuciyarta cike da ɗokin ganin shi.

Gaishe shi ta yi, sarari ya ji ta amma ya É—auke kai kamar bai ji ba, hakan ya faÉ—ar mata da gaba. Amma dai ta daure suka yi sallama da waÉ—anda suka kawo ta, har da kukanta lokacin da suka fice daga parlour'n.
Chapter 76 · 0% Book details