Sashe 109
Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yanzu waye za shi can ɗin?" Sp ya tambaya yana katse kiran da Fayyad ke sake yi masa. "Ina ci-gaba da bincikawa, Private investigator muke buƙata wanda zai komai cikin sirri ba tare da mutumin ya fahimta ba" shiru Sp yai can ya ce "Ok a bani case ɗin zani" I.g ya zare idanu yana faɗin "Rufa mini asiri, a ba aikin bane kai kake da ikon zaɓar wanda za shi ma, rashinka ya sa na tsaya a akan abun ba girman ka bane sam".
"Ina son barin ƙasar ne daman, sabida na samu peace of mind amma zan bar komai naje ƙauyen da kai ne a can na samu nutsuwar zuciyar ka amince kawai, ba ruwana da girman aikin da nayi" I.g ya daɗe yana jinjina al'amarin, ta ya ya Sp da kansa zai je bincike? Amma kuma zuwan Sp ɗin shi ne daidai domin ya san me yake. "shikenan All the best yaushe zaka tafin?"
Sp na Miƙewa tsaye ya ce "Gobe" Sallama sukai Sp Adnan Aliyu Matawalle ya koma gida yana zuwa ya samu Usman da Fayyad a can gidan suna zaman jiransa.
Abbi na zaune hannunsa riƙe da Aishatul-humaira yana mata wasa, ta kafesa da fararen idanunsa duk idan yai da fuskarsa tana biye da ita dai na wasan zata saka kuka tana harba ƙafa, yana ci-gaba kuma zata kafesa da idanu wani lokacin har dariya take masa. Kamar daga sama yaga Mami ta faɗo cikin ɗakin nasa tana huci kamar zakayya. Kallonta kawai yake ba tare da ya ce komai ba. "Ni zaka ci amana kayi mini kishiya ba tare dana sani ba Khamal? Ban cancanci haka daga gareka ba, me na aikata maka har haka da zafi?" Kwantar da Aishatul-humaira yai yana gyara zama ya ce "Ba kiyi mini komai ba Na'ima, kawai naji ina son ƙara auren ne saboda Ubangiji ya bani dama kuma ya hure mini arziƙin da zan haka daga ɗaya har zuwa huɗu" cikin raunin murya Mami ta ce "Me na yi maka to? Ka rasa wacce zaka aura sai wannan Shegiyar karuwar? Wallahi idan ina gidan nan babu Shegiyar data isa ta shigo gidan nan a matsayin kishiyata, zan nuna mata asalin haka wallahi akan son ka sai na illata yarinya"
Murmushi Abbi yai yana faɗin "Ashe? Ita karuwa ba mutum bace? And don Allah ki daina kiran matar da zan aura da karuwa kuma aure babu fashi duk abin da ki kai niyya Bisimillah ki aikata ban hanaki ba Na'ima, amma ki sani a wannan karan idanuna akan ki suke ba kamar baya ba, kuma baki isa kin yaudareni ba" zubewa tai a wajan tana sakin kuka ta ce "Wallahi Khamal ina son ka, ba zan iya jure ganinka da wata ƴa mace ba, kada ka hutani ta hanyar kishiya don Allah" "look Na'ima, idan hukuntaki zan yi da tuni nayi, aure ra'ayina ne ba sbd ke zan ba, don haka bana son wata fitina please" miƙewa tai idanunta cike da hawaye ta ce "Ok fine idan ba danni zakai ba, ai ka faɗa mini zakai aure na shirya? Ko yanzu ma ba kai ka faɗa mini ba a wajan ƴan uwanka na gani, zan bar maka gidan ka kawo Shegiyar karuwar taci gaba da zama a gidan" tana faɗin hakan ta saka hannu tare da ɗaukan Aishatul-humaira zata fita ya ce "Dawo ki Ajjiye mini Aishatul-humaira, Salima za taci gaba da kulawa da ita" cikin ɗaga murya ta ce "Wallahi babu tsinanniyyar da zan bawa Aishatul-humaira balle ta cutar mini da ita, kuma ni da Aishatul-humaira butu karaba" fuuuu tai waje tana zuwa ta ɗauki mayafi ta goya Aishatul-humaira tare da yin waje.
Abdullah dake zaune saman Kujera idanunsa akan Ummi ya ce "Bana son ganinki cikin damuwa Ummi" Murmushi Ummi tai ta ce "Gajiyar azumin da nake ne Abdullah, ba damuwa nai ba, burina daman an rufe Companyn kuma an rufe Alhaji ya ce mini yana hanya, munyi waya da Shuwa itama ta ce tana hanya" Murmushi mai kyau Abdullah yai cikin nutsuwa da kamalarsa ya ce "Shikenan Ummi, kici gaba da kulawa bana son komai ya sameki" hararar wasa tai masa ta ce "Uhm sannu Audu, bayan kai na lura kana cikin damuwa amma u can't sharing with me" shafa kai kawai yai cike da kunya ba tare da ya ce komai ba. Ummi ta miƙe tana ɗaukan plate ɗin Apple ta ce "Ina son a turawa gidan marayun nan kuɗin da suka buƙata na taimako kamar 2.3m ne ko?" Abdullahi ya ce "Sure Ummi za a tura kije ki kwanta ki huta yanzu don Allah" dungure masa kai tayi ta ce "Wallahi ka nemo matar aure kafin na fita na nemaka da kai na tuzurun kawai" kunnensa ya riƙe da hannu bibbiyu ya ce "Afuwa Ummi am still searching" dry tai tana faɗin "Keep searching har network ya samu, wallahi ka kiyayeni Abdullah" ta faɗi hakan tana shigewa part ɗin ta. Fararen idanunsa ya rufe yana sauke numfashi ina zai ganta? Mene ya sa bashi da Sa'a a duk sanda zai ganta ne? Babu inda bai duba iya inda yake tunanin zai ganta a Dubai amma babu ita. A fili ya ce "Me ya sa kika tsaya mini arai ne?"...
" 'Yar Baba mai sunan larabawa, kwanciyar ta isa haka, ki tashi ki je gangare ki karɓo mini gyaɗar nan"
Wadda aka kira da 'yar Baba ta tura baki, ta ce "Ni wallahi ba ni da lafiya ki aiki Yaya Musa"
"Ai na san baki da lafiyar, dan ki ji daÉ—in jikinki ne, kwanciyar ta isa haka" tana yamutsa fuska haka ta tashi daga kwanciyar, ta fita tsakar gida ta É—ebi ruwa a bokiti ta shiga wanka.
Maimakon da ta fito daga banÉ—akin ta saka kaya, kawai sai ta bemi wuri ta kwanta tana kuka.
"Wai ke meye haka ne? Wane irin sakarci ne haka?".
Ƙara sautin kukan ta yi tana faɗin "Wayyo Allah Babana, Allah ya jiƙanka Baba"
Matar ta ƙarasa gaban matashiyar yarinyar, ta shiga share mata hawayen fuskarta tana faɗin "Kiyi haƙuri 'yar Baba, muma duk zaman jiranta muke yi, kuma ba a yiwa mamaci kuka, ki daina addu'a zaki yi masa" da ƙyar ta rarrasheta ta yi shiru, ta saka kayanta, ta ɗauki wani ƙaton farantin silba, ta fice daga gidan.
Sannu a hankali yake tuƙin, yana ratsa 'yar siriyar hanyar da ke tsakanin gonaki, sam hanyar ba ta da kyau, duk uban kwazazzabai, ga ƙura, yana yi yana duba kwatancen wurin a wayarsa. Kamar yadda aka tsara idan yaje garin, zsi sauka a gidan maigari ne, amma hanya na neman ta ƙwace masa.
Tana tafe tana zancen zuci, da tunani daban daban a ranta, lokaci lokaci tana share hawaye da gefen ɗan ƙaramin mayafin da ta yafa a kafaɗarta, tayi tafiya mai nisa sosai sannan ta isa gidan da aka aiketa.
Wani matashi ne ya washe korayen haƙoransa da ya ganota " 'yar Baba kin fi zinare, sarauniyar kyawawan garin nan, farin wata sha kallo, ke ɗaya kin fi duk matan karkarar nan, daga ina haka?".
"Daga gidan ubanka" ta bashi amsa kai tsaye, tana watsa masa wani irin mugun kallo da idanuwanta da suka ƙanƙance suka yi jawur, saboda kuka.
BuÉ—e baki yayi ya ce "Ni kike zagi?"
"An zage ka É—in, idan ka kuma shiga sabgata, ba zagi ba marinka zan yi, mutumin banza kawai".
"Zaki gane kuskuren ki, zaki san ni kika zaga, ai mai goya miki baya kina iskanci a garin nan, ya mutu ba zamu ƙara ɗaga miki ƙafa ba".
"In kun sake ɗaga mini ƙafa, Allah ya tsine muku" ta ƙarasa Maganar ta wuce shi ta shiga gidan da aka aiketa.
Da an saba idan aka aiketa gidan, ai ta hira ana wasa ana dariya, amma ganin yadda ta shigo ranta a haɗe, ba wanda ta gaisar daga sallama sai miƙa farantin gyaɗa, ya sa ba wanda ya kulata suka bata saƙon gyaɗarta ta fito.
Tafe take tana tunani, a kan abinda yafi komai ci mata tuwo a ƙwarya tsawon rayuwarta, ga rashin Babanta maganin kukanta.
Wani uban ihu ta saki, ta faɗi ƙasa farantin gyaɗar ya faɗi, gyaɗar ta zube a wurin, ta sa hannayenta biyu ta ɗora a kanta. Sam ba ta san ta hawo hanya haka ba, saboda tunanin da take yi.
Cikin tashin hankali Adnan ya fito daga motar, ganin babu abin da ya sameta amma ta ɗora hannun a kanta ta rintse ido, duk ta firgice ya sanya shi harzuƙa, ya kalli bayanta da ta juya, fari tas ga gashinta ta tufke amma ya fito ta ƙasan ɗankwalin ya kwanta a bayanta.
"Mahaukaciyar ina ce ke, zaki hawo kan hanya haka ina miki horn, amma ki ka yi banza? Wace irin mara hankali ce ke?".
"Kar ka sake ce mini mara hankali, kai ne mara hankalin ai, Yanzu da na mutu..... Kasa ƙarasa Maganar ta yi, ganin mutumin da yake tsae a kanta, sankacecen ingarman namiji, fuskarsa a ɗaure babu walwala, ko da idanunsu suka sarƙe a na juna, take ta ga ya sake ware idanuna a kanta.
"A..Ab....Abra..My Angel you are still alive, dama na gaya musu ba ki mutu ba, dama nan ki ka taho ki ka ɓuya?"
Zazzare ido ta shiga yi tana kallonsa, ita dai bata taɓa ganin sa ba, ko mai kama da shi a ƙauyen nan babu, ga kayan jikinsa masu kyau balle ta ce ko mahaukaci ne.
"Abrana ki yi magana mana, Angel ashe baki mutu ba" ya ƙarasa Maganar tare da miƙa hannunsa zai ɗagota!!!
Ki biya mu haƙƙinmu kan ki karanta, na kuɗi ne ₦300 kacal.
"Ina son barin ƙasar ne daman, sabida na samu peace of mind amma zan bar komai naje ƙauyen da kai ne a can na samu nutsuwar zuciyar ka amince kawai, ba ruwana da girman aikin da nayi" I.g ya daɗe yana jinjina al'amarin, ta ya ya Sp da kansa zai je bincike? Amma kuma zuwan Sp ɗin shi ne daidai domin ya san me yake. "shikenan All the best yaushe zaka tafin?"
Sp na Miƙewa tsaye ya ce "Gobe" Sallama sukai Sp Adnan Aliyu Matawalle ya koma gida yana zuwa ya samu Usman da Fayyad a can gidan suna zaman jiransa.
Abbi na zaune hannunsa riƙe da Aishatul-humaira yana mata wasa, ta kafesa da fararen idanunsa duk idan yai da fuskarsa tana biye da ita dai na wasan zata saka kuka tana harba ƙafa, yana ci-gaba kuma zata kafesa da idanu wani lokacin har dariya take masa. Kamar daga sama yaga Mami ta faɗo cikin ɗakin nasa tana huci kamar zakayya. Kallonta kawai yake ba tare da ya ce komai ba. "Ni zaka ci amana kayi mini kishiya ba tare dana sani ba Khamal? Ban cancanci haka daga gareka ba, me na aikata maka har haka da zafi?" Kwantar da Aishatul-humaira yai yana gyara zama ya ce "Ba kiyi mini komai ba Na'ima, kawai naji ina son ƙara auren ne saboda Ubangiji ya bani dama kuma ya hure mini arziƙin da zan haka daga ɗaya har zuwa huɗu" cikin raunin murya Mami ta ce "Me na yi maka to? Ka rasa wacce zaka aura sai wannan Shegiyar karuwar? Wallahi idan ina gidan nan babu Shegiyar data isa ta shigo gidan nan a matsayin kishiyata, zan nuna mata asalin haka wallahi akan son ka sai na illata yarinya"
Murmushi Abbi yai yana faɗin "Ashe? Ita karuwa ba mutum bace? And don Allah ki daina kiran matar da zan aura da karuwa kuma aure babu fashi duk abin da ki kai niyya Bisimillah ki aikata ban hanaki ba Na'ima, amma ki sani a wannan karan idanuna akan ki suke ba kamar baya ba, kuma baki isa kin yaudareni ba" zubewa tai a wajan tana sakin kuka ta ce "Wallahi Khamal ina son ka, ba zan iya jure ganinka da wata ƴa mace ba, kada ka hutani ta hanyar kishiya don Allah" "look Na'ima, idan hukuntaki zan yi da tuni nayi, aure ra'ayina ne ba sbd ke zan ba, don haka bana son wata fitina please" miƙewa tai idanunta cike da hawaye ta ce "Ok fine idan ba danni zakai ba, ai ka faɗa mini zakai aure na shirya? Ko yanzu ma ba kai ka faɗa mini ba a wajan ƴan uwanka na gani, zan bar maka gidan ka kawo Shegiyar karuwar taci gaba da zama a gidan" tana faɗin hakan ta saka hannu tare da ɗaukan Aishatul-humaira zata fita ya ce "Dawo ki Ajjiye mini Aishatul-humaira, Salima za taci gaba da kulawa da ita" cikin ɗaga murya ta ce "Wallahi babu tsinanniyyar da zan bawa Aishatul-humaira balle ta cutar mini da ita, kuma ni da Aishatul-humaira butu karaba" fuuuu tai waje tana zuwa ta ɗauki mayafi ta goya Aishatul-humaira tare da yin waje.
Abdullah dake zaune saman Kujera idanunsa akan Ummi ya ce "Bana son ganinki cikin damuwa Ummi" Murmushi Ummi tai ta ce "Gajiyar azumin da nake ne Abdullah, ba damuwa nai ba, burina daman an rufe Companyn kuma an rufe Alhaji ya ce mini yana hanya, munyi waya da Shuwa itama ta ce tana hanya" Murmushi mai kyau Abdullah yai cikin nutsuwa da kamalarsa ya ce "Shikenan Ummi, kici gaba da kulawa bana son komai ya sameki" hararar wasa tai masa ta ce "Uhm sannu Audu, bayan kai na lura kana cikin damuwa amma u can't sharing with me" shafa kai kawai yai cike da kunya ba tare da ya ce komai ba. Ummi ta miƙe tana ɗaukan plate ɗin Apple ta ce "Ina son a turawa gidan marayun nan kuɗin da suka buƙata na taimako kamar 2.3m ne ko?" Abdullahi ya ce "Sure Ummi za a tura kije ki kwanta ki huta yanzu don Allah" dungure masa kai tayi ta ce "Wallahi ka nemo matar aure kafin na fita na nemaka da kai na tuzurun kawai" kunnensa ya riƙe da hannu bibbiyu ya ce "Afuwa Ummi am still searching" dry tai tana faɗin "Keep searching har network ya samu, wallahi ka kiyayeni Abdullah" ta faɗi hakan tana shigewa part ɗin ta. Fararen idanunsa ya rufe yana sauke numfashi ina zai ganta? Mene ya sa bashi da Sa'a a duk sanda zai ganta ne? Babu inda bai duba iya inda yake tunanin zai ganta a Dubai amma babu ita. A fili ya ce "Me ya sa kika tsaya mini arai ne?"...
" 'Yar Baba mai sunan larabawa, kwanciyar ta isa haka, ki tashi ki je gangare ki karɓo mini gyaɗar nan"
Wadda aka kira da 'yar Baba ta tura baki, ta ce "Ni wallahi ba ni da lafiya ki aiki Yaya Musa"
"Ai na san baki da lafiyar, dan ki ji daÉ—in jikinki ne, kwanciyar ta isa haka" tana yamutsa fuska haka ta tashi daga kwanciyar, ta fita tsakar gida ta É—ebi ruwa a bokiti ta shiga wanka.
Maimakon da ta fito daga banÉ—akin ta saka kaya, kawai sai ta bemi wuri ta kwanta tana kuka.
"Wai ke meye haka ne? Wane irin sakarci ne haka?".
Ƙara sautin kukan ta yi tana faɗin "Wayyo Allah Babana, Allah ya jiƙanka Baba"
Matar ta ƙarasa gaban matashiyar yarinyar, ta shiga share mata hawayen fuskarta tana faɗin "Kiyi haƙuri 'yar Baba, muma duk zaman jiranta muke yi, kuma ba a yiwa mamaci kuka, ki daina addu'a zaki yi masa" da ƙyar ta rarrasheta ta yi shiru, ta saka kayanta, ta ɗauki wani ƙaton farantin silba, ta fice daga gidan.
Sannu a hankali yake tuƙin, yana ratsa 'yar siriyar hanyar da ke tsakanin gonaki, sam hanyar ba ta da kyau, duk uban kwazazzabai, ga ƙura, yana yi yana duba kwatancen wurin a wayarsa. Kamar yadda aka tsara idan yaje garin, zsi sauka a gidan maigari ne, amma hanya na neman ta ƙwace masa.
Tana tafe tana zancen zuci, da tunani daban daban a ranta, lokaci lokaci tana share hawaye da gefen ɗan ƙaramin mayafin da ta yafa a kafaɗarta, tayi tafiya mai nisa sosai sannan ta isa gidan da aka aiketa.
Wani matashi ne ya washe korayen haƙoransa da ya ganota " 'yar Baba kin fi zinare, sarauniyar kyawawan garin nan, farin wata sha kallo, ke ɗaya kin fi duk matan karkarar nan, daga ina haka?".
"Daga gidan ubanka" ta bashi amsa kai tsaye, tana watsa masa wani irin mugun kallo da idanuwanta da suka ƙanƙance suka yi jawur, saboda kuka.
BuÉ—e baki yayi ya ce "Ni kike zagi?"
"An zage ka É—in, idan ka kuma shiga sabgata, ba zagi ba marinka zan yi, mutumin banza kawai".
"Zaki gane kuskuren ki, zaki san ni kika zaga, ai mai goya miki baya kina iskanci a garin nan, ya mutu ba zamu ƙara ɗaga miki ƙafa ba".
"In kun sake ɗaga mini ƙafa, Allah ya tsine muku" ta ƙarasa Maganar ta wuce shi ta shiga gidan da aka aiketa.
Da an saba idan aka aiketa gidan, ai ta hira ana wasa ana dariya, amma ganin yadda ta shigo ranta a haɗe, ba wanda ta gaisar daga sallama sai miƙa farantin gyaɗa, ya sa ba wanda ya kulata suka bata saƙon gyaɗarta ta fito.
Tafe take tana tunani, a kan abinda yafi komai ci mata tuwo a ƙwarya tsawon rayuwarta, ga rashin Babanta maganin kukanta.
Wani uban ihu ta saki, ta faɗi ƙasa farantin gyaɗar ya faɗi, gyaɗar ta zube a wurin, ta sa hannayenta biyu ta ɗora a kanta. Sam ba ta san ta hawo hanya haka ba, saboda tunanin da take yi.
Cikin tashin hankali Adnan ya fito daga motar, ganin babu abin da ya sameta amma ta ɗora hannun a kanta ta rintse ido, duk ta firgice ya sanya shi harzuƙa, ya kalli bayanta da ta juya, fari tas ga gashinta ta tufke amma ya fito ta ƙasan ɗankwalin ya kwanta a bayanta.
"Mahaukaciyar ina ce ke, zaki hawo kan hanya haka ina miki horn, amma ki ka yi banza? Wace irin mara hankali ce ke?".
"Kar ka sake ce mini mara hankali, kai ne mara hankalin ai, Yanzu da na mutu..... Kasa ƙarasa Maganar ta yi, ganin mutumin da yake tsae a kanta, sankacecen ingarman namiji, fuskarsa a ɗaure babu walwala, ko da idanunsu suka sarƙe a na juna, take ta ga ya sake ware idanuna a kanta.
"A..Ab....Abra..My Angel you are still alive, dama na gaya musu ba ki mutu ba, dama nan ki ka taho ki ka ɓuya?"
Zazzare ido ta shiga yi tana kallonsa, ita dai bata taɓa ganin sa ba, ko mai kama da shi a ƙauyen nan babu, ga kayan jikinsa masu kyau balle ta ce ko mahaukaci ne.
"Abrana ki yi magana mana, Angel ashe baki mutu ba" ya ƙarasa Maganar tare da miƙa hannunsa zai ɗagota!!!
Ki biya mu haƙƙinmu kan ki karanta, na kuɗi ne ₦300 kacal.