← Book details Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 130 OF 145

Sashe 130

Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Buri ya cika bayan fitar da rai da hakan, farincikin da Bulama da Rumaisa suka yi a lokacin Aurensu ba zai misaltu ba. Musamman shi da ya jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, yana son Rumaisa sannan kuma ya san dukiyarta yanzu za ta koma tasa da ta ƴaƴan da za su haifa. Soyayyar da Bulama ya nuna mata a zaman Aurensu ya sa ta ƙara yarda da shi da ƙaunar shi. Bayan ya kammala karatunsa ya shirya don komawa Nigeria, a nan mahaifiyar Rumaisa ta ce ba zai tafi da ita ba, ba za ta yarda yarta ta yi nesa da ita ba. Shi ma ya ce ba zai fasa komawa Nigeria ba, saboda Mahaifiyarsa da ƙanwarsa shi kaɗai suke da shi, suna buƙatar shi a kusa da su. Ba don Rumaisa taso ba ta bar shi ya tafi. Dawowar shi ba jimawa ya fara aiki a wani babban asibiti a nan Adamawa. Bayan wasu watanni ya koma ya ga Rumaisa, a lokacin ta raba dukiyarta biyu ta ba shi rabi, ta ce ya je ya yi duk kasuwancin da yake so a Nigeria ya juya kuɗin. Kusan haukacewa Bulama ya yi saboda tsabar murna da farinciki, ranar ƙaunar da ya nunawa Rumaisa bai taɓa nuna mata kamar ta ba. Bai jima ba ya ƙara dawowa Nigeria, anan ya yi deciding ya buɗe Babban Asibiti nasa na kansa. Bai buɗe a Adamawa ba saboda wani dalili nasa ya buɗe a Kaduna, ya saka masa sunan mahaifinsa GARBA YUSUF BULAMA. A lokacin ya haɗu da Saudat suka fara soyayya. Saudat irin matan nan masu feleƙe da iyayi da son sabgar ƙarya. Farkon haɗuwar su da bulama ba ta zata yana da mata ba sai da ya faɗa mata. Ta ji takaici da baƙincikin fara mallakar wata da ya yi kafin ita, amma haka ta daure suka cigaba da soyayyar su. Sai dai cikin ranta ƙiyayyar Rumaisa ce fal duk da ba ta taɓa ganin ta ba sai dai a hoto. Abin da yake ƙara ƙona mata rai yadda Bulama ya ɓoye wa Rumaisa tarayyar su, ya nuna ba ya son ta sani. Kammala ginin G.Y HOSPITAL AND MATERNITY Ya yi daidai da lokacin bikin SAUDAT da BULAMA, don haka aka sha shagali ba na wasa ba. Auren ya kasance tamkar na cin amana, tunda ba da sanin Rumaisa aka yi ba kuma da dukiyarta. Bayan bikin da wata biyu Bulama ya koma Dubai, a wannan zuwan Rumaisa ta samu ciki, bai jima ba ya dawo Nigeria saboda yana son ya kula da Hospital ɗinsa, sai dai bai sanarwa da Rumaisa ya buɗe asibitin ba.

Watan cikin Rumaisa takwas ta kira Bulama ta ce za ta zo Nigeria ta gaishe da Inna ta zazzaga danginsa su san ta, ta san su. Bulama bai so hakan ba saboda gudun tonuwar asirin Auren Saudat, amma bai nuna mata ba saboda kar ta yi tunanin wani abu, dama tana ta complain akan yana daÉ—ewa yanzu kafin ya je ya gan ta.

Bayan sun gama wayar ya fara haÉ—a kayansa, cikin mamaki Saudat da ta shigo É—akin da yake ta ce masa. "Lafiya kake haÉ—a kaya da sakaliyar yammar nan Doctor?"

"Adamawa zan je."
Ya ba ta amsa a tak'aice

"Adamawa kuma? Shi ne ba ka sanar mini na fara haÉ—a kaya ba ni ma?"

Yana zuge zip ɗin trolley ɗinsa ya ce. "Ba da ke zan tafi ba, Rumaisa ce za ta sauka a ƙasar nan gobe, kin kuma san ba ta san da zamana a Kaduna ba balle aurenki da na yi, don haka dole ya zamana a Adamawa za ta same ni." Cikin takaici ta ce. "Sai yaushe kuma za ka dawo?"

"Sai ranar da ta tafi."

"Asibitinka kuma fa."

"Akwai masu kula shi kamar ina nan ai."

"To amma ni haka zan ta zama ni kaɗai, kana ƙasar ma amma ba za mu haɗu ba har sai ranar da ta tafi?"

Cikin fusata ya ce. "Haba Saudat ya kike so in yi ne? Ke duk watanni da nake yi a gurinki ban je wajenta ba, ba kya gani? Sai yau ɗaya za ki ɗaga mini hankali. Rumaisa tana buƙatar kulawata a halin yanzu sosai fiye da ke, saboda tana ɗauke da juna biyu, don haka ko da ba za ta zo ba ni zan je. And lastly kar ki kuskura ki kira ni ko ki mini text, ni zan na kiran ki da kaina, sai na dawo, zan miki transfer ɗin kuɗi idan na ƙarasa." Ya ƙarashe maganar tare miƙewa ya fita.

Da wani irin kallo ta bi shi cikin bugawar zuciya da tsananin tashin hankali har ya fice. Gwauron numfashi ta sauke tare da furta "Ciki?" Tana gyaɗa kai, lokaci ɗaya ta miƙe kamar wadda aka tsikara ta shiga kaiwa da komowa a cikin ɗakin.

Littafin kuÉ—i ne, ku biya kafin ku karanta. 09047871750
[11/25, 10:36 AM] Abk: Maganar samun cikin Rumaisa ya ɗagawa Saudat hankali, zuciyarta ta fara saƙawa kwakwalwarta mugun tunani. Ta ɓangaren Rumaisa ta samu iyayen Dr lafiya cikin karamci da walwala hakan yasa ta saki jiki har ta ce zatai wasu kwanaki. Tana saura kwana uku tafiyarta naƙuda ta kamata cikin gaggawa suka nufi asibiti tasha baƙar wahala ƙwarai har an fara tunanin za ai mata C.s sai Ubangiji ya sauke ta lafiya ta haifi twins.
Murna ta kama Dr G.Y sai dai murna ta koma ciki domin awanni wajan biyu da haihuwar aka dawo da jariran a hannu Allah ya yi musu rasuwa, daman da aka haife su ba wanda yaga kalar su sai da suka rasu. Haka akai musu suttura ba tare da mahaifiyar su ta gansu ba. Lokacin da Rumaisa ta samu labari kusan hauka ta kusa yi uwa uba akace ba zata sake haihuwa ba Wannan dalilin ya sanya ta saka damuwa a ranta ƙwarai da gaske.

Bayan sati biyu ta tattara ta koma Dubai hakan ya yi wa Bulama daɗi ya ƙara samun damar da zai zauna da Saudat, a lokacin ne kuma labarin rasuwar P.A ɗin Rumaisa ya riskesu ya yi hatsari ya rasu da shi da motar gaba ɗaya suka ƙone ƙurmus.
Bulama ya sanya wa ransa samun dukiyar Rumaisa ko ta halin yaya ne ta zama mallakinsa. Lokacin guda ya shiga amsar kuɗi wajanta da niyyar zai buɗe wasu, kamfanoni wani lokacin yace kuɗin sun gaza wani lokacin ya ce za a ƙaro kaya, wani lokacin ya ce ta bashi rance. Yarda da amincin da tai masa sai ta kalle shi tare da yin murmushi ta ce "Wanne irin rance ya kai Yusuf dukiyata taka ce dani da duk abin dana mallaka naka ne" idan Rumaisa ta faɗi haka sai Dr Bulama ya rungume ta tsam a jikinsa tare da maganganun masu daɗi.

Ganin abubuwa sun fara runcaɓewa Rumaisa ga P.A ɗinta ya rasu ya sanya ta ɗakko Abdullah ƙaninta ta dawo da shi wajanta, tare da ragama wasu gefe na dukiyoyinta yana kulawa dasu ta bashi matsayin sabon P.A
Daga nan ganin Dr Bulama ya ƙara yiwa Rumaisa wahala a cewar shi aiki ne ya yi masa yawa sosai, lokacin kuma tuni Saudat ta samu cikin Meenal farin ciki wajan Bulama ba a magana, ya tattara ya manta da batun ya taɓa haihuwar yara bai kuma damu da rashin haihuwar Rumaisa ba.
Da Meenal ta girma ya ƙara himma wajan kwashe dukiyar Rumaisa lokacin Abdullah ya tsaya tsayin daka akan kuɗin da ƙyar suke fita, sbd a kaso goma na dukiyar Rumaisa bai fi kaso huɗu ya rage mata ba. Babban dalilin daya sanya Rumaisa shiga tashin hankalin har ta saka aka rufe sabon companyn data buɗe. Wannan kenan.

Waje ya yi shiru cikin kuka Rumaisa ta ce "Wace kuma Meenal daga ina aka sameta shin itama yarinya ta ce?" Dr Bulama ya kasa cewa komai zufa na yanko masa sosai. A hankali Adnan ya sauke numfashi yana ƙara rungume Little a jikinsa ya ce.
"Ƴar ce wacce matar shi ta haifa masa"

"Ƴa tare da wata matar Yusuf? Da gaske ne abin da ake faɗa Ya kai Yusuf kada kayi mini ƙarya na amince da kai"
Gaba ɗaya mutanan parlourn suka zuba wa Ummi idanu cike da tausayawa ya aka ƙare da kishiyar daka sani ma balle wacce akai a bayan idanun ka, uwa uba auren cin amana anyi mata kishiya da kuɗin ta.

Cikin gunjin kuka sosai Ummi ta ce "Yusuf ka cuce ni kaci amanata, kaci amanar yarda da amincin da nayi maka na tsayin shekara da shekaru, kayi aure da dukiyata without knowing everyone Wallahi Wallahi Allah.....,"

Da sauri Abba ya ce "A'a Hajiya Rumaisa kada ayi haka, kiyi haƙuri don Allah ai ba a tabbatar auren ya yi ba" ya juya kan Adnan yana nuna shi da hannu ya ce.
"Kai kuma kada na sake jin bakinka manya na magana"

"I'm sorry Abba"
Abba ya watsa masa harara ya ce "sorry for yourself Adnan Aliyu Matawalle" Adnan yai shiru.
Abbi ya sauke numfashi yana mamakin rayuwa yadda bata da tabbas É—in nan cikin nutsuwa ya ce.
"Yanzu Dr da gaske dai kana da wata mata bayan Rumaisa?" kan Dr a ƙasa ya ce. "Gaskiya ne ina da mata Saudat na aureta ba tare da sanin Rumaisa ba, amma ita Saudat ta san da zaman Rumaisa ina da yarinyar Meenal ita ce wacce nake cewa wani ma'aikacina bashi da lafiya"
Ya juya gaba ɗaya zai magana Ummi ta girgiza kai tana ɗaga masa hannu alamar bata buƙatar jin komai. "Ina yarinyar tawa? Kuyi haƙuri na kasa jurewa"

Murmushi kawai Abbi ya yi ya shiga faɗin "Daughter, Afra... Come here your parents are here" da gudu Afra ta fito daga cikin ɗaki kamar me jira. Tana fitowa Ummi ta miƙe tsaye hawaye na zuba daga cikin idanunta ta warewa Afra hannu muryar ta na rawa ta ce.
Chapter 130 · 0% Book details