Sashe 68
Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da sauri Adnan ya ciro hanky yana share mata ya ce "dan Allah kar ki ɓata mana Wannan Farincikin, ba kowane buri namu ne yake zuwa ya cika a yadda muke so ba, kiyi haƙuri" haka ya rarrasheta, aka kammala event ɗin wannan ranar.
Daren ranar, haka Adnan ya kasance da ita a waya, yana cigba da aikin rarrashi.
Zuba mata idanunsa yayi yana kallonta, yadda take maye, cike da rashin Sabo, sai tamɓele take ya sakata a gaba kawai yana murmushi, yana zuƙar shisha yana fesar da hayaƙin a cikin iska.
Ganin tana ƙoƙarin faɗuwa ne ya sanya shi tashi da sauri ya riƙota yana murmushi "Sweetheart, it seems like you are enjoying the moment" yayi Maganar tare da kissing ɗin goshinta.
Kan makeken gadon dake tsakiyar É—akin ya kaita, ya kwantar da ita, yana shafa dogon gashinta. Gaba É—aya Meenal ba ta hayyacinta, ba ta tashi farkawa daga mayen da take yi ba, sai bayan magariba.
A hankali ta buÉ—e idanunta ta kalli in da ya idar da salla, ta tashi da sauri ta kalli agogo, a gigice ta ce "Ya a kai na kai wannan lokacin? Me ka bani haka na sha?".
"Calm down Baby, kayan caji ne fa kawai"
"Kamar yaya kayan caji, lokacin komawata gida tuni ya ƙure, me zanje in ce a gida?"
"Haba ke kuwa, kamar ba babbar yarinya ba, da alama fa kin ji daÉ—in cajin nan da kika yi"
Wani gululun baƙin ciki ne ya cunkushe mata zuciya, a gurguje ta tattara kayanta da mukullin motarta, tai waje.
Gudu take tamkar zata tashi sama, saboda tsananin tashin hankali, cike da fargaba da zullumi ta shiga cikin gidan, a Falo ta tarar da Mummy tana kaiwa tana komowa, tana ganin Meenal a rikice ta ce "Ke daga gidan ubanwa kike Yanzu?".
"Amm...mm..... Mummy da..dama".
"Dama me? Gidan ubanwa kika tafi? Ƙarfe nawa yanzu? Kin sanya ya tayar mini da hankali, yanzu haka ya tafi kai report gurin hukuma, akan cewar kin ɓata, ina ki ka je?".
Kan Meenal ta bata amsa, sai ga Doctor Bulama ya shigo, yana ganin Meenal rai a ɓace ya ce "Ke! Daga ina kike?"
"Ba ko ina".
"Daga ina kike?!" Ya sake tambayar cikin tsawa.
Rawar baki ta fara yi, amma ta kasa Magana, aikuwa yayi kanta ya shaƙota yana zazzare ido tare da maimaita tambayar daga ina take?"
"Haba doctor,ka bita a hankali mana, idan ka illata ta fa, ko ka manta uta kaÉ—aice da mu?".
"Dan ita kaÉ—aice da mu ba shi ya bata lasisin yin iskancin da ta ga dama ba, gidan wa kika je?".
A shaƙe Meenal ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haƙuri, ƙawata na bi gidansu, muka tafi gurin biki daga school".
"Meyasa baki kira kin gaya mini ba, aka dinga kiran wayarki amma a kashe?".
"Nayi kuskure, amma dan Allah kayi haƙuri kar ka kasheni" da Doctor ya ƙyale Meenal, bayan ta sha shaƙar da sai da ta kusa zuwa lahira.
Hall ya haɗu iya haɗuwa, Abra ta haɗe cikin wani danƙareren Material, kai da gani ka san ba duk jiki ba, sai jikin 'yar gata.
Adnan kuwa gaba ɗaya kishi ne ya mamaye masa zuciya, yadda kowa ke ɗaukar hoton matarsa a waya, shifa wannan taron bidi'ar dan anfi ƙarfinsa ne, amma da babu dalilin da zai sanya ayi wannan taron ana kallon matarsa.
MC ne ya kira Amarya, tare da umartar ta da taje ta taho da mamanta.
Cikin takun Abra na nutsuwa, taje gaban table ɗin da Hajiya Na'ima take, ta durƙusa ta kamo hannunta zuwa filin rawa.
MC ya ce "Ki kalli Mamanki, ki ce nata kin gode, kuma kina sonta"
Abra ta kama hannun Hajiya Na'ima, ta kalli idonta murya na rawa ta ce "Thank you very much Mamina, for all you did for me Bani da Abun da zance miki sai Allah ya baki Aljanna maɗaukaiya, and I love You Mamina" ta ƙarasa Maganar tana rungume Na'ima, tare da sakin wani irin kuka mai ban tausayi.
Nan dj ya saki waƙar Wayyo Allah mamana, Na'ima ma rungume Abran ta yi tana ɗan dukan bayanta alamar rarrashi. Yayin da ta ɓalle bakin jaka, ta dinga zubawa Abra kuɗi kamar ba gobe, ji take dama Abra 'yar ta ce ta halak, da shagalin da za tayi a bikin nan yafi haka.
Haka aka yi Dinner, 'yan uwa da abokan arziki, duk sun yi bajinta, ta hanyar liƙi da bada gudunmawa.
Abbi tuni ya sauka garin Kano tare da tasa tawagar, kasancewar bayan É—aurin Aure akwai reception na mussaman, da kuma parrate na sojoji, abunka da masu abu da abunsu.
A can birnin Sin kuwa, Salman ne zaune a wani katafaren ɗaki, a gaban madubi ya sanya hoton Abra a gaba, ya ƙura masa idanu, idan lissafinsa daidai ne, yau ne ake ɗaurawa Abra Aure, Abran da ya ƙallafa a rai, ya taso ya rayu da soyayyarta, a yau ta zama mallakin wani ba shi ba, ina ma Mami ba ta sanar masa Abra ba 'yar uwassa ba ce ta jini, da duk wannan al'amuran basu faru ba, gaba ɗaya tun da ya zo China ba ya jin daɗin garin, komai nasu daban kamar ba Normal Mutane ba, gashi ko turancin ma ba kowane ya iya ba a cikinsu, dan haka abubuwa suna masa wahala, duk da wai kafin su fara lectures, sai sunyi wata shida ana koya musu Yaren Chinese.
An ɗaura Auren Adnan da Abra, wanda dubban mutane suka sheda hakan, ɗaurin Auren da ya samu halartar manyan ƙasa daga ɓangarori daban-daban ciki har da Captain Faruk da aka tsinto Abra da shi.
Daidai gwargwado an yiwa Abra Nasiha mai ratsa zuciya game da rayuwar Aure, yayin da Granny ta ta Nasihar mai ɓaro_ɓaro ce ba rufi ba kunyar komai.
Da la'asar aka shirya Abra cikin wata dakakkiyar rantsatsiyar lafaya, Mami ta kaita gurin Abbi, yayi mata nasiha sosai tare da Adduoi da fatan shiga É—akin miji a sa'a.
Dangin Adnan sun zo da manyan motoci, domin É—aukar Amarayar su.
Sai dai Abra ta ƙanƙame Mami tana kuka, karo na farko a rayuwar Na'ima, tun da ta fara riƙon Abra, taji jikinta yayi sanyi, dan tun a gurin Dinner jiya Abran ta sa jikin Na'ima yin sanyi.
Abra ta ƙanƙame Na'ima tana faɗin "Mamina, a zaman mu idan na yi miki laifi ki yafe mini, Mami bana son barinki".
Anty Suwaiba ce cikin masifa ta ce "Wai ke bayinki ne mutanen da suka tsaya suna jiran ki, dalla ki fito ki wuce mu tafi"
A hankali Na'ima ta shafa bayan Abra ta ce "Na yafe miki Abra, Allah ya baku zaman lafiya, muje in rakaki bakin Mota".
"Mami to ke yaushe zaki zo?".
"Very soon" daga haka ta ja hannun Abra zuwa bakin mota. Da ƙyar Abra ta yadda ta shiga, tana kuka tana ɗagawa Mami hannu.
Anty Suwaiba ta ce "Ke Na'ima, wai me kike yi hakane kamar kin damu da tafiyar yarinyar nan? Allah ya raba ki da ƙwallon mangwaro kin huta da ƙuda, amma naga kamar kina cikin damuwa? Wai ni fa kamar ƙwalla nake gani a idanun ki".
Jiki a sanyaye Na'ima ta ce "Gaskiyar Husawa da suka ce, 'Sabo turken wawa' a zamana da yarinyar nan ban taɓa jin abunda na ji ba jiya da ta kalli idanuna tana mini Addu'a tare da jaddada soyayyarta a gareni, idanunta ɗauke da zallar soyayyar uwa da ɗa, duk da kwashe shekarun da nayi ina azabtar da ita, amma tana mini biyayya fiye da yadda ɗan da na durƙusa na haifa yake mini, ko ba komai da ina ganin gilmawar ta da ta Salman, amma Yanzu shi ya tafi, ita ma kuma haka".
"To shine me? Ke ba hutunki bane bama, ta je can ta ƙarata Allah ya tsare miki mijinki da ɗan ki".
Na'ima ta ce "Hakane, dama babban fatana kenan, ta bar mini gida, shekarun da mukayi Allah ya amfana, kawai dai kin san zuciya".
"Ke dalla can manta da ita".
Awanni uku cif, da magariba su Abra suka isa garin Kaduna, aka fara kaita gidan su Adnan, aka yi mata nasiha, suka bata kyaututtuka, sannan suka wuce da ita gidanta.
Tubarkallah Adnan ya ƙera mata gida na gani na faɗa, Abbi kuma da Hajiya Na'ima sun cika gidan da kaya na kerewa sa'a, Masha Allah gida yayi komai tsaf.
Wanda suka rako Abra daga Kano, suka koma gidansu Adnan su kwana a can, daga nan su koma Kano, Abra ji tayi Kamar ta tashi ta bisu, haka suka watse suka bar Abra.
Abra ta zauna jiran shigowar Ango, sai dai har ƙarfe goma sha ɗaya ba ango ba dalilinsa, tun Abra na jira har ta fara gajiya, tsoro ya fara kamata, ta takure a ƙuryar gado, gaba ɗaya tsoro ya baibayeta.
Abu kamar wasa har ƙarfe biyu na dare, Adnan be shigo ba, ta ɗauko wayarta domin ta kirashi amma wayarta ta ɗauke babu caji.
Rashin sanin abun yi ya sanya ta fara kuka.
Haka Abra ta kwana a zaune, sai É—an gyangyaÉ—i da ta dinga yi daga zaune a haka har Asuba tayi.
A tsorace ta lallaɓa ta shiga banɗakin da ke cikin ɗakin tayi alwala, ta gabatar da sallar Asubahi, ta koma gefe ta takure.
Daren ranar, haka Adnan ya kasance da ita a waya, yana cigba da aikin rarrashi.
Zuba mata idanunsa yayi yana kallonta, yadda take maye, cike da rashin Sabo, sai tamɓele take ya sakata a gaba kawai yana murmushi, yana zuƙar shisha yana fesar da hayaƙin a cikin iska.
Ganin tana ƙoƙarin faɗuwa ne ya sanya shi tashi da sauri ya riƙota yana murmushi "Sweetheart, it seems like you are enjoying the moment" yayi Maganar tare da kissing ɗin goshinta.
Kan makeken gadon dake tsakiyar É—akin ya kaita, ya kwantar da ita, yana shafa dogon gashinta. Gaba É—aya Meenal ba ta hayyacinta, ba ta tashi farkawa daga mayen da take yi ba, sai bayan magariba.
A hankali ta buÉ—e idanunta ta kalli in da ya idar da salla, ta tashi da sauri ta kalli agogo, a gigice ta ce "Ya a kai na kai wannan lokacin? Me ka bani haka na sha?".
"Calm down Baby, kayan caji ne fa kawai"
"Kamar yaya kayan caji, lokacin komawata gida tuni ya ƙure, me zanje in ce a gida?"
"Haba ke kuwa, kamar ba babbar yarinya ba, da alama fa kin ji daÉ—in cajin nan da kika yi"
Wani gululun baƙin ciki ne ya cunkushe mata zuciya, a gurguje ta tattara kayanta da mukullin motarta, tai waje.
Gudu take tamkar zata tashi sama, saboda tsananin tashin hankali, cike da fargaba da zullumi ta shiga cikin gidan, a Falo ta tarar da Mummy tana kaiwa tana komowa, tana ganin Meenal a rikice ta ce "Ke daga gidan ubanwa kike Yanzu?".
"Amm...mm..... Mummy da..dama".
"Dama me? Gidan ubanwa kika tafi? Ƙarfe nawa yanzu? Kin sanya ya tayar mini da hankali, yanzu haka ya tafi kai report gurin hukuma, akan cewar kin ɓata, ina ki ka je?".
Kan Meenal ta bata amsa, sai ga Doctor Bulama ya shigo, yana ganin Meenal rai a ɓace ya ce "Ke! Daga ina kike?"
"Ba ko ina".
"Daga ina kike?!" Ya sake tambayar cikin tsawa.
Rawar baki ta fara yi, amma ta kasa Magana, aikuwa yayi kanta ya shaƙota yana zazzare ido tare da maimaita tambayar daga ina take?"
"Haba doctor,ka bita a hankali mana, idan ka illata ta fa, ko ka manta uta kaÉ—aice da mu?".
"Dan ita kaÉ—aice da mu ba shi ya bata lasisin yin iskancin da ta ga dama ba, gidan wa kika je?".
A shaƙe Meenal ta ce "Dan Allah Daddy ka yi haƙuri, ƙawata na bi gidansu, muka tafi gurin biki daga school".
"Meyasa baki kira kin gaya mini ba, aka dinga kiran wayarki amma a kashe?".
"Nayi kuskure, amma dan Allah kayi haƙuri kar ka kasheni" da Doctor ya ƙyale Meenal, bayan ta sha shaƙar da sai da ta kusa zuwa lahira.
Hall ya haɗu iya haɗuwa, Abra ta haɗe cikin wani danƙareren Material, kai da gani ka san ba duk jiki ba, sai jikin 'yar gata.
Adnan kuwa gaba ɗaya kishi ne ya mamaye masa zuciya, yadda kowa ke ɗaukar hoton matarsa a waya, shifa wannan taron bidi'ar dan anfi ƙarfinsa ne, amma da babu dalilin da zai sanya ayi wannan taron ana kallon matarsa.
MC ne ya kira Amarya, tare da umartar ta da taje ta taho da mamanta.
Cikin takun Abra na nutsuwa, taje gaban table ɗin da Hajiya Na'ima take, ta durƙusa ta kamo hannunta zuwa filin rawa.
MC ya ce "Ki kalli Mamanki, ki ce nata kin gode, kuma kina sonta"
Abra ta kama hannun Hajiya Na'ima, ta kalli idonta murya na rawa ta ce "Thank you very much Mamina, for all you did for me Bani da Abun da zance miki sai Allah ya baki Aljanna maɗaukaiya, and I love You Mamina" ta ƙarasa Maganar tana rungume Na'ima, tare da sakin wani irin kuka mai ban tausayi.
Nan dj ya saki waƙar Wayyo Allah mamana, Na'ima ma rungume Abran ta yi tana ɗan dukan bayanta alamar rarrashi. Yayin da ta ɓalle bakin jaka, ta dinga zubawa Abra kuɗi kamar ba gobe, ji take dama Abra 'yar ta ce ta halak, da shagalin da za tayi a bikin nan yafi haka.
Haka aka yi Dinner, 'yan uwa da abokan arziki, duk sun yi bajinta, ta hanyar liƙi da bada gudunmawa.
Abbi tuni ya sauka garin Kano tare da tasa tawagar, kasancewar bayan É—aurin Aure akwai reception na mussaman, da kuma parrate na sojoji, abunka da masu abu da abunsu.
A can birnin Sin kuwa, Salman ne zaune a wani katafaren ɗaki, a gaban madubi ya sanya hoton Abra a gaba, ya ƙura masa idanu, idan lissafinsa daidai ne, yau ne ake ɗaurawa Abra Aure, Abran da ya ƙallafa a rai, ya taso ya rayu da soyayyarta, a yau ta zama mallakin wani ba shi ba, ina ma Mami ba ta sanar masa Abra ba 'yar uwassa ba ce ta jini, da duk wannan al'amuran basu faru ba, gaba ɗaya tun da ya zo China ba ya jin daɗin garin, komai nasu daban kamar ba Normal Mutane ba, gashi ko turancin ma ba kowane ya iya ba a cikinsu, dan haka abubuwa suna masa wahala, duk da wai kafin su fara lectures, sai sunyi wata shida ana koya musu Yaren Chinese.
An ɗaura Auren Adnan da Abra, wanda dubban mutane suka sheda hakan, ɗaurin Auren da ya samu halartar manyan ƙasa daga ɓangarori daban-daban ciki har da Captain Faruk da aka tsinto Abra da shi.
Daidai gwargwado an yiwa Abra Nasiha mai ratsa zuciya game da rayuwar Aure, yayin da Granny ta ta Nasihar mai ɓaro_ɓaro ce ba rufi ba kunyar komai.
Da la'asar aka shirya Abra cikin wata dakakkiyar rantsatsiyar lafaya, Mami ta kaita gurin Abbi, yayi mata nasiha sosai tare da Adduoi da fatan shiga É—akin miji a sa'a.
Dangin Adnan sun zo da manyan motoci, domin É—aukar Amarayar su.
Sai dai Abra ta ƙanƙame Mami tana kuka, karo na farko a rayuwar Na'ima, tun da ta fara riƙon Abra, taji jikinta yayi sanyi, dan tun a gurin Dinner jiya Abran ta sa jikin Na'ima yin sanyi.
Abra ta ƙanƙame Na'ima tana faɗin "Mamina, a zaman mu idan na yi miki laifi ki yafe mini, Mami bana son barinki".
Anty Suwaiba ce cikin masifa ta ce "Wai ke bayinki ne mutanen da suka tsaya suna jiran ki, dalla ki fito ki wuce mu tafi"
A hankali Na'ima ta shafa bayan Abra ta ce "Na yafe miki Abra, Allah ya baku zaman lafiya, muje in rakaki bakin Mota".
"Mami to ke yaushe zaki zo?".
"Very soon" daga haka ta ja hannun Abra zuwa bakin mota. Da ƙyar Abra ta yadda ta shiga, tana kuka tana ɗagawa Mami hannu.
Anty Suwaiba ta ce "Ke Na'ima, wai me kike yi hakane kamar kin damu da tafiyar yarinyar nan? Allah ya raba ki da ƙwallon mangwaro kin huta da ƙuda, amma naga kamar kina cikin damuwa? Wai ni fa kamar ƙwalla nake gani a idanun ki".
Jiki a sanyaye Na'ima ta ce "Gaskiyar Husawa da suka ce, 'Sabo turken wawa' a zamana da yarinyar nan ban taɓa jin abunda na ji ba jiya da ta kalli idanuna tana mini Addu'a tare da jaddada soyayyarta a gareni, idanunta ɗauke da zallar soyayyar uwa da ɗa, duk da kwashe shekarun da nayi ina azabtar da ita, amma tana mini biyayya fiye da yadda ɗan da na durƙusa na haifa yake mini, ko ba komai da ina ganin gilmawar ta da ta Salman, amma Yanzu shi ya tafi, ita ma kuma haka".
"To shine me? Ke ba hutunki bane bama, ta je can ta ƙarata Allah ya tsare miki mijinki da ɗan ki".
Na'ima ta ce "Hakane, dama babban fatana kenan, ta bar mini gida, shekarun da mukayi Allah ya amfana, kawai dai kin san zuciya".
"Ke dalla can manta da ita".
Awanni uku cif, da magariba su Abra suka isa garin Kaduna, aka fara kaita gidan su Adnan, aka yi mata nasiha, suka bata kyaututtuka, sannan suka wuce da ita gidanta.
Tubarkallah Adnan ya ƙera mata gida na gani na faɗa, Abbi kuma da Hajiya Na'ima sun cika gidan da kaya na kerewa sa'a, Masha Allah gida yayi komai tsaf.
Wanda suka rako Abra daga Kano, suka koma gidansu Adnan su kwana a can, daga nan su koma Kano, Abra ji tayi Kamar ta tashi ta bisu, haka suka watse suka bar Abra.
Abra ta zauna jiran shigowar Ango, sai dai har ƙarfe goma sha ɗaya ba ango ba dalilinsa, tun Abra na jira har ta fara gajiya, tsoro ya fara kamata, ta takure a ƙuryar gado, gaba ɗaya tsoro ya baibayeta.
Abu kamar wasa har ƙarfe biyu na dare, Adnan be shigo ba, ta ɗauko wayarta domin ta kirashi amma wayarta ta ɗauke babu caji.
Rashin sanin abun yi ya sanya ta fara kuka.
Haka Abra ta kwana a zaune, sai É—an gyangyaÉ—i da ta dinga yi daga zaune a haka har Asuba tayi.
A tsorace ta lallaɓa ta shiga banɗakin da ke cikin ɗakin tayi alwala, ta gabatar da sallar Asubahi, ta koma gefe ta takure.