Sashe 114
Dare Da Duhu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Washegari ta kama ranar Alhamis, ranar aka yi kamun amaryar Abbi kamar yadda aka tsara. An sha shagali sosai abin ya ƙayatar duk da ba a yi ƙida ba, manyan malamai mata aka kira suka yi wa'azi mai ratsa zuciya. Amarya ta sha pictures, dangin Abbi sukai ta ɗorawa a status, amma Nai'ma ba ta gani ba. Don ƙwace wayarta Wasila ta yi ta ce ba za ta ga abin da zai ɗaga mata hankali ba, don ta san halinta. Daren yau Na'ima ba ta iya runtsawa ba, kwana ta yi tana kuka tare da tunanin daga gobe Khamal ya zama nasu su biyu, za ta fara sharing ɗinsa da wata.
Rana ba ta ƙarya, yau juma'a ranar ɗaurin Auren Abbi da amaryarsa Salima. Ba ƙaramin Dauriya Nai'ma ta yi ba ta shirya cikin wani tsadadden farin less mai adon red, bi sa takurawar su Wasila. Har gida Hajara ta kira wata mai make up ta zo ta yi mata. Duk da idonta a jeme yake saboda kuka amma ta yi kyau, sai dai ramar ta ta fito sosai. A'isha Humairah ma an mata kwalliya cikin sabbin kaya masu kyau white and red, tana rungume a jikin Nai'ma tana bacci bayan ta ci ta ƙoshi. Ƙawayen Nai'ma da wasu daga cikin danginta sun zo tun safe, don ita ma ranar za ta yi nata taron. A tsarin ta ba za ta yi taron komai ba, amma su Wasila suka dage sai an yi, don ƙin yin taron zai saka mutane su gane halin da take ciki na damuwa a kan auren, hakan zai saka kuma a yi mata dariya ne.
Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana suna zazzaune a bedroom ɗinta ita da su Aunty Suwaiba, ana ta dannar ƙirjinta, masu zuga ta akan ta yi hauka na yi, masu ba ta shawarwari na gari wanda za su amfane ta na yi. Ita dai duk ba fahimtar su take ba, don hankalinta gabaɗaya ba ya jikinta, yanda take jin zuciyarta kamar ta tashi tay ta zunduma ihu, ganin abun take tamkar a mafarki, wai yau ita za a yiwa kishiya? Ita da ta gama cika baki a cikin ƙawaye da dangi akan Khamal ba zai taɓa ƙara aure ba, amma ya watsa mata ƙasa a ido. A haka Abbi ya shigo ya same su cikin shirin shi na tafiya gurin ɗaurin Aure, ya fito tsaf a angon shi, ba za ka taɓa cewa ya ajiye ɗa kamar Salman ba. Bayan sun gaisa da mutanen ɗakin sai suka tashi suka fice don ba su guri.
A hankali ta ɗago kanta dake sunkuye ta zuba masa ido, tunda ya shigo ta ji sallamar shi gami da ƙamshinsa da ya cika ɗakin ta sunkuyar da kanta, ya yi matuƙar yi mata kyau ba kaɗan ba, farar shaddar jikinsa ba ƙaramin haska shi ta yi ba. Shi ma kallon ta yake yi cikin wani irin yanayi hakan ya sa idanunsu suka sarƙe cikin na juna, ranar da ya fara ganin ta a rayuwarsa ya tuno, ya sani Nai'ma tana son shi ba kaɗan ba, shi ma kuma yana son ta, matsalar ta kawai zafin kishi.
Ganin yadda ta rame sai ya ji tausayin ta mai ɗimbin yawa ya cika masa zuciya, a hankali ya taka ya ƙarasa ya tsugunna a gabanta tare da ɗora hannunsa a kan nata dake kan cikakkiyar sumar kan A'isha Humairah.
"Wifey."
Ya kira sunanta cikin wata irin murya. Duk yadda ta so daurewa kasawa ta yi ta fashe da kuka, cikin kukan ta ce. "Da gaske Khamal kishiya za ka yo mini? Ni ce fa Na'iman ka uwar Ƴaƴanka, me na yi maka ka zaɓi hukunta ni da abin da zuciyata ba za ta dauka ba, ka san ba zan juri ganin ka tare da wata ba.
"Babu abin da kika mini Na'ima." Ya yi maganar yana ɗauke A'isha daga kan cinyarta ya kwantar da ita a gefe. Cikin ƙauna da kulawa ya rungume ta tare da faɗin. "I'm sorry, Ina son ki sosai matata, kuma duk wata mace da zan so a bayan ki take." Rarrashin ta ya yi sosai da daddaɗan kalamai har ya samu ta yi shiru, bai bar ɗakin ba sai da ya tabbatar ya sanyaya mata rai, ya yi musu pictures a wayarsa tare da A'isha Humairah, yana fita ta ƙara fashewa da kuka, a haka su Hajira suka dawo suka same ta.
"Mene haka? Kukan na mene kuma? Sai kin ɓata kwalliyar? Haba Nai'ma sai ka ce wata yarinya, jama'a sun fara taruwa ke kuma kina nan kina kuka? Haka za a kawo amaryar kina wannan sakarcin? To wallahi idan ba kya danne kishin ki za ta samu lagon ki tana ƙunsa miki baƙin ciki, ki je ki yi tunda ke ba kya jin magana."
"To ni Aunty Wasila ya kuke so in yi? Ko don ba ku san me nake ji ba ne a cikin raina?"
Ganin yadda take kuka kamar za ta shiɗe sai suka shiga lallaɓa ta, har ta haƙura ta yi shiru ta shiga hada-hada da jama'a. Biki ya ƙayatar sosai, Nai'ma ta saki ranta ana ta hidima da ita, duk da ba ƙaramin dauriya take ba, don ji take tamkar ana rura mata garwashin wuta a cikin zuciyarta. Bayan Magriba aka kawo amarya, kafin ƙarfe tara kowa ya tafi, gidan ya rage daga Na'ima da Humairah sai amarya a part ɗinta, sai mai gadi da sauran masu aiki dake waje. Na'ima tana zaune tana ta trying numbern Salman amma ta ƙi tafiya Abbi ya shigo gidan. Part ɗinta ya zarce direct ya ajiye mata yoghurt da kazar ta, sannan ya sanar mata yana son ganin su a main parlour. Ba ta yi musu ba ta ce masa ga ta nan zuwa. Sai da ta kwantar da A'isha Humairah a cikin net ɗinta sannan ta yafa mayafi ta fita. Shigar ta parlour'n ya yi daidai da ɗago kai da amarya ta yi tana gyara mayafin jikinta. Turus Nai'ma ta ja ta tsaya cikin tsananin ƙaduwa da mamaki, lokaci ɗaya gabanta ya yi mummunar faɗuwa, sakamakon tozali da fuskar amaryar.
Littafin kuɗi ne, don neman ƙarin bayani ku tuntuɓe mu a wannan lambar. 09047871750
[11/9, 8:06 PM] Abk: Da mamaki Na'ima ta din ga bin amaryar Abbi da kallo,dan abin da take gani ya saɓa zatonta, a tunaninta zata ga Salima, tsinanniyyar karuwar data maƙalewa mijinta Khamal Khamis. Matar data tsani jin ko sunanta balle kuma ta yi tozali da mummunar fuskarta wacce take ƙara harzuƙa Mami. Amma sai taga akasin haka dan kuwa wannan Salimar baƙa ce sannan yarinya ce ɗaya shakaf.
Danne mamakinta ta yi tare da ƙarasowa ta nemi kujera can gefe da su ta zauna ba tare da tace musu komai ba.
Gyara zama Abbi ya yi, yana ƙarewa matan nasa kallo cike da Soyayyar ko wacce a zuciyarsa,sai dai son wata ya rinjayi na wata. Sauke numfashi ya yi kafin yai gyaran murya yana kallonsu duka, a hankali ya fara magana yana ɗan satan kallon Na'ima da yaga ta sunkuyar da kanta tana kallon ƙasa,kwata-kwata taƙi kallon inda yake zaune bare kuma amarya tasa Salima.
Nasiha ya yi musu sosai akan yadda zasu zauna da juna lafiya, su mutunta juna sannan ya juya ga Salima yana faÉ—in.
"Salima ga yayarki nan, bana so ki ɗauke ta a matsayin kishiyarki ina so ki ɗauke ta a matsayin ƴar uwarki,wanda zaki iya tunkarar ta idan abu ya shige miki duhu, sannan ina so in sake jaddada miki ban aureki dan bana son Na'ima ba, ina son matata, bata taɓa nuna gazawa akan kulani da kuma iyalina ba, kada ki sawa ranki cewa don bana son matata na aureki ba, na aureki me sbd Ubangiji ya bani damar hakan. Allah ya ƙaddara ni acikin mutanen da zasu ƙara aure sannan su zauna da mata sama da ɗaya, saboda haka ina so ki girmamata ki mutunta ki bata girmanta a matsayinta na wacce take gaba da ke"
Ita dai Na'ima har lokacin kanta a sunkuye yake tana yaƙi da hawayen dake son zubowa kan fuskarta amma taƙi bashi daman hakan, cikin kulawa Abbi ya juyo ga Na'ima ya ce.
"Uwargida sarautar mata, Mrs Khamal ga ƙanwarki nan na kawo miki ita, please Na'ima bana so ki ɗauke ta less than a sister, ki gyara mata inda tayi kuskure ku taru ku bani farinciki, sannan bawai nayi aurennan bane dan kin gaza a wani guri ba,nayi aure ne dan Allah ya bani dama kuma ya hore mini arziƙin da zan zauna daga mace ɗaya har zuwa huɗu, saboda haka ina so ki karɓeta hannu bibbiyu ku zauna lafiya hakan zai sanya ni cikin farin ciki"
Ƙala Na'ima bata ce ba, sai ma amarya Salima ce tayi gyaran murya tare da soma magana cikin kissa
"Insha Allah zaka same mu masu maka biyayya, kuma daga yau wallahi na É—auke ta kamar Æ´ar uwa kuma ina fatan nima zata É—auke ni haka, Insha Allah babu abin da zaka samu daga garemu sai tarin farin ciki mara yankewa mijinmu"
Murmushi kawai Abbi yayi kafin yace "Na gode"Sake kallon Na'ima yayi
"Baki da abin faÉ—a ne uwargidan Khamal?"
"Eh" kawai ta faɗa tare da miƙewa tana gyara mayafinta.
"zan iya tafiya?"
"Eh kije sai da safe"
Bata jira komai ba tayi wucewarta ɗakinta, a hankali ta mayar da ƙofan ta rufe tana sauƙe ajiyar zuciya tare da bin ledojin da ya ajiye mata a bedside da kallo, ƙarasawa tayi ta buɗe, kaza ce guda uku sai fresh milk da sauran tarkacen su fruit da sauransu, tsaki tayi tare da sunkutar ledan ta fito falo, ganin Abbi shi kaɗai yasa ta ƙarasa ba tare da tace masa komai ba ta ajiye ledan akan table ɗin gabansa kafin ta juya zata bar wajen.
"Na'ima" ya kira sunanta a hankali
Daka tawa tayi da tafiyar da take ba tare da ta juyo ba, tana ƙoƙarin mai da hawayen idanunta.
"Please ki kawo min Aishatul-humaira , i want to say goodnight"
Juyowa tayi a fusace kamar za ta yi magana sai kuma ta fasa kallonsa kawai take hawaye na bin fuskarta, cikin sauri Abbi yace
Rana ba ta ƙarya, yau juma'a ranar ɗaurin Auren Abbi da amaryarsa Salima. Ba ƙaramin Dauriya Nai'ma ta yi ba ta shirya cikin wani tsadadden farin less mai adon red, bi sa takurawar su Wasila. Har gida Hajara ta kira wata mai make up ta zo ta yi mata. Duk da idonta a jeme yake saboda kuka amma ta yi kyau, sai dai ramar ta ta fito sosai. A'isha Humairah ma an mata kwalliya cikin sabbin kaya masu kyau white and red, tana rungume a jikin Nai'ma tana bacci bayan ta ci ta ƙoshi. Ƙawayen Nai'ma da wasu daga cikin danginta sun zo tun safe, don ita ma ranar za ta yi nata taron. A tsarin ta ba za ta yi taron komai ba, amma su Wasila suka dage sai an yi, don ƙin yin taron zai saka mutane su gane halin da take ciki na damuwa a kan auren, hakan zai saka kuma a yi mata dariya ne.
Misalin ƙarfe goma sha biyu na rana suna zazzaune a bedroom ɗinta ita da su Aunty Suwaiba, ana ta dannar ƙirjinta, masu zuga ta akan ta yi hauka na yi, masu ba ta shawarwari na gari wanda za su amfane ta na yi. Ita dai duk ba fahimtar su take ba, don hankalinta gabaɗaya ba ya jikinta, yanda take jin zuciyarta kamar ta tashi tay ta zunduma ihu, ganin abun take tamkar a mafarki, wai yau ita za a yiwa kishiya? Ita da ta gama cika baki a cikin ƙawaye da dangi akan Khamal ba zai taɓa ƙara aure ba, amma ya watsa mata ƙasa a ido. A haka Abbi ya shigo ya same su cikin shirin shi na tafiya gurin ɗaurin Aure, ya fito tsaf a angon shi, ba za ka taɓa cewa ya ajiye ɗa kamar Salman ba. Bayan sun gaisa da mutanen ɗakin sai suka tashi suka fice don ba su guri.
A hankali ta ɗago kanta dake sunkuye ta zuba masa ido, tunda ya shigo ta ji sallamar shi gami da ƙamshinsa da ya cika ɗakin ta sunkuyar da kanta, ya yi matuƙar yi mata kyau ba kaɗan ba, farar shaddar jikinsa ba ƙaramin haska shi ta yi ba. Shi ma kallon ta yake yi cikin wani irin yanayi hakan ya sa idanunsu suka sarƙe cikin na juna, ranar da ya fara ganin ta a rayuwarsa ya tuno, ya sani Nai'ma tana son shi ba kaɗan ba, shi ma kuma yana son ta, matsalar ta kawai zafin kishi.
Ganin yadda ta rame sai ya ji tausayin ta mai ɗimbin yawa ya cika masa zuciya, a hankali ya taka ya ƙarasa ya tsugunna a gabanta tare da ɗora hannunsa a kan nata dake kan cikakkiyar sumar kan A'isha Humairah.
"Wifey."
Ya kira sunanta cikin wata irin murya. Duk yadda ta so daurewa kasawa ta yi ta fashe da kuka, cikin kukan ta ce. "Da gaske Khamal kishiya za ka yo mini? Ni ce fa Na'iman ka uwar Ƴaƴanka, me na yi maka ka zaɓi hukunta ni da abin da zuciyata ba za ta dauka ba, ka san ba zan juri ganin ka tare da wata ba.
"Babu abin da kika mini Na'ima." Ya yi maganar yana ɗauke A'isha daga kan cinyarta ya kwantar da ita a gefe. Cikin ƙauna da kulawa ya rungume ta tare da faɗin. "I'm sorry, Ina son ki sosai matata, kuma duk wata mace da zan so a bayan ki take." Rarrashin ta ya yi sosai da daddaɗan kalamai har ya samu ta yi shiru, bai bar ɗakin ba sai da ya tabbatar ya sanyaya mata rai, ya yi musu pictures a wayarsa tare da A'isha Humairah, yana fita ta ƙara fashewa da kuka, a haka su Hajira suka dawo suka same ta.
"Mene haka? Kukan na mene kuma? Sai kin ɓata kwalliyar? Haba Nai'ma sai ka ce wata yarinya, jama'a sun fara taruwa ke kuma kina nan kina kuka? Haka za a kawo amaryar kina wannan sakarcin? To wallahi idan ba kya danne kishin ki za ta samu lagon ki tana ƙunsa miki baƙin ciki, ki je ki yi tunda ke ba kya jin magana."
"To ni Aunty Wasila ya kuke so in yi? Ko don ba ku san me nake ji ba ne a cikin raina?"
Ganin yadda take kuka kamar za ta shiɗe sai suka shiga lallaɓa ta, har ta haƙura ta yi shiru ta shiga hada-hada da jama'a. Biki ya ƙayatar sosai, Nai'ma ta saki ranta ana ta hidima da ita, duk da ba ƙaramin dauriya take ba, don ji take tamkar ana rura mata garwashin wuta a cikin zuciyarta. Bayan Magriba aka kawo amarya, kafin ƙarfe tara kowa ya tafi, gidan ya rage daga Na'ima da Humairah sai amarya a part ɗinta, sai mai gadi da sauran masu aiki dake waje. Na'ima tana zaune tana ta trying numbern Salman amma ta ƙi tafiya Abbi ya shigo gidan. Part ɗinta ya zarce direct ya ajiye mata yoghurt da kazar ta, sannan ya sanar mata yana son ganin su a main parlour. Ba ta yi musu ba ta ce masa ga ta nan zuwa. Sai da ta kwantar da A'isha Humairah a cikin net ɗinta sannan ta yafa mayafi ta fita. Shigar ta parlour'n ya yi daidai da ɗago kai da amarya ta yi tana gyara mayafin jikinta. Turus Nai'ma ta ja ta tsaya cikin tsananin ƙaduwa da mamaki, lokaci ɗaya gabanta ya yi mummunar faɗuwa, sakamakon tozali da fuskar amaryar.
Littafin kuɗi ne, don neman ƙarin bayani ku tuntuɓe mu a wannan lambar. 09047871750
[11/9, 8:06 PM] Abk: Da mamaki Na'ima ta din ga bin amaryar Abbi da kallo,dan abin da take gani ya saɓa zatonta, a tunaninta zata ga Salima, tsinanniyyar karuwar data maƙalewa mijinta Khamal Khamis. Matar data tsani jin ko sunanta balle kuma ta yi tozali da mummunar fuskarta wacce take ƙara harzuƙa Mami. Amma sai taga akasin haka dan kuwa wannan Salimar baƙa ce sannan yarinya ce ɗaya shakaf.
Danne mamakinta ta yi tare da ƙarasowa ta nemi kujera can gefe da su ta zauna ba tare da tace musu komai ba.
Gyara zama Abbi ya yi, yana ƙarewa matan nasa kallo cike da Soyayyar ko wacce a zuciyarsa,sai dai son wata ya rinjayi na wata. Sauke numfashi ya yi kafin yai gyaran murya yana kallonsu duka, a hankali ya fara magana yana ɗan satan kallon Na'ima da yaga ta sunkuyar da kanta tana kallon ƙasa,kwata-kwata taƙi kallon inda yake zaune bare kuma amarya tasa Salima.
Nasiha ya yi musu sosai akan yadda zasu zauna da juna lafiya, su mutunta juna sannan ya juya ga Salima yana faÉ—in.
"Salima ga yayarki nan, bana so ki ɗauke ta a matsayin kishiyarki ina so ki ɗauke ta a matsayin ƴar uwarki,wanda zaki iya tunkarar ta idan abu ya shige miki duhu, sannan ina so in sake jaddada miki ban aureki dan bana son Na'ima ba, ina son matata, bata taɓa nuna gazawa akan kulani da kuma iyalina ba, kada ki sawa ranki cewa don bana son matata na aureki ba, na aureki me sbd Ubangiji ya bani damar hakan. Allah ya ƙaddara ni acikin mutanen da zasu ƙara aure sannan su zauna da mata sama da ɗaya, saboda haka ina so ki girmamata ki mutunta ki bata girmanta a matsayinta na wacce take gaba da ke"
Ita dai Na'ima har lokacin kanta a sunkuye yake tana yaƙi da hawayen dake son zubowa kan fuskarta amma taƙi bashi daman hakan, cikin kulawa Abbi ya juyo ga Na'ima ya ce.
"Uwargida sarautar mata, Mrs Khamal ga ƙanwarki nan na kawo miki ita, please Na'ima bana so ki ɗauke ta less than a sister, ki gyara mata inda tayi kuskure ku taru ku bani farinciki, sannan bawai nayi aurennan bane dan kin gaza a wani guri ba,nayi aure ne dan Allah ya bani dama kuma ya hore mini arziƙin da zan zauna daga mace ɗaya har zuwa huɗu, saboda haka ina so ki karɓeta hannu bibbiyu ku zauna lafiya hakan zai sanya ni cikin farin ciki"
Ƙala Na'ima bata ce ba, sai ma amarya Salima ce tayi gyaran murya tare da soma magana cikin kissa
"Insha Allah zaka same mu masu maka biyayya, kuma daga yau wallahi na É—auke ta kamar Æ´ar uwa kuma ina fatan nima zata É—auke ni haka, Insha Allah babu abin da zaka samu daga garemu sai tarin farin ciki mara yankewa mijinmu"
Murmushi kawai Abbi yayi kafin yace "Na gode"Sake kallon Na'ima yayi
"Baki da abin faÉ—a ne uwargidan Khamal?"
"Eh" kawai ta faɗa tare da miƙewa tana gyara mayafinta.
"zan iya tafiya?"
"Eh kije sai da safe"
Bata jira komai ba tayi wucewarta ɗakinta, a hankali ta mayar da ƙofan ta rufe tana sauƙe ajiyar zuciya tare da bin ledojin da ya ajiye mata a bedside da kallo, ƙarasawa tayi ta buɗe, kaza ce guda uku sai fresh milk da sauran tarkacen su fruit da sauransu, tsaki tayi tare da sunkutar ledan ta fito falo, ganin Abbi shi kaɗai yasa ta ƙarasa ba tare da tace masa komai ba ta ajiye ledan akan table ɗin gabansa kafin ta juya zata bar wajen.
"Na'ima" ya kira sunanta a hankali
Daka tawa tayi da tafiyar da take ba tare da ta juyo ba, tana ƙoƙarin mai da hawayen idanunta.
"Please ki kawo min Aishatul-humaira , i want to say goodnight"
Juyowa tayi a fusace kamar za ta yi magana sai kuma ta fasa kallonsa kawai take hawaye na bin fuskarta, cikin sauri Abbi yace