← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 94 OF 238

Sashe 94

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Angel ina tayaki murnar ganin auntynki, Nima nayi murnar ganinki, wallah ba zan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, naji dadi dana zama silar haduwarku...." ta ƙare maganr tare da raba jikinta daga na Unaisah, share mata hawaye tayi da tafukan hannayenta"ki daina kuka kinji, Allah yakamata muyiwa godiya daya sake hadaku, naga ma kamar baki da lafiya, fuskarki ta kumbura, Jikinki da zafi..." cikin kulawa da nuna tausayawa tayi mata maganr

Cikin sanyin murya tace"lafiyana lou, babu abunda ke damuna, farin cikin ganin auntyna ne" ta fada tare da kallon Aneelerh dake kallon ta.

Wayar Aneeleerh ce ta fara ringing, ta ɗauko bag din data bari kasan sofa ta zaro wayar

"Tun bayan da chief ya kiraku wayarki take ta ringing, banaso na katse maku tattaunawarku shiyasa ban kawo maki ita ba..." murmushi aneelerh tayi aranta ta ayyana har yanzu tana nan da wayonta, ga hankali

Ko da ta duba screen din wayar missed calls ta gani sunkai ashirin, daga wurin mutun uku hajiya layla da dr shurem dana mami din su..

Unaisah zan amsa kira" amsa wa tay da toh, mikewa aneelerh tayi ta nufi gefe ɗaya, tabar zahra zaune tare da Unaisah kamar wasu kawaye haka suka fara fira

Hajiya layla ta fara danna wa kira, bayan sun gaisa hajiya layla tace"Aneelerh ya ake ciki? Naji shiru baki kirani ba, ko dai iyayen yarinyar basu bamu ita bane? Wallahi jiya ko baccin kirki Benazir batayi ba, tana ta sambatu tana ambaton sunan yarta .."

"Ki cigaba da kwantar mata da hankali, nayi magana da iyayen yarinyar sun bamu ita, amma sai zuwa anjima zata zo asibitin"

Muryar Hajiya layla da alamun farin ciki ta furta"Alhamdulillah!....wallahi naji dadi Aneenerh, dan Allah kuyi mana godiya wurin iyayanta..."

Murmushi Aneelerh tayi"in sha Allah zanyi masu" sallama sukai da juna, ta sauke ajiyar zuciya, idanunta akan su unaisah, wani irin sonta ne ke kara baibaye zuciyarta,

Layin mami ta kira, ko sallama Aneelerh bata kaiga yi ba, mami ta katse ta da cewe"Aneelerh sai yanzu zaki kirani? Baki ga missed call dina bane? Kunsa inata zullumi, na kasa tsaye na kasa zaune..."

"Allah sarki mami, Yanzu na dauko wayar, banga call din ki ba"

"Toh ya ake ciki ne"?

"Mami, mun ga yarinyar, dagaske ba unaisah bace, zahra tayi kuskuren fada mata sunan ta, ashe ita wannan sunanta Azeezaty, suna bala'en kama da unaisah, amma iyayen yarinyar sun bamu aron ta har zuwa time da benazir zataji sauƙi"

"Toh Aneelerh, har naji sanyi wlh, yanzu zakuje asibitin ne"?

"Mu zamu tafi, ita kuma yarinyar sai zuwa anjima da dare za'a kaita"

"Allah yakaimu lafiya" ameen mami, daga haka sukai sallama da juna, komawa tayi wurin su unaisah suka cigaba da yin firar yaushe rabo, chief tuni ya shige gidan saboda yana son ya fita office, zama taj yai a wurinsu suka dinga sanya juna nishadi, ana tuna rayuwar baya, har wuraren ƙarfe 9 na safe kafin su Aneelerh suka mike zasu tafi, Angel kamar tay masu kuka taso su shiga ciki suka ce a'a sai zuwa na gaba suna sauri ne, dakyar taj ya lallashe ta yace ta koma gida, zaije ya rakasu, tana ji tana gani ya tafi da su aneelerh, a motarshi yakaisu cikin estate din inda suka bar motarsu, sai da ya tabbatar sun tafi kafin ya dawo.

________________________________✍️

Fitowa dr shureim yayi daga bedroom dinsa, Ya kimtsa tsaf cikin shigar su ta larabawa, hannun sa ruke da wayarshi, har ya fara tafiya kiran Aneelerh ya katse mashi hanzarin shi, da sauri yai picking tare da kara wayar a kunnansa

"Assalamu alaikum Aneelerh, barka da safiya, fatan kun wayi gari lafiya"

On the other hand Aneelerh tace"lafiyalou Alhamdulillah, Ya shureim.."

"Tun ɗazu nake ta kiran layin ki don inji Ya ake ciki game da yarinyar an dace ko kuwa"?

"Yaya shureim, mu hadu asibitin zanyi maka bayanin komai" amsa mata yayi da toh, kafin sukai sallama, a tsanake Ya nufi falo, tunkafin Ya isa ya hango mutanan gidan a dining sun hallara sunayin breakfast,

"Shureim har ka kammala shiryawa"? alhaji ubaid ne yai masa maganar

"Eh daddy..." ya faɗa tare da gaishe da su, Alhaji musa yace"ba zakayi breakfast din bane"?

"Idan naje can zanyi..."

"Okey,

Hajiya sarah tace"in sha Allah idan na taso daga office zanbiyo asibitin.."

"Allah ya kawo ku lafiya..." satar kallon zeenatu yayi, hannunta ruke da cup tana shan tea, murmushi ta sakar mashi tare da kashe mashi ido ɗaya...lamarinta ya fara bashi tsoro yarinya kamar mai iskokai?

"Zeenatu ba zaki bini mu tafi ba"?

"Ina zamuje"?

"Asibiti wurin auntynki benazir.." maƙe mashi kafada tayi"bana jin dadi, bazan iya zuwa ba, ka tafi kawai..." da mamaki hajiya sarah take kallon ta

"Zeenatu! Kin kuwa saurari abun da yace maki dakyau? Asibitinne ke bazaki je ba? Dallah tashi ki bi shi ku tafi, idan kika zauna gidan me zaki yi ke kadai? Daddynki ma fita zaiyi..." bata kare maganar ba, Alhaji musa ya katse ta da cewa"ba ki ji tace bata da lafiya ba?

Rai a6ace hajiya sarah tace"amma ay lafiyarta qalou, ni banga wani alamun rashin lafiya atare da ita ba..."

Alhaji ubaid yace"shureim ka tafi kawai, Kada ku takura mata, tun da ba koshin lafiya gare ta ba, ni bana so ma taje asibitin taita kuka kamar jiya da mukai ta fama da ita...." jiki asanyaye dr shureim Ya miƙe idanunsa akan fuskar zeenatu, itama kallon nashi take Yi, ji take kamar ta tashi tabi shi sai dai ta kasa kamar ana ruke kafafunta, a hankali Ya juya yana tafiya kamar babu kuzari a jikin shi, bakomai yake tariyowa ba face kalamanta! Meyasa zeenatu ta canza daga jiya zuwa yau? Ya jefawa kansa tambayar da baida amsarta!!

*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne dukanshi za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08103884440*

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions[14/10, 6:05 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 31 by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
August 27, 2024
Takun Ƙarshe

Bayan komawar Unaisah cikin parlour, a dining room ta hango ƴan uwan ta, har sun fara yin breakfast sunyi neman ta har sun gaji ba su ganta ba, suna jin takun tafiyarta gaba ɗaya suka dago suna kallon ta.....
"Sister! Ina kika shiga muna ta neman ki"? Batool ce tayi mata maganar, bata tanka masu ba, sai faman sakin murmushi takeyi kamar wadda akayiwa albishir da gidan Allah, yau ranta fari fess, cike da zumudi taja kujera ta zauna tana kallon su ɗaya bayan ɗaya, tasan in har ta sanar da su Azeeza game da zuwan auntyn ta aneelerh ba karamin dadi zasu ji ba saboda tasha basu labarinta agidan kurkukun ƙaddara,

abunda bata sani ba tun da ta zauna suke ta kallon ta

"Aunty ummi Ina kwana.. " wani kallo ummi tabi ta da shi, har saida tasha jinin jikin ta

Kafin ummi ta furta kalma Sajeed Ya riga ta cewa"Sister baki da lafiya ne? ko kinyi kuka ne"? lokaci ɗaya yanayin fuskarta ya canza! Kwata kwata ta manta da abun da ya faru daren jiya, saboda murnar zuwan Aunty Anila, maganar sajeed ce ta tuna mata, tuni murnar da take yi ta koma ciki.

"Sister kinyi shiru baki ce komai ba? Meke damunki"? Cike da tashin hankali batool tayi maganar, su Parveen duk sun kura mata ido suna kallonta, jemimah tace"le6enki ma ya kumbura kamar yankan tumatur"

"Unaisah! Lafiyarki kuwa"? Acewar ummi ta faɗa tana kare mata kallon ƙurulla

Adabarbace ta furta"am.. Umm.." sam ta kasa ƙarasa maganar, idanunta azazzare take kallon su.

gani take kamar sun san komai daya faru da ita adaren jiya, da sauri ta miƙe jikinta na kerma tace" aunty ummi babu komai, ba abunda ke damuna, lafiyana lou..." bata ƙare maganar ba, kamar mara gaskiya ta nufi hanyar fita daga dining room din zuciyarta cike fal da tashin hankali

Gaba daya sun lura da tashin hankalin dake akan fuskarta

Deeja na dariya tace"wallahi Allah kumatunta sun kumbura suntum kamar alkubus, wama ya sani ko bugun tsiya akai mata..." bata kare maganar ba, Haris ya toshe bakin ta..

Miƙewa ummi tayi sam hankalin ta bai kwanta da yanayin unaisah ba, miƙewa batool tayi da niyar tabi bayansu, da sauri ummi ta dakatar da ita"ki zauna ku karasa cin abincin, zanji da ita" jiki asanyaye ta amsa mata da toh..

Da sauri ummi ta nufi dakin su Unaisah, tana shiga tajiyo sautin kakarin amanta a toilet kamar zata fasa makoshin ta.

Knocking ƙofar toilet din tay"unaisah ina son magana dake"

Fitowa tayi fuskarta sharkaf da hawaye, hannun ta ruke da ɗan pant din ta.
Chapter 94 · 0% Book details