Sashe 158
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
kasa karasa maganar tayi saboda kukan daya tokare makogwaronta nan hawaye suka dinga zarya kan kuncinta.
Zuciyarshi taso ta karaya da maganarta,
Shesshekar kukan tane Ya fargar da shi, Cikin sigar lallashi yace"in har kin yi imanin cewa Allah shi ke tsare bawansa bai kamata kina tunanin Zai rasa ransa a gurin Yaki ba, ay bashi kadai zaije ba Unaisah baga mu ba ko mu baki damu mu mutu ko muyi rai ba? Wlh Unaisah jininmu akan akaifa yake babu gudu ba ja da baya ko da zamu rasa ranmune sai mun yi yaƙi da dukkan karfin mu, mun dogara da Allah kuma munyi imanin shine zai bamu nasara akan kyakkyawar niyar da muke da ita na ganin mun kawo karshen zaluncin kurkukun kaddara...."
Kwata kwata bata gane me yake cewa ba, ita fa damuwarta akan Danish ne cikin karyayyar murya tace"ni abun da nafi jimawa har yanzu shi ba musulmi bane, I don't want him to lose his life as an unbeliever! ya makomarsa zata kasance?..." ta faɗa tana kallon fuskarshi da idanunta wadanda suka kaɗa jawur da su
shi kanshi abun na damun shi, baida burin daya wuce Danish ya musulunta ko dan ya tsira da imaninsa, amma yasan bamai yiwuwa bane in ba wani iko na Allah ba, saboda wadannan evils din na jikin shi.
"Mu cigaba da taya shi addu'a in sha Allah zai musulunta, ni dai yanzu damuwana ki yi kokari kisa ya amince mana..." kifa kanta tayi jikin pillow, sam bata son maganar gani take kamar tursasa mata yakeyi don ta ingiza danish ga fadawa halaka..
Sarai ya fahimci daga ita har Danish din Giyar soyayyace ke dibarsu, shiyasa har suke neman su bijire..
Gwiwar shi ta sage, cike da rashin kwarin jiki Ya miƙe ba tare daya kauda idanun shi daga kallon ta ba Yace"banzo nan donna bata maki rai ba, kodan na tursasa maki nazo ne don mu hada hannu gurin cimma burin da muka dade muna jiran ranar da zamu aiwatar da shi, kada ki manta nayi ma mahaifiyata alkawarin zan kawo karshen zaluncin Elders bayan haka kema kin min alkawari watakil Yanzu kin manta nasani..." wani irin radadi take ji acikin zuciyarta tana maijin bakin cikin gaza amsa mashi bukatar shi
"Zan tafi Unaisah, ki zauna kiyi nazari da hankalin ki, Zan jira har zuwa lokacin da zaki aiwatar da abun da na sanyaki, bana so kiyi danasani mara amfani..." ya fada tare da juyawa ya nufi kofar fita daga dakin Harya ruke handle din Ya dan dakata tare da juyawa ya dube ta, still bata dago da kanta ba sai kuka take yi
"Kina tunanin zaman Danish agidan nan shi zaisa Ya tsira da ranshi? Abunda baki sani ba dokar elders ce duk wanda ya san sirrinsu dole su kashe shi, in har baije Ya farmakesu ba, to su zasu farkama ke shi ne akowani lokaci" ya na fadan hakan yasa kai ya fuce
Fitar shi keda wuya ta kuma fashewa da wani sabon kukan kamar ranta zai fita, maganar salsabeel ta fara tariyowa farkon haduwarsu agidan kurkukun ƙaddara
_inaso ki ɗaurawa kan ki nauyin yin hakan ko dan saboda rayukan dake rayuwa acikin kurkukun nan cikin mawuyacin hali! Akwai ire iren ku da yawa wadanda basu ji ba basu gani ba, An kulle su an hanasu sakat, Kullum ne sai an rasa rayuka agidan kurkukun nan, kashe mutane suke yi tamkar kyankyasai, Idan har bamu kawo ƙarshen kurkukun nan ba to kuwa zasu cigaba da aikata 6arnar da babu ranar dainawa, Muna matuƙar jin tausayin yaran da ke rayuwa a kurkukun nan, Dan Allah Unaiserh ki taimaki rayuwar su! Ki daure ki jure wurin ganin kun tona asirin abun da ake aikata......" hannayenta Ya ruƙo a cikin nashi ya dinga yi mata magiya sautin muryar shi kamar zai fashe da kuka_
_"NAYI MAKA ALƘAWARI Idan Allah ya bani damar fita daga kurkukun nan zan tona asirin su harma mu bada gudunmawa wurin ganin an kawo ƙarshen su, Bi'iznillahi_
Tuna wannan yasa ta ƙara sautin kukan nata.
A bangaren Salsabeel bayan ya koma backyard din kamar yadda yabarsu Chief haka ya taras da su zaune suna jiran shi.
Bawan Allah duk Ya rasa kuzarin shi, su Unaisah sun bata mashi rai ba kaɗan ba..
Hankalin su baya akan shi har saida yai masu sallama kafin su ka dube shi, zama yai kan kujera ya sunkuyar da kan shi ƙasa tun daga yanayin shi suka fahimci akwai damuwa..
"Salsabeel ka yi shiru baka ce mana komai ba! Ya kuka ƙare da shi"? Cikin kulawa Taj yai maganar..
Cike da jin nauyin su ya girgiza kai,
"Danish ya bani kunya, ban ta6a zaton zai bijire min ba..." tun da suka ji hakan damuwa ta bayyana akan fuskokin su don sun riga sun hasaso karashen zancen na shi..
Rai a6ace Omar yace"meyasa zamu wahalar da kanmu akan shi? Yaron nan fa ɗan rainin wayau ne, idan muka ce zamu bishi ta lalama bazai ta6a bamu haɗin kai ba, kwara mu bi shi ta ƙarfi da yaji mu ci ubanshi har sai ya miƙa wuya..."yana huci ya faɗa kamar zai haɗiyi zuciyarsa saboda bacin rai..
Chief ya ɗaga mashi hannu badan Ya ƙarasa maganar ba yaja baki yayi shiru fuskar shi a murtuke..
"In har bashi yayi niya ba, ko da zamu rasa damar da muke da ita na zuwa gidan kurkukun bazan bari a tursasa masa ba, itama Unaisah ban amince ayi amfani da ita gurin shawo kan shi ba, cos zai ga kamar ni na sanya ta ne" Salsabeel ya ɗan kalle sa cos shi harya riga daya tuntu6i Unaisah.
Cike da takaici Big guy ke kallon chief da yai maganar
"Haba Owais, Saboda shi kawai zamu fasa niyar mu"?
"Omar, ba ina nufin zan fasa aikin mu bane, sai dai mu nemi wata hanyar..." bai ƙare maganar ba, Big guy ya mike yana huci ya kama hanya zai bar backyard din..
Damuwa ta hana Taj furta kalma baima san me suke cewa ba.
Miƙewa chief yayi da sauri yabi bayan Omar, don bazai bari su sabamu sabani tsakaninsu ba dama kwanakin nan yana jin haushin fifita Danish da yake yi.
Bayan tafiyar su, ya rage saura Taj da Salsabeel sunyi shiru babu mai magana acikin su.
Ganin yadda Taj ya zabga uban tagumi ne yasa Salsabeel furta"Sir are you Okay"?
Yamutsa fuska yai"kada ka damu, i'm okay, just banji dadin yadda ɗan uwanka yaƙi bamu haɗin kai ba" ya fada yana kallon Salsabeel
"Amma Salsabeel babu dabara da zamu iya yi don mu shawo kan shi"?
Shiru Salsabeel yayi yana nazarin maganar shi, wata dabara ce ta faɗo mashi arai da sauri Ya dubi Taj
"Akwai hanya ɗaya" akagare Taj yace"Ina sauraronka"
"Ƴarka Unaisah, Ita kaɗai ce zata Iya sa shi dole yayi..." lokaci ɗaya Taj ya haɗe rai, annurin fuskar shi ya ɗauke, saboda zafin maganar Salsabeel daya ji.
"Meyasa kace haka"?
Murmushi Salsabeel ya ɗanyi kafin ya fara zayyana masa dalilinsa nacewa haka!
"in har ta umarce daya je zai je, saboda ya mutu akan Sonta, ba irin magiyar da banyi mata ba akan taje ta rokar mana shi amma taƙiya saboda gudun kada ta yi silar da zai rasa ranshi, amma ina da tabbacin in har ka yi mata magana zamu iya cin galaba akan ta saboda kai mahafinta ne, bazata ki bin umarninka ba"...
Tun da ya fara magana Taj ya tsare shi da ido batare da kyaftawa ba, bakomai yake tunawa ba face abunda idanun shi suka gane mashi, ɗari bisa ɗari ya yadda da maganar Salsabeel saboda shi shaidane akan mahaukacin son da suke ma junan su, duk da ya ɗauke ƙafa akanta amma yana jin zai iya zuwa gurinta don ya jarabata"
Har salsabeel ya ƙare maganar Taj bai sani ba, gyaran muryar da yayi mashi ne ya fargar da shi
"Pls, ka taimaka koda sau ɗaya ne ka jaraba yi mata magana.." fuskar shi amarairaice ya fada..
Wayar Taj ce tay ringing, kallon Salsabeel yayi"it is Okay, zan jaraba" ya faɗa tare da miƙewa Yai picking call din
"Sir, ina fata lafiya, naji shiru baku dawo ba"
"Boss, Ka sallami Salsabeel ya tafi, kaima zaka iya tafiya..." amsa mashi yai da toh..
"Chief yace ka tafi, zai neme ka" mikewa yayi"pls sir, sai naji daga gare ka" jinjina mashi kai yai batare daya fur ta kalma ba.
_________________________________✍️
Su Batool na zaune a falo suna fira kusan su dukkansu in ka cire Unaisah da Danish sai ummi su kadai ke babu a cikin su...
Sam basu lura da shugowarshi ba fira taja hankalin su, ganin babu Unaisah yasa shi juyawa ya nufi bedroom din...
Adai dai lokacin ta fito daga bathroom, sanye da yar rigar wanka, zuciyarta cike fal da tunanin abunda suka tattauna da Salsabeel
Wayar ce ta fara ringing, har zata dauka taji anyi knocking din kofar
"Wanene"?
"Ki buɗe kofar ki gani" ras ta ɗan ji gabanta ya fadi jin muryar daddynta, tana jin shakkar shi yanzu ba kadan ba saboda canzawar da yayi mata.
"Unaisah ba zaki buɗe min ƙofar bane"! Jikinta na 6ari ta je ta buɗe ƙofar, shigowa ciki yai tare da aza idanun shi kan fuskarta wani irin tausayinta ne ya kama shi.
Cikin rawar murya tace"daddy Ina wuni" ta fada tana kallon shi
Shiru yayi bai tanka mata ba hakan ba karamin karya mata zuciya yayi ba.. Kasa jurewa tayi batasan sa'adda ta faɗa kan kirjin shi ta kankame shi tana tana kuka tace laifin me na maka daddy? Meyasa ka canza min? Ka daina sakar min fuska, idan na gaishe ka dakyar kake amsa min idan na kira wayarka baka ɗagawa, daddy don soyayyarka da manzon Allah ka fadamin laifin me nayi maka sai in nemi yafiyarka, wlh bana so kana fushi dani Daddy, kaifa mahaifina ne kasan hukuncin wanda iyayensa ke fushi da shi ...."sambatu taci gaba dayi batare data raba jikinta daga nashi ba..
Zuciyarshi taso ta karaya da maganarta,
Shesshekar kukan tane Ya fargar da shi, Cikin sigar lallashi yace"in har kin yi imanin cewa Allah shi ke tsare bawansa bai kamata kina tunanin Zai rasa ransa a gurin Yaki ba, ay bashi kadai zaije ba Unaisah baga mu ba ko mu baki damu mu mutu ko muyi rai ba? Wlh Unaisah jininmu akan akaifa yake babu gudu ba ja da baya ko da zamu rasa ranmune sai mun yi yaƙi da dukkan karfin mu, mun dogara da Allah kuma munyi imanin shine zai bamu nasara akan kyakkyawar niyar da muke da ita na ganin mun kawo karshen zaluncin kurkukun kaddara...."
Kwata kwata bata gane me yake cewa ba, ita fa damuwarta akan Danish ne cikin karyayyar murya tace"ni abun da nafi jimawa har yanzu shi ba musulmi bane, I don't want him to lose his life as an unbeliever! ya makomarsa zata kasance?..." ta faɗa tana kallon fuskarshi da idanunta wadanda suka kaɗa jawur da su
shi kanshi abun na damun shi, baida burin daya wuce Danish ya musulunta ko dan ya tsira da imaninsa, amma yasan bamai yiwuwa bane in ba wani iko na Allah ba, saboda wadannan evils din na jikin shi.
"Mu cigaba da taya shi addu'a in sha Allah zai musulunta, ni dai yanzu damuwana ki yi kokari kisa ya amince mana..." kifa kanta tayi jikin pillow, sam bata son maganar gani take kamar tursasa mata yakeyi don ta ingiza danish ga fadawa halaka..
Sarai ya fahimci daga ita har Danish din Giyar soyayyace ke dibarsu, shiyasa har suke neman su bijire..
Gwiwar shi ta sage, cike da rashin kwarin jiki Ya miƙe ba tare daya kauda idanun shi daga kallon ta ba Yace"banzo nan donna bata maki rai ba, kodan na tursasa maki nazo ne don mu hada hannu gurin cimma burin da muka dade muna jiran ranar da zamu aiwatar da shi, kada ki manta nayi ma mahaifiyata alkawarin zan kawo karshen zaluncin Elders bayan haka kema kin min alkawari watakil Yanzu kin manta nasani..." wani irin radadi take ji acikin zuciyarta tana maijin bakin cikin gaza amsa mashi bukatar shi
"Zan tafi Unaisah, ki zauna kiyi nazari da hankalin ki, Zan jira har zuwa lokacin da zaki aiwatar da abun da na sanyaki, bana so kiyi danasani mara amfani..." ya fada tare da juyawa ya nufi kofar fita daga dakin Harya ruke handle din Ya dan dakata tare da juyawa ya dube ta, still bata dago da kanta ba sai kuka take yi
"Kina tunanin zaman Danish agidan nan shi zaisa Ya tsira da ranshi? Abunda baki sani ba dokar elders ce duk wanda ya san sirrinsu dole su kashe shi, in har baije Ya farmakesu ba, to su zasu farkama ke shi ne akowani lokaci" ya na fadan hakan yasa kai ya fuce
Fitar shi keda wuya ta kuma fashewa da wani sabon kukan kamar ranta zai fita, maganar salsabeel ta fara tariyowa farkon haduwarsu agidan kurkukun ƙaddara
_inaso ki ɗaurawa kan ki nauyin yin hakan ko dan saboda rayukan dake rayuwa acikin kurkukun nan cikin mawuyacin hali! Akwai ire iren ku da yawa wadanda basu ji ba basu gani ba, An kulle su an hanasu sakat, Kullum ne sai an rasa rayuka agidan kurkukun nan, kashe mutane suke yi tamkar kyankyasai, Idan har bamu kawo ƙarshen kurkukun nan ba to kuwa zasu cigaba da aikata 6arnar da babu ranar dainawa, Muna matuƙar jin tausayin yaran da ke rayuwa a kurkukun nan, Dan Allah Unaiserh ki taimaki rayuwar su! Ki daure ki jure wurin ganin kun tona asirin abun da ake aikata......" hannayenta Ya ruƙo a cikin nashi ya dinga yi mata magiya sautin muryar shi kamar zai fashe da kuka_
_"NAYI MAKA ALƘAWARI Idan Allah ya bani damar fita daga kurkukun nan zan tona asirin su harma mu bada gudunmawa wurin ganin an kawo ƙarshen su, Bi'iznillahi_
Tuna wannan yasa ta ƙara sautin kukan nata.
A bangaren Salsabeel bayan ya koma backyard din kamar yadda yabarsu Chief haka ya taras da su zaune suna jiran shi.
Bawan Allah duk Ya rasa kuzarin shi, su Unaisah sun bata mashi rai ba kaɗan ba..
Hankalin su baya akan shi har saida yai masu sallama kafin su ka dube shi, zama yai kan kujera ya sunkuyar da kan shi ƙasa tun daga yanayin shi suka fahimci akwai damuwa..
"Salsabeel ka yi shiru baka ce mana komai ba! Ya kuka ƙare da shi"? Cikin kulawa Taj yai maganar..
Cike da jin nauyin su ya girgiza kai,
"Danish ya bani kunya, ban ta6a zaton zai bijire min ba..." tun da suka ji hakan damuwa ta bayyana akan fuskokin su don sun riga sun hasaso karashen zancen na shi..
Rai a6ace Omar yace"meyasa zamu wahalar da kanmu akan shi? Yaron nan fa ɗan rainin wayau ne, idan muka ce zamu bishi ta lalama bazai ta6a bamu haɗin kai ba, kwara mu bi shi ta ƙarfi da yaji mu ci ubanshi har sai ya miƙa wuya..."yana huci ya faɗa kamar zai haɗiyi zuciyarsa saboda bacin rai..
Chief ya ɗaga mashi hannu badan Ya ƙarasa maganar ba yaja baki yayi shiru fuskar shi a murtuke..
"In har bashi yayi niya ba, ko da zamu rasa damar da muke da ita na zuwa gidan kurkukun bazan bari a tursasa masa ba, itama Unaisah ban amince ayi amfani da ita gurin shawo kan shi ba, cos zai ga kamar ni na sanya ta ne" Salsabeel ya ɗan kalle sa cos shi harya riga daya tuntu6i Unaisah.
Cike da takaici Big guy ke kallon chief da yai maganar
"Haba Owais, Saboda shi kawai zamu fasa niyar mu"?
"Omar, ba ina nufin zan fasa aikin mu bane, sai dai mu nemi wata hanyar..." bai ƙare maganar ba, Big guy ya mike yana huci ya kama hanya zai bar backyard din..
Damuwa ta hana Taj furta kalma baima san me suke cewa ba.
Miƙewa chief yayi da sauri yabi bayan Omar, don bazai bari su sabamu sabani tsakaninsu ba dama kwanakin nan yana jin haushin fifita Danish da yake yi.
Bayan tafiyar su, ya rage saura Taj da Salsabeel sunyi shiru babu mai magana acikin su.
Ganin yadda Taj ya zabga uban tagumi ne yasa Salsabeel furta"Sir are you Okay"?
Yamutsa fuska yai"kada ka damu, i'm okay, just banji dadin yadda ɗan uwanka yaƙi bamu haɗin kai ba" ya fada yana kallon Salsabeel
"Amma Salsabeel babu dabara da zamu iya yi don mu shawo kan shi"?
Shiru Salsabeel yayi yana nazarin maganar shi, wata dabara ce ta faɗo mashi arai da sauri Ya dubi Taj
"Akwai hanya ɗaya" akagare Taj yace"Ina sauraronka"
"Ƴarka Unaisah, Ita kaɗai ce zata Iya sa shi dole yayi..." lokaci ɗaya Taj ya haɗe rai, annurin fuskar shi ya ɗauke, saboda zafin maganar Salsabeel daya ji.
"Meyasa kace haka"?
Murmushi Salsabeel ya ɗanyi kafin ya fara zayyana masa dalilinsa nacewa haka!
"in har ta umarce daya je zai je, saboda ya mutu akan Sonta, ba irin magiyar da banyi mata ba akan taje ta rokar mana shi amma taƙiya saboda gudun kada ta yi silar da zai rasa ranshi, amma ina da tabbacin in har ka yi mata magana zamu iya cin galaba akan ta saboda kai mahafinta ne, bazata ki bin umarninka ba"...
Tun da ya fara magana Taj ya tsare shi da ido batare da kyaftawa ba, bakomai yake tunawa ba face abunda idanun shi suka gane mashi, ɗari bisa ɗari ya yadda da maganar Salsabeel saboda shi shaidane akan mahaukacin son da suke ma junan su, duk da ya ɗauke ƙafa akanta amma yana jin zai iya zuwa gurinta don ya jarabata"
Har salsabeel ya ƙare maganar Taj bai sani ba, gyaran muryar da yayi mashi ne ya fargar da shi
"Pls, ka taimaka koda sau ɗaya ne ka jaraba yi mata magana.." fuskar shi amarairaice ya fada..
Wayar Taj ce tay ringing, kallon Salsabeel yayi"it is Okay, zan jaraba" ya faɗa tare da miƙewa Yai picking call din
"Sir, ina fata lafiya, naji shiru baku dawo ba"
"Boss, Ka sallami Salsabeel ya tafi, kaima zaka iya tafiya..." amsa mashi yai da toh..
"Chief yace ka tafi, zai neme ka" mikewa yayi"pls sir, sai naji daga gare ka" jinjina mashi kai yai batare daya fur ta kalma ba.
_________________________________✍️
Su Batool na zaune a falo suna fira kusan su dukkansu in ka cire Unaisah da Danish sai ummi su kadai ke babu a cikin su...
Sam basu lura da shugowarshi ba fira taja hankalin su, ganin babu Unaisah yasa shi juyawa ya nufi bedroom din...
Adai dai lokacin ta fito daga bathroom, sanye da yar rigar wanka, zuciyarta cike fal da tunanin abunda suka tattauna da Salsabeel
Wayar ce ta fara ringing, har zata dauka taji anyi knocking din kofar
"Wanene"?
"Ki buɗe kofar ki gani" ras ta ɗan ji gabanta ya fadi jin muryar daddynta, tana jin shakkar shi yanzu ba kadan ba saboda canzawar da yayi mata.
"Unaisah ba zaki buɗe min ƙofar bane"! Jikinta na 6ari ta je ta buɗe ƙofar, shigowa ciki yai tare da aza idanun shi kan fuskarta wani irin tausayinta ne ya kama shi.
Cikin rawar murya tace"daddy Ina wuni" ta fada tana kallon shi
Shiru yayi bai tanka mata ba hakan ba karamin karya mata zuciya yayi ba.. Kasa jurewa tayi batasan sa'adda ta faɗa kan kirjin shi ta kankame shi tana tana kuka tace laifin me na maka daddy? Meyasa ka canza min? Ka daina sakar min fuska, idan na gaishe ka dakyar kake amsa min idan na kira wayarka baka ɗagawa, daddy don soyayyarka da manzon Allah ka fadamin laifin me nayi maka sai in nemi yafiyarka, wlh bana so kana fushi dani Daddy, kaifa mahaifina ne kasan hukuncin wanda iyayensa ke fushi da shi ...."sambatu taci gaba dayi batare data raba jikinta daga nashi ba..