← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 194 OF 238

Sashe 194

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hakika ta burge shi sosai, Har ya zagayo ta gabanta bata lura da shi ba, saboda ta ɗan lumshe idanunta, dogayen eye lashes din ta sun jiƙu da ruwan hawayenta.

Kyakkyawar fuskarta ta 6aci da hawayen ta, ɗaga hannayenta tayi sama Cikin harshen larabci ta fara karanta addu'o'i duk akan Danish dinta.

Lumshe idanun shi yai a hankali ya sake bude su kan fuskarta, ya jinjinama irin kaunar da take ma Danish yayi fatan ace shi ya samu soyayyarta, saboda samun mace tagari irin ta zaiyi wuya a fadin duniyar nan, yarinyar da zata iya tashi in the middle of the Night tayi nafilfili don ta yi maka addu'a Omg😘

A hankali Ya zukunna ta gefen ta, Ya zuba mata lumsassun idanun shi masu ɗauke da bacci.

Bakomai yake kallo ba fa ce eye lashes dinta da soft lips dinta dake kerma sun jiku da hawayen ta sometime har tongue take zurowa ta lashe su baisan ya akai ya tsinci kan shi da kallon ta ba.

A hankali ya mayar da eye balls dinsa kan kwantaccen gashin forehead dinta dark brown ya nannade gwanin ban sha'awa kai komai nata abun ban sha'awa ne.

Kasa yi mata magana yai cos yai tunanin she may feel uncomfortable if she sees him in front of her.

Slowly ya miƙe tare da juyawa ya nufi hanyar fucewa daga dakin
Kamar daga sama yajiyo muryarta a cikin kunnan shi"Wanene" dan dakatawa yai ba tare da ya juya ba, Zumbur ta mike gabanta na faduwa cos tajiyo motsin tafiyar shi.

waro idanu waje tay lokacin da tay arba da faffadan bayan shi, wlh sai taga kamar Danish ne yanayin tsayuwarsa banbancin Danish yafi sa tsayi da kuma doguwar sumar kai, uwa uba launin fatarsu ba daya ba.

"Wanene"? Ta ƙara faɗa cike da fargaba, gudun kada ya tsoratar da ita yasa shi juyowa a hankali suka fuskanci juna tana ganin chief tay saurin share hawayen ta saboda ya hanata kuka, tayi mamakin ganinsa a wannan lokacin a cikin dakinsu, arude ta furta"barka da dare" ya fahimci rudani dake akan fuskarta hakan yasa shi cewa"I'm sorry na shigo dakin ku batare da izninku ba, na fito ina zagayawane najiyo shesshekar kukanki, Hankali ya tashi sau uku ina yin sallama ba'a amsa min ba, har knocking nayi shiru shiyasa na yanke shawarar shigowa ciki amma ba halina bane"

Cikin sanyin murya ta furta"na fahimce ka, kuma nagode da kulawarka agare ni, ka damu dani sosai"

Sam taki bari su hada ido tun kallon farko da tay mashi ta kawar da idanun ta.

"Kin manta sharaddun da dr ya gindaya maki? I thought I would find you sleeping, although you are doing good thing, but you should continue resting until you've fully recovered, ban hana ki masa addu'a ba, zaki iya yi masa addu'a aduk lokacin da kikai sallah, amma yanzu dare ne Unaisah"

with respect ta amsa mashi da toh.

Shiru suka ɗanyi na wani lokaci, takun tafiyarsa taji da sauri ta dago matsowa yai dab da ita..

Ta sadda kanta kasa tana dan jin faduwar gaba.

In a cool voice yace"a ranar da mu ka kwana a sansanin mu, Danish ya nemi in yi masa alkawarin ko bayan ransa In kula da rayuwarki data mahaifinki da yan uwanki, and I vowed to fulfill his request"

jin wannan maganar yasata kusa fashewa da kuka jikinta ya kama kerma.

"Ban fada maki don in fama maki raunin dake a cikin zuciyarki ba, sai don inaso ki taimakamin Unaisah, Ki bani hadinkai gurin ganin na cika masa alkawarinsa, in har kika bani dama duk da ina shiga busy saboda aiki zan yi kokarin ware mana lokacin da zamu dinga ganawa da juna, in sha Allah I'll support you in overcoming the pain that's troubling you."

dakyar ya ƙare maganin ganin yadda hawaye ke yar tseral kan kuncinta aranta ta ayyana wata irin kauna Danish yakeyi mata? Ya Ilahi, Shi damuwar shi wanda zai kula da rayuwarsu in baya nan wayyo Allah hakika tayi babban rashi arayuwar ta.

batai aune ba taji safkar yatsun chief kan fuskarta gently ya soma share mata hawayen ta.

Muryarsa tamkar ta me yin raɗa ya furta"If you give me a chance, I will replace him, despite knowing I may never fully replace him in your heart" ya ɗan dakata yana mayar da numfashi, ta nutsu tana sauraron shi.

"Na riga shi sanin ki amma ya riga ni haduwa dake, nasan da ace tun lokacin na bayyana kaina agurinki da nima na samu gurbi acikin zuciyarki, sai dai kash na makaro amma har yanzu ina da sauran dama Unaisah, nasan kun shaku da juna ke da shi, kun sha wahala a tare, kun yi rayuwa a guri ɗaya, kun san sirrin juna, nikuma bansan komai dangane dake ba, amma idan kika bani dama nayi maki alkawarin zan canza maki rayuwarki...."

da wata irin siga ta jan hankali yai mata maganar, har saida taji wani irin yanayi atare da ita, kalamansa sun ta6a zuciyarta.

Ɗagowar da zatay keda wuya karan hancinsu ya gogi na juna razanar da ta ɗanyi ne yasa ta ɗaga ƙafa zatay baya aikuwa gaba daya ta tafi zata kife kasa saboda rashin kwarin jikinta.

Cikin zafin nama yai hanzarin damko waist dinta Ya janyota gaba daya ta fada kan broad chest din shi, wani irin faduwar gaba taji, She could feel his heart beating rapidly, lumshe idanunta ta danyi sam ta kasa motsawa daga jikin shi, ta rasa gane me take ji? Amma tabbas taji wani irin sanyi da kwanciya hankali yana ratsa zuciyarta.

har ga Allah bai janyota da wata manufa ba, gudun kada ta fadi yasa shi rukota sai kuma abun ya nemi ya jefasa a wani yanayi mara misaltuwa, nutsuwa yai yana kallon fuskarta tay lamo a jikin shi kamar jinjira.

Damuwar rashin Danish ta fara affecting brain din ta, komai ya faru Danish take gani a yanzu haka ji take kamar a jikin Danish ta faɗa shiyasa ta kara narke masa.

abunka ga mabukacin dake bukatar duk wani abu da zai sanyaya mashi zuciya.

"Unaisah" shiru bata amsa mashi ba.

"are you sleepy? Ya tambaya yana leken fuskarsa.

Still bata motsa ba, Batool ce ta fara mutsu mutsu kamar zata farka, hakan yasa shi raba ta daga jikin shi ya ɗan jijjigata dakyar ya samu ta buɗe idanunta wadanda suka kaɗa jawur kamar an watsa masu barkono.

"Muje ki kwanta" kamar gunki tay shiru babu alamun zata ɗaga ƙafarta, kamar bata jin me yake cewa.

Sungumarta yai kan Shoulder inshi Ya nufi bed da ita, Cikin kulawa ya kwantar da ita..

"Kada Ki kwana Da hijab a jikin ki, Ki cire sannan ki yi addu'a" sai lokacin ta dan jinjina ma shi kai.

Ajiyar zuciya ya sauke kafin Yai hanzarin juyawa ya fuce daga dakin.

Sai bayan daya fitane ta samu kanta, maganganunsa ne suka dinga yi mata yawo akai a haka har bacci mai dadi yai awon gaba da ita.

"ANEELEERH🌹*

ba ita ta tashi farkawa ba sai wuraren ƙarfe huɗu na dare dayake tasa abun aranta har mafarki saida tayi, idanunta biji biji ta buɗe su ta dubi agogo, kafin ta curo wayar daga chargy harta cika, Kunna wayar tayi Haskenta na kawowa taga abunda ya karya zuciyarta hoton Ana ne da baby junaid akan wallpaper dinta sunyi murmushi a hoton.

Bata samu wayar da password ba, lalube ta cigaba dayi mata ta shiga whatsapp dinta, tana tsaka dayin scrolling ta fada Archived anan taga wani Group da Ana ta bude ita da sisters dinta,, Shiga ciki tayi ta soma karanta firarsu.

_sister, ke da kike zaune cikin rufin asirin Allah, meyasa kika ce kin gaji da zama gidan? Bayan irin sabon da kikayi da Aneelerh, gashi muma ta silarki mun samu taimako a gurin ta_

_ba zaku gane ba, Ni kadai nasan halin da nake aciki, bawai don son raina nakeso In bar gidan ba, kawai hankalina ba akwance Yake ba, ni dai kawai inaso nabar gidan ne_

_kinga in wani abu ke damunki, ki fada mana, mu nemi mafita a tare_

_kada ku ɗaga hankulanku, babu komai, kawai inaso nadinga ganinku kullum akusa dani, saboda kuka dai ne dangin da kuka rage min a duniya_

_idan kina so mu dawo kusa dake, toh ki sama mana aiki anan abujan mana, sai mu dawo, muma munfiso mu zauna kusa da ke_

_bazan bari ku dawo nan ba, sai ni kusa ma min aiki in dawo nan_

_meyasa_

_nafison zama a Jos din fiye da nan_

Dakatawa Aneelerh tayi da karanta sakon, aranta ta ayyana meyasa Ana take gudun zama abuja? Bayan kafin zuwansu tafi kowa daukin zasu dawo nan"! Girgiza kai ta danyi kafin ta yanko wata firar tasu ta ci gaba da karantawa..

_janet tace"Ana! Kina cikin hayyacinki kuwa? Meyasa kike magana kamar wata musulma"? esther tace"Na fara zarginta, cikin kwanakin nan kullum in zakiyi magana a group chat dinmu sai kin sanya mana abun addinin musulunci bayan mu ba musulmai bane_

_Voice note ta tura masu"nagaji da 6oye maku da nake yi, ku yan uwana ne babu wani sirri atsakanin mu, nasan zaku goyi bayana" su kace muna sauraronki"Na musulunta, Yau wata biyu kenan, amma babu wanda ya sani, ko Aneelerh ban fada mata ba, A boye nake yin sallah ta"_

_"Dagaske kike ko wasa" janet ce ta fada_

_"Na ta6a maki wasa irin wannan"?
Janet tace"a'a"_

_Ana Tace"toh, Dagaske nake Ana ɗinku Yanzu musulmace ni, na yi imani da Allah kuma nayi imanin cewa Jesus da muke bautamawa bawan Allah ne kuma manzon sa ne"_

Esther tace"nagaza yarda Ana, kamar dai kin haukace, taya zaki bar addinin iyayen mu da kakannin mu"?
Chapter 194 · 0% Book details