← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 238

Sashe 77

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushi Zahra tayi "itace yarinyar da nake baki labari mun haɗu a wurin dinner ɗin, amma ya akai naga kamar hankalinki Ya tashi da ganinta?" Ta faɗa tana kallon fuskarta,

"Zahra taya hankalina bazai tashi ba, ke baki ga fuskarta da kyau ba? wannan yarinyar kamanninta sun 6aci dana Angel ɗinmu...!" Saida Aneelerh tay wannan maganar Zahra tafara tariyo fuskar Yarinyar, haba shiyasa take tayi mata kallon sani,

"Zahra bata fada maki sunanta ba"?

"Tace min sunanta UNAISAH"!

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK

COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more

Accept !
[14/10, 6:05 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Page 26 Complete
by
Novels Elite Admin
July 07, 2024
Sponsored Link

Novels Elite English
Rass Taji gabanta Ya faɗi La66anta na kerma tace"Zahra itama ainihin sunanta Unaisah, Angel da muke kiranta nickname ne da daddynta Ya sanya mata, ɗiyar wacece ne a family din su"?

Hankalin zahra ba karamin tashi yayi ba, ganin yadda aneelerh ta ruɗe ita kanta aruɗen take

"Na manta ban faɗa maki labarin Yaran ba, Kamar Yadda naji daga bakin chief owais, kamar ba su da alaka da su, hasalima a daji suka tsinto su..." tiryan tiryan Zahra ta kwashe duk abunda Ya faru a wurin dinner din dangane da su Unaisah ta sanar da aneelerh

Kusan zaucewa tayi hannunta dafe da kai, ganin tana tangyal tangyal kamar zata faɗi Yasa Zahra Yin saurin ruƙo Aneeelerh ta taimaka mata ta zauna gefen gado

"Wallahi itace, Angel ce, Har abada bazan ta6a mantawa da fuskarta ba, ko shakku banayi wannan Yarinyar ANGEL ce tun da har kika ce tsintar su akai....

Gaba ɗaya rudanine akan fuskokin su,

"Hakan na nufin Junaid Shi Ya fara gane itace?

"Bangane me kike nufi ba yaga hoton ne"!

Jinjina mata kai tay lokacin dana buɗe hoton don in nuna masa da karfi ya kwace wayar daga hannuna Yana fadin Angel Angel..."

"Zai iya yiwuwa saboda Yawan nuna masa hotunanta da nake Yi shiyasa Ya gane ta, Ni dai Yanzu Ki taimaka min zahra! Inason na tabbatar da abun da nake hasashe! Taya zamu Iya ganin ta"❓❓❓

"Auntyna Ganinta ba abune mai sauƙi ba, dama ace bangaren su hajiya saratu suke da zama zaifi min sauki in nemi alfarmar ganinta, amma gaskiya tunkarar chief owais ba abune mai sauƙi ba! Kinsan Yanayin aikin su na jami'an sirri wallahi in ma suka ji maganar zasu Iya tuhumarmu"

"Wallahi zahra In har ban samu ganin Yarinyar nan ba Hankalina bazai ta6a kwanciya ba, ke koda Zasu tuhume ni ne, gobe sai naje estate din nasu..." da kwarin gwiwa tayi maganar

"Ƙwara mu bi komai a sannu, kada mu ce zamuyi gaggawa tun da bamu da tabbacin in itace dagaske...." kafin zahra ta ƙare maganar Aneelerh ta katse ta da cewa"zahra itace! Nifa ba makauniya bace, wallahi unaisah ce Yarinyar nan, tun fa tana jinjirarta muke kula da ita, shayar da ita ne kawai banyi na, tayaya bazan gane fuskarta ba"? Idanunta cike tab da kwalla ta furta maganar

"Ki taimaka min zahra, dan Allah, ko dan saboda Halin da mahaifiyarta take a ciki, wallahi bakiga tashin hankalin data Shiga ba a lokacin dana sanar da ita zancen 6acewar su, ba dan zuciyar imani ba da tuni zuciyarta ta buga...."

Ruƙo hannunta zahra tayi a cikin nata"ki kwantar da hankalinki aunty aneelerh, kada ki bari hawayen dake taruwa a cikin idanunki su zuba, muyi hakuri zuwa gobe inyaso sai muje can estate din nasu watakil adace su barmu mu ganta..." cikin kwantar da murya tayi maganar donta fahimci nema take ta zauce har lokaci bata daina kallon hoton ba

"Mezai hana mu tuntu6i Ziyad? tun da shi yasan da zancen 6acewarsu kuma yana da hotunan Unaisah da na tura masa ko shi zai iya yi mana hanyar haɗuwa da ita"

"Good Idea Auntyna, Yanzu Ki kwanta Ki huta, Gobe saimu ƙarasa maganar"

Jinjina kai tayi"shikenan zahra, Allah yasa zan Iya runtsawa, Bakisan Yadda na ƙagu da son ganin Yarinyar nan ba, fatana Allah Yasa itace ɗin."

"Amma kunyi waya da su aunty Benazir din? Sun isa gida Lafiya?

"Na kira layinta bata ɗaga ba, sai zuwa gobe zan sake jaraba kiran ta.."

Suna Cikin Yin magana Baby Junaid Ya fara mutsu mutsu zai farka daga bacci

"Junaid zai farka, Ki koma gurinsa, ni zan wuce aunty aneelerh,

Miƙa mata wayar tayi"mu kwana lafiya zahra"

Fucewa tayi daga dakin, Aneelerh ta koma kan gado ta janyo junaid on her chest ta rungumesa

Babu alamun zata Iya runtsawa saboda zumudin jiran gobe tayi, abu biyu ne suka tsaya mata aranta, na farko damuwar Benazir, na biyu yarinyar nan mai suna Unaisah...

*HAJJATY*

Can cikin bacci ta soma jin motsi a dakin ta wanda yayi silar farkar da ita, tayi zaton pravin ne Ya shigo shiyasa batai yunkurin tashi ba sai ma ta ƙara gyara kwanciyarta, kwatsam kamar daga sama tajiyo ƙarar faɗuwar wani abun firgigit ta zabura zaune tana faman zare idanunta jikinta Ya hau 6ari ta fara laluban fitila zata kunna hasken ɗakin, akan kunnanta taji takun tafiyar mutun adai dai lokacin ta samu damar kunna light din kamar walkiya taga gifcin mutun Ya lullu6e jikinshi da bargo, wata irin zufa ce ta keto mata numfashinta na hauhawa take kallon ƙofar cike da mamakin wanene Ya shigo? don kwata kwata baiyi kama da pravin ba...

Wurga ido tai akan tsakar dakin bakhhoor burner din da take ajiyewa kan mirror shi ta gani kan floor daga gani kado shi akai

Lamarin Ya ɗaure mata kai, saukowa tay daga kan gadon ta, gaba ɗaya tsoro Ya kamata, dama ƙwarin gwiwarta pravin ne gashi baya nan Yana can dakin Hajiya saratu.

Tayi mamakin ganin bedside drawer dinta a buɗe, zukunna tayi gaban drawer din yatsun hannunta na kerma ta curo album din dake a ciki mai ɗauke da hotunan auransu, cike da tashin hankali take bubbuɗe su ganin ba'a ɗauki hoton Ba Yasa Hankalinta Ya ɗan kwanta, da sauri ta mike taje taja ƙofar ta datse, ta sanya key

Komawa tayi gefe gado ta zauna har time din jikinta bai daina 6ari ba gani take kamar wani mugun abunne zai faru da ita, tun da gashi har an fara kawo mata hari adakin ta, Allah Allah take gari ya waye pravin yazo don ta faɗa masa abun da ya faru

______________________BATOOL✍️

Tsakar dare ta farka sakamakon fitsari da ya matse ta, saukowa tayi daga kan gado

Miƙa tayi kafin ta nufi toilet din tana dab da zata shiga, tajiyo sautin murya ƙasa ƙasa Ana magana har sai da taji gabanta Ya ɗan faɗi da sauri ta kalli gadon su duk a tsammanin ta ummi tana akwance ashe bata nan fululluka ta lullu6e da bargonta sai yai kamar mutun na akan gadon

Kanga kunne tayi don ta ƙara tabbatarwa da kanta muryar waye take ji ƙasa ƙasa kamar ana raɗa

"Kaima kasan bazan ta6a yin kuskuren da wani zaisan ina a tare da kai ba, yanzu haka da nake Yi maka magana ina a cikin toilet saboda bani kaɗai bace a ɗakin, akwai ɗaya daga cikin yaran da muke kula da su, Yarinyar tana sona, a tare muke kwana da ita........"

Ɗagowa batool tayi da kanta, Idanunta aɗan zare babban abun da take jima tsoro da wa aunty ummi take magana a tsakar daren nan kuma acikin toilet? Wanene? Da har take faɗin bata son asan tana waya da shi?

Gaba ɗaya tashiga ruɗani, Ƙara kanga kunnan tay jikin ƙofar

"Bazai yiwu ba, Ni Bazan Iya yakice ta daga gare ni ba, na faɗa maka Yarinyar bata da matsala, she is innocent bayan haka bata da wayon da har za ta sanya min ido..."

"Meyasa baka son kowa Yasan Ina atare dakai? kamar wani mara gaskiya kodai bakasan sunan ka Ya 6aci ne a idon jama'a"?

Ta sake ji ummi ta faɗa, can kuma sai tajiyo tayi wani sauti mai kama da nishi nishi da jan numfashi

Kwatsam tari Ya kubcewa batool waro idanu tayi kafin jiki na 6ari ta watsa aguje ta kashe light din dakin ta haye kan gado ta ja bargo ta lullu6e tana faman sauke ajiyar zuciya

A fujajen Ummi ta fito daga toilet din, yar rigar bacci ce a jikinta shara shara, kai tsaye ta sauke idon ta kan gadon, ganin batool a kwance tana bacci Yasa ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya, juyawa tayi ta koma cikin toilet din taja kofa ta datse

Batool dake a kudundu ne cikin bargo jin alamun ta rufe kofarne Yasa ta ƙara jin hankalinta Ya kwanta, ta kudiri aniyar saita faɗa ma Unaisah maganar da aunty umminsu keyi a toilet, saboda ta tsorata gani take kamar akwai wani abu a ƙasa duk da bata zarginta.
Chapter 77 · 0% Book details