← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 238

Sashe 128

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK

COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
Our website uses cookies to improve your experience. Learn more

Accept !
[14/10, 6:06 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Novels Elite

Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe chapter 42 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 05, 2024
Takun Ƙarshe

Boss Bature

A kishingiɗe yake saman lallausan rug din dakin baba obie ya ɗaura head dinsa kan pillow, jikinshi na sanye da jallabiya fara kyal, fragrance dinsa ya haɗe da sanyin A.c din dakin, ba su jima da dawowa daga sallar asuba ba yabiyo baba obie dakin shi...A hankali yake danna phone dinsa Kira ne ya shigo ganin sunan commender james yasa shi picking call din tare da kara wayar a kunne, cikin girmamawa suka gaishe da junansu kafin daga bisani commender james ya sanar da shi sun samu izni daga manyan su, za su shigo Nigeria da shi da sauran sojojin da suka tsinci su Angel a dajin evil forest

Chief yace"I'm very happy to hear that, I can't wait to see you"

Commender james yace"I'm also very happy, this is the first time I'll be coming to Nigeria because of the children we found in the forest, naji dadi saboda abun alfahari ni agare ni"

sun ɗan jima suna tattaunawa kafin daga bisani su ka yi sallama da juna.

Fitowa baba obie yayi daga toilet, jikinshi sanye da jallabiya fara, ya dago da ido ya dubi owais fuskarshi da fara'a yace"jikallena, nabarka zaune kana jira na, uziri ne ya ruƙe ni a ciki" dagowa chief yai tare da kallon shi suka haɗa ido da juna"barka da fitowa,"

"Yawwa owaisu na, fadamin me kakeson ci insa akawo mana, yau atare zamu yi breakfast.."

ya faɗa yayin da yake nufar bedside drawer chief yace"duk abunda kakeson ci nima shi zan ci "

Landline din kitchen baba obie ya kira, bayan an daga kiran ya isar da sakon abunda za'a kawo masu na breakfast bayan ya ajiye wayar

Ya samu guri kan lallausar rug din ya zauna haɗi da daura kan shi saman laps din chief yadda kasan uba da ɗansa.

ya ɗago ya kalli fuskar Owais dake kokarin saita shi da phone camera"me zaka min haka"?

"Hoto zan ɗauke ka, naga ka yi min kyau"

murmushi baba obie ya sakar mashi"duk kyau na nakai ka"?

"Eh mana, mu da mukai gado agurin ka, gaba ɗaya kamanninka muka ɗauko"

Saurari Littafin >>>>Kurkukun Ƙaddara Takun farko Kada a manta ayi mana subscribe like da kuma comment sannan a yi share. Domin samun sabbin littafi idan Mun ɗora.
"Na tsufa owais, yanzu babu wannan kyan da kake faɗin ina da shi"

"Kai kake ganin haka, ni tun da na taso rayuwata ban ta6a ganin mutumin daya tsufa da kyan shi irinka ba" ƙayataccen murmushi baba obie ya saki yana kallon fuskar chief, yaji dadin kalaman shi sun faranta ran shi.

"Baba, ɗazu kace zamuyi magana, ya fada bayan ya kammala daukar shi hoton.

shigowar hajjaty dakin ne ya katse firar su, ta ɗauki wankan material, hannunta ruƙe da tray na kayan breakfast dinsu agabansu ta ajiye tray din cikin girmamawa ta gaishe da su suka amsa mata har ta juya zata fuce daga dakin muryar baba obie ta dakatar da ita.

"Ya jikin marwa"?

"Da sauƙi baba,"

"Okey, ubangiji Allah ya bata lafiya" ta amsa mashi da ameen bayan ta fuce daga dakin chief ya dubi baba obie"wacece marwa"?

Ba halinsa bane tambayar abunda bai shafe shi ba, just saboda yaji ya ambaci ya jikin ta.

"Ɗaya daga cikin masu aikin gidan nan ce, bata da lafiya" iya abunda ya fada masa kenan saboda baison ya ɗaga mashi hankali, kamar yadda su twins sukai hijra saboda kyamar marwa.

"Allah ya bata lafiya" ya amsa mashi da ameen

Tea pot baba obie ya dauka ya tsiyaya masu shayi a kananun kofuna suka dauka suna sha

"Ka tambaye ni dangane da maganar da nace maka inaso muyi ko" ɗaga mashi kai yai alamar eh

"Nasan bazaka ji dadi ba, amma kada ka hanani tafiya" janye cup din hannunsa yai daga kan lips dinsa"tafiya zakayi"! Jinjina mashi kai yayi"lagos nakeson zuwa gurin aminina, kasan na daɗe ban ziyarce shi ba, kuma shi yana kokarin zuwa akai akai ya dubani har gida" jinjina kai chief yai"yaushe ne zaka tafi"?

"Karshen watan nan, 3 weeks zanyi in dawo" ɗaure fuska chief yayi"har sati uku baba, ina laifin one week" murmushi yayi"dama sai da nayi fargaban fada maka nasan da wuya ka kyale ni, indai bazaka barni ba to saidai muje atare" girgiza kai chief yayi"ba zan iya binka ba, naso muje atare amma ayyuka sunyi min yawa, amma fa bazan bari ka tafi kai kadai ba,"! Yamutsa fuska baba obie yai"to ni da wa zan tafi owais? Kowa yana da aikin yi, bana son in takura masu"

Shiru yayi jim kafin yace"zanyi magana da pravin, ya ɗauki hutun aiki Ya bika ku tafi, don gaskiya ni bazan bari ka tafi kai kadai ba"

"Haba owais kamar wani karamin yaro, sai kace bakasan wanene kakan naka ba, waɗannan kafafuwan nawa ba inda basu taka ba, har birnin sin sunje, nafa yi yawan duniya fiye da tunaninka, tun ina matashina nake fita kasashen waje ni kadai abuna."

Murmushi chief yayi"da da yanzu ba ɗaya ba, ka manyanta sosai ga tsufa, shiyasa nake tattalinka bana son wani abu ya same ka, duk da nasan Allah ke tsare bawansa."

kalaman chief sun kara faranta ranshi murmushi yayi yana kallon fuskar shi"anya akwai wanda yakaini dacen jika a duniyar nan"? chief yace"ni yakamata nayi wannan tunanin, cos bana tunanin akwai wanda yayi dacen kaka irina, ina alfahari dakai," dariyar farin ciki baba obie yasaki idan owais na yabon shi dadi yake ji kamar ya zuba ruwa kasa ya sha.

"Owais Mu fara cin abincin nan kada ya huce.." Chief ne yayi serving dinsu atsanake suke cin abinci ya lura duk dagowar da zaiyi sai sun haɗa ido da baba obie wani kallon so da kauna yakeyi mashi.

"Naga kana kallona, ba zan canza maganata ba, zanyi magana da pravin din atare zaku je nasan zai baka kulawa ta musamman kuma zai dinga sanar dani duk wani motsinka" dariya baba obie yayi"oh ɗan leken asiri zaka hada ni da shi kenan" ɗaga mashi gira chief yayi"bakomai nasan saboda kaunar da kake yi min ne, naji na amince muje atare da shi din" ya fada yayin da yake tura abinci abakin shi.

Knocking room door din akay daga waje, baba obie yace shigo ciki"

muryar hajiya saratu ce ta katse masu cin abincin nasu, atare suka dago suna kallonta, shugowa tayi jikinta sanye da swiss code lace, idanunta sanye da farin glass, ta aza veil a kafadarta, ta kashe daurin ture kaga tsiya, hannunta na aruke da handbag dinta.

Kwata kwata babu annuri akan fuskarta saida taga chief ta ɗan saki fuskarta.

"Shalelena barka da safiya, har anyi shirin xuwa office.. " murmushi ta sakar mashi"barka da safiya babana, ina fata ka tashi lafiya" tay maganar tare da samun guri ta zauna tana fuskantar su..

"Lafiyalou auta,"

"Barka da safiya auntyna, kin tashi lafiya? murmushi tasakar ma chief da fara'a tace"lafiyalou my son, ina fata kaima haka ya aiki"?

Yace"Alhamdulillah"

"I'm sorry na shiga busy, kwanaki nace zan shiga asibiti in duba patient din nan banje ba, Ya jikin nata? Ya kuma babynta Unaisah ina fata suna lafiya"? cikin kulawa tayi maganar tana duban shi.

"She's feeling better, almost 3 days da sallamarta, unaisah tana lafiya"

"Masha Allah, naji dadin jin hakan"

tun da suka fara magana baba obie ke kallonsu cike da mamakin taya akai suka sasanta tsakaninsu, shi dai yasan tsakanin jikallan nasa da autarsa ba sa jituwa.

gaba ɗaya sun fahimci kallon da yakeyi masu, murmushin gefen fuska ya saki har cikin ranshi yaji dadin shiryawarsu"tun yaushe kuka sulhunta tsakaninku bansani ba"? Ya faɗa yana kallon su

Murmushin dattako hajiya saratu tayi batare data furta kalma ba, chief ne ya bashi amsa da cewa"me ka gani baba?

Nuna su yayi da yatsan shi"ga abunan azahiri, ku fadamin wani ɗan arzikin ne ya hadamin kanku? Ni dai nasan baku jituwa"

tattausan murmushi sukayi

Hajiya saratu tace"Allah ne ya hada kanmu, dama can shaidan ne ya shiga tsakaninmu amma muna kaunar juna, ko ba haka ba my son" ta faɗa tana kallon shi

"Hakane baba, kuma in sha Allah ba za'a kara jin kanmu ba" har cikin ranshi yaji dadin maganarsu, dama baya son sabanin da suke samu atsakaninsu.

"Alhamdulillah, naji dadi ubangiji Allah ya cigaba da hada mun kanku, Allah ya kara dankon zumunci atsakaninku, shi kuma shaidanin daya shiga tsakaninku Allah Ya kare mu daga sharrinsa"

A tare suka amsa mashi da ameen, kwata kwata baiyi masu maganar mara lafiyan dayaji sun ambata ba, hankalin shi ya karkata akan jituwar da suka samu.

Miƙewa chief yayi da sauri baba obie yace"Grandson ina zuwa bamu gama yin breakfast ba"?

"I'm sorry, Grandpa. I'll come back later"
Chapter 128 · 0% Book details