Sashe 179
Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read
saukowa sukayi daga kan gadon da sauri Gabriella ta shige karkashin gadon, ba laifi Yana da faɗi da tsawo, kamar ƙaramin ɗaki, tayi mamakin ganin buhun huna kusan Biyar a karkashin gadon ga wasu akwatinan ƙarfe, jikinta na kerma amma saboda karanbani saida ta yi kokarin kwance buhun don ta ga menena aciki, Sai dai takasa saboda mugun ɗaurine akayi masu, tatta6a jikin buhun tayi sai taji kamar Makamai ne a cikin su...
Komawa tsohuwa khala tayi kan gadon ta kwanta tare da lumshe idanunta, zuciyarta cike fal da fargaban abun da zai biyo baya don tasan muddin Elder ya ƙaraso adakinta zai huce gajiyar shi.
bakomai yafi damunta ba face zuwan Garkuwa, Allah Allah take su karaso saboda batason Elders suyi nasarar Salwantar da rayuka a wannan daren, In har daren yau ya wuce Bata cimma burinta ba, bata jin zata Iya jure rayuwa adoron duniyar nan, saboda in har ta kuskura asirin ta Ya tonu na abunda take kullawa Allah kadai Yasan Mummunan hukuncin da zasuyi mata, donma saukinta daya Elder Yana Ji da ita.
Bata kare zancen zucinta ba, Kamar daga sama Taji dirar wani abu adakinta,
Sautin shu'umar dariyar shi ce ta karaɗe kunnuwanta, Tuni tasha jinin jikin ta.
"Da wata irin Murya irin ta tantiran ƴan'duniya Ya furta"Idan ma bacci kike, toh ki farka..." yunkurawa tayi ta miƙe zaune, tare da kai dubanta gare shi, Yana atsaye cikin wata rantsattsiyar alkebba launin Ja mai adon duwatsu irinta sarakuna..ya lullu6e kanshi da hular alkyabbar, rabin fuskarshi arufe yake da takuntumi, kafafunshi suna asanye da wasu hadaddun takalma na alfarma, yayin da hannunsa ke aruke da sanda ta zallar Zinari.
ba'a Iya ganin fatar jikin shi saboda ya lullu6e ko'ina hatta yatsun hannunsa safa ya sanya masu.
Gabriella dake labe ta kasa kunne tana sauraronsu, da ga inda take tana Iya hangen kafafuwan Elder..
"Taya zan Iya bacci batare dana sanyaka acikin idanuna ba, tun bayan daka tafi kabarni da kewarka, idanuna sunyi maraicin ganin ka, sanyin idaniyata, mijina uban ya'yana, sarki ɗaya tak da ke mulkar zuciyata..." cike da qasaita yake sakin dariya yayin da yake tinkarar gadonta cike da dattako yake taka matakalar gadon.
"Meyasa soyayyar mu bata tsufa ne? Aduk lokacin dana ganki sai inji kamar ana rura wutar sonki a cikin zuciyana, bazan Iya misalta kewarki da nayi ba.
yayin da yakeyin maganar, wani irin kallo khala take binsa da shi mai wuyar fassaruwar, ta tsane shi fiye da yadda ta tsani mutuwarta, shine silar komai 💔
gaba daya tayi zurfi a tunaninta sam ta manta da shi akusa daita, batai aune ba taji ya janyota jikin shi, wani ɗaci taji aranta, sai taji kamar ta hada jikinta da wuta saboda tsanar da tayi mashi..
Sumbatar kuncinta yayi, cikin wani irin salo ya fara sarrafa ta.
Gabriella dake la6e a karkashin gadon, gabanta sai faduwa yakeyi ganin yadda gadon ke girgiza kamar zai rubzo mata, gani take kamar mutumin dayazo ne ke cutar da Khala.
kasa jurewa tayi duk tabi ta rude jikinta sai kakarwa yakeyi bata san sa'adda ta saki ƙara ba, da sauri ta toshe bakinta da tafukan hannayenta.
Lokaci ɗaya Elder Ya raba jikin shi daga na Khala, ido cikin ido suke kallon juna..tun daga yanayinta ya fahimci akwai wani abu da take boye masa.
Kamar daga sama taji Ya furta"kamshin mutum nake ji adakin nan..." arazane ta ware idanunta akan fuskar shi, jinjina mata kai yayi
"Ke da wanene Kuke rayuwa adakin nan? Kuma Yana ina"? Ji tayi kamar ta fasa ihu saboda tashin hankali, batasan ya akai ya gane akwai mutun ba..
.
"Kinyi shiru baki bani amsa ba, Ko kin bani za6i In gano da kaina"?
Yawu mai daci ta hadiya muryarta na rawa tace"bakowa, Ni kadai ce, nayi mamaki da naji kace kaji kamshin mutun bayan ni kadai ce mutum da ke rayuwa a cikin dakin nan.."
"baki saba min karya ba, Amma yau kinyi min, kinsan na tsani makaryaci, saboda alamace dake nuna mutun zai Iya cin amanarka wata rana"
idanunta ne suka ciko tab da kwallo, cikin sanyin murya tace"ka yi hakuri, na gane kuskurena, kasan ba halina bane, dama yarince daga cikin prisoners, inason yarinyar ne shiyasa na taimake ta..."
tun kafin ta kare maganar Ya daka mata tsawa a faɗace Ya furta"meke damunkine? Kina cikin hayyacinki kuwa? Kin manta gargadin da nayi maki?
Kamar ƙaramar yarinya ya rufe ta da faɗa.
"Ki rasa wa zaki kawo cikin dakina sai ƙasƙantacciya Prisoner? Ɗakin Elder? kefa sirrina ce, sai da na fada maki banaso kowa ya rabeki in bani ba"
kokarin bashi hakuri tayi, ko kallo bata ishe shi ba, saukowa yayi daga kan gadon da kakkausar murya ya furta"Tana ina"! Jiki na rawa tsohuwa Khala ta sauko daga kan gadon.
"Pls kada ka rabani da ita, Inasonta, wallahi bada wata manufa na ajiyeta adakin nan ba.." magiya ta dinga yi mashi amma dayake zuciyar irin ta fir'auna ce ko kadan bai saurare ta ba.
Tsoro Ya hana Gabriella fitowa, kirjinta kamar ana luguden ta6are..
"Zaki fito da kafafuwanki, ko kuwa Ni kikeso In fito dake..." cikin karyayyar murya khala ta kira sunanta..
Jiki asanyaye ta fito daga karkashin gadon, wani dan iskan kallo Elder yabita da shi, farat ɗaya Ya gane ƴar wacece.
Dariyar shaƙiyanci Ya saka kafin Yace"wannan Ay yar gurin Jan wuya ce, sadaukarwar Jini ce, bazan Iya barmaki ita ba, dama wata ce daban, Ko ubanta Yaji kin dauke ta sai yazo ya kar6eta ya mayar da ita cikin prisoners, kinga kuwa babu amfanin boyeta agurin ki...."
Gabriel ta ruɗe da jin maganar shi, ta fashe da kuka, idanunta akan fuskar Khala dake kallon ta.
cikin shesshekar kuka tace"kada ki bari arabani dake, kashe ni zasuyi, bana so na koma gurin su, kada ki manta da alkawarin da kikayi min pls...."
Da kallon tuhuma Elder Ya dubi Khala"wani alkawari ne kikayi mata"
"Zan hada ta da ɗan uwanta" ta fada rai a6ace..
"Ku shigo ku dauke ta" suka ji ya fada, kafin wani Ya furta kalma sai ga Giants biyu karfafa sun fado cikin ɗakin, wani irin faduwar gaba Gabriella taji, jikinta na bari kamar mazari ta la6e bayan Khala, ta rurruke hannunta tanayi mata magiya kan kada ta bari su tafi da ita.
shiru khala tayi jikinta yayi sanyi lakwas, Zuciyarta ta karaya.
"Ku maida ta, Cikin Ƴan uwanta,"
Duk yadda Gabriella taso ta kubce masu abun yaci tura, tana ji tana gani suka nuna mata fin karfi akan idonta Giants suka fuce da Gabriella...
Jiki asanyaye ta koma kan kujera ta zauna, idanunta suka cicciko tab da kwalla...
Matsawa yayi kusa da ita tare da sunkuyar da kanshi gab da fuskarta"fushi kike dani"? Ya faɗa tare da ɗage mata gira..
*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥✍️*
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08169856268 ko 08103884440*
[14/10, 6:06 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: _______________________________✍️🔥💋💔🫀🌹☠️❓😈👹💞💘
Yar dariyar takaici ta yi, "Elder kenan, ka jima kana nuna min fin ƙarfi, wlh tun ranar dana gane asalin wa nene kai, na ji ka fita araina, wlh na tsaneka kamar mutuwa, babu abunda nake kwaɗayi da ya wuce inga bayanka, dan Allah ka mutu mana, na gaji ! na gaji !! da irin baƙincin da kake ƙunsa mini, wai kai wani irin mutunne? ko sau ɗaya baka ta6a jin nadamar irin zunubban da kake aikatawa ba? Na jima ina kokwanton anya kai mutunne? Saboda babu zuciyar imani a ƙirjinka... "
Bata ƙare maganar ba, ya daka mata tsawar da tayi silar rikicewarta tuni tasha jinin jikinta, nuna ta yayi da yatsan shi, "Bansan a ina kika samu ƙwarin gwiwar gaya min magana cikin idona ba, koda yake dama haka kike da kafiyar tsiya, ke kin sani bada son raina na jefa ki cikin kurkukun nan ba, kece sila, shisshiginki da bin kwakkwafinki ne suka ja maki, naso mu dawwama acikin farin ciki amma kin 6ata komai, wallahi ba don son da nake maki ba da tuni najima da kashe ki, amma saboda ƙaunar da nake maki shiyasa na killaceki anan saboda kada ki tona min asirina..."
Cike da taikaici ta yi murmushi haɗi da ɗan girgiza kai ta ce, "Ai ni tuni kajima da kashe ni, me kuma ya rage? Tsawon shekaru ashirin rabona da inga hasken rana, tsawon shekara ashirin rabona da inga wani dangina, dan Allah ka kashe ni in huta, na roƙe ka Ka kashe ni mana...!" cikin jin kunar rai ta faɗa.
Lumshe idanunshi yayi akan fuskarta tare da buɗe su, da wata irin siga ta jan hankali yace,
"Idan na kashe ki, kamar na kashe kaina ne, nafison in ma mutuwar zakiyi mu mutu atare."
"Elder kenan, makomarmu ba zata ta6a zama ɗaya ba, ni da nake so In mutu Cikin rahamar ubangiji, taya za kai min fatan mu mutu atare?"
Tuntsirewa ya yi da dariya, cike da tsana take kallon shi....
"Bazan bari ki 6ata min ranata ba, yau ina cikin farin cikin zagayowar ranar da muka kafa gidan kurkukun ƙaddara, ko murna baki tayani ba..."
Wani kallon rainin wayau ta jefa ma shi a cikin ranta ta furta, "In Sha Allah yau ce rana ta ƙarshe da zaku yi black night a duniya, Ubangiji Allah Yasa su kawo maku farmaki su tarwatsa tawagar azzalumai..."
"Me kika ce?" Firgigit ta kalle shi cike da fargaban kada ace Yaji ta, duk da ta dai san a zuciya tayi maganar amma tasan yana iya karantar abunda take saƙawa acikin zuciyarta.
"Kaji nayi magana ne?" Girgiza mata kai yayi.
"Ni zan Shiga fadata, ko zaki raka ni?" Banza tayi da shi,
"Ki kula min da kanki." Bai tsaya yaji amsarta ba, Ya 6ace ma ganin ta..
Me ya faru bayan Giants sun tafi da Gabriella?
Tana ta kuka tana tirjewa, a haka suka miƙi hanyar komawa cikin Kurkukun da ita, adaidai zasu karya wata kwana kwatsam saiga Tsohuwa Inno ta fito daga fadar elders karaf idanunta suka hango mata Gabriella...
A sukwane ta dakata da yin tafiya ta zuba mata idanu, yarinyar da take nema ruwa ajallo sai gata yau Allah Ya haɗasu..
Komawa tsohuwa khala tayi kan gadon ta kwanta tare da lumshe idanunta, zuciyarta cike fal da fargaban abun da zai biyo baya don tasan muddin Elder ya ƙaraso adakinta zai huce gajiyar shi.
bakomai yafi damunta ba face zuwan Garkuwa, Allah Allah take su karaso saboda batason Elders suyi nasarar Salwantar da rayuka a wannan daren, In har daren yau ya wuce Bata cimma burinta ba, bata jin zata Iya jure rayuwa adoron duniyar nan, saboda in har ta kuskura asirin ta Ya tonu na abunda take kullawa Allah kadai Yasan Mummunan hukuncin da zasuyi mata, donma saukinta daya Elder Yana Ji da ita.
Bata kare zancen zucinta ba, Kamar daga sama Taji dirar wani abu adakinta,
Sautin shu'umar dariyar shi ce ta karaɗe kunnuwanta, Tuni tasha jinin jikin ta.
"Da wata irin Murya irin ta tantiran ƴan'duniya Ya furta"Idan ma bacci kike, toh ki farka..." yunkurawa tayi ta miƙe zaune, tare da kai dubanta gare shi, Yana atsaye cikin wata rantsattsiyar alkebba launin Ja mai adon duwatsu irinta sarakuna..ya lullu6e kanshi da hular alkyabbar, rabin fuskarshi arufe yake da takuntumi, kafafunshi suna asanye da wasu hadaddun takalma na alfarma, yayin da hannunsa ke aruke da sanda ta zallar Zinari.
ba'a Iya ganin fatar jikin shi saboda ya lullu6e ko'ina hatta yatsun hannunsa safa ya sanya masu.
Gabriella dake labe ta kasa kunne tana sauraronsu, da ga inda take tana Iya hangen kafafuwan Elder..
"Taya zan Iya bacci batare dana sanyaka acikin idanuna ba, tun bayan daka tafi kabarni da kewarka, idanuna sunyi maraicin ganin ka, sanyin idaniyata, mijina uban ya'yana, sarki ɗaya tak da ke mulkar zuciyata..." cike da qasaita yake sakin dariya yayin da yake tinkarar gadonta cike da dattako yake taka matakalar gadon.
"Meyasa soyayyar mu bata tsufa ne? Aduk lokacin dana ganki sai inji kamar ana rura wutar sonki a cikin zuciyana, bazan Iya misalta kewarki da nayi ba.
yayin da yakeyin maganar, wani irin kallo khala take binsa da shi mai wuyar fassaruwar, ta tsane shi fiye da yadda ta tsani mutuwarta, shine silar komai 💔
gaba daya tayi zurfi a tunaninta sam ta manta da shi akusa daita, batai aune ba taji ya janyota jikin shi, wani ɗaci taji aranta, sai taji kamar ta hada jikinta da wuta saboda tsanar da tayi mashi..
Sumbatar kuncinta yayi, cikin wani irin salo ya fara sarrafa ta.
Gabriella dake la6e a karkashin gadon, gabanta sai faduwa yakeyi ganin yadda gadon ke girgiza kamar zai rubzo mata, gani take kamar mutumin dayazo ne ke cutar da Khala.
kasa jurewa tayi duk tabi ta rude jikinta sai kakarwa yakeyi bata san sa'adda ta saki ƙara ba, da sauri ta toshe bakinta da tafukan hannayenta.
Lokaci ɗaya Elder Ya raba jikin shi daga na Khala, ido cikin ido suke kallon juna..tun daga yanayinta ya fahimci akwai wani abu da take boye masa.
Kamar daga sama taji Ya furta"kamshin mutum nake ji adakin nan..." arazane ta ware idanunta akan fuskar shi, jinjina mata kai yayi
"Ke da wanene Kuke rayuwa adakin nan? Kuma Yana ina"? Ji tayi kamar ta fasa ihu saboda tashin hankali, batasan ya akai ya gane akwai mutun ba..
.
"Kinyi shiru baki bani amsa ba, Ko kin bani za6i In gano da kaina"?
Yawu mai daci ta hadiya muryarta na rawa tace"bakowa, Ni kadai ce, nayi mamaki da naji kace kaji kamshin mutun bayan ni kadai ce mutum da ke rayuwa a cikin dakin nan.."
"baki saba min karya ba, Amma yau kinyi min, kinsan na tsani makaryaci, saboda alamace dake nuna mutun zai Iya cin amanarka wata rana"
idanunta ne suka ciko tab da kwallo, cikin sanyin murya tace"ka yi hakuri, na gane kuskurena, kasan ba halina bane, dama yarince daga cikin prisoners, inason yarinyar ne shiyasa na taimake ta..."
tun kafin ta kare maganar Ya daka mata tsawa a faɗace Ya furta"meke damunkine? Kina cikin hayyacinki kuwa? Kin manta gargadin da nayi maki?
Kamar ƙaramar yarinya ya rufe ta da faɗa.
"Ki rasa wa zaki kawo cikin dakina sai ƙasƙantacciya Prisoner? Ɗakin Elder? kefa sirrina ce, sai da na fada maki banaso kowa ya rabeki in bani ba"
kokarin bashi hakuri tayi, ko kallo bata ishe shi ba, saukowa yayi daga kan gadon da kakkausar murya ya furta"Tana ina"! Jiki na rawa tsohuwa Khala ta sauko daga kan gadon.
"Pls kada ka rabani da ita, Inasonta, wallahi bada wata manufa na ajiyeta adakin nan ba.." magiya ta dinga yi mashi amma dayake zuciyar irin ta fir'auna ce ko kadan bai saurare ta ba.
Tsoro Ya hana Gabriella fitowa, kirjinta kamar ana luguden ta6are..
"Zaki fito da kafafuwanki, ko kuwa Ni kikeso In fito dake..." cikin karyayyar murya khala ta kira sunanta..
Jiki asanyaye ta fito daga karkashin gadon, wani dan iskan kallo Elder yabita da shi, farat ɗaya Ya gane ƴar wacece.
Dariyar shaƙiyanci Ya saka kafin Yace"wannan Ay yar gurin Jan wuya ce, sadaukarwar Jini ce, bazan Iya barmaki ita ba, dama wata ce daban, Ko ubanta Yaji kin dauke ta sai yazo ya kar6eta ya mayar da ita cikin prisoners, kinga kuwa babu amfanin boyeta agurin ki...."
Gabriel ta ruɗe da jin maganar shi, ta fashe da kuka, idanunta akan fuskar Khala dake kallon ta.
cikin shesshekar kuka tace"kada ki bari arabani dake, kashe ni zasuyi, bana so na koma gurin su, kada ki manta da alkawarin da kikayi min pls...."
Da kallon tuhuma Elder Ya dubi Khala"wani alkawari ne kikayi mata"
"Zan hada ta da ɗan uwanta" ta fada rai a6ace..
"Ku shigo ku dauke ta" suka ji ya fada, kafin wani Ya furta kalma sai ga Giants biyu karfafa sun fado cikin ɗakin, wani irin faduwar gaba Gabriella taji, jikinta na bari kamar mazari ta la6e bayan Khala, ta rurruke hannunta tanayi mata magiya kan kada ta bari su tafi da ita.
shiru khala tayi jikinta yayi sanyi lakwas, Zuciyarta ta karaya.
"Ku maida ta, Cikin Ƴan uwanta,"
Duk yadda Gabriella taso ta kubce masu abun yaci tura, tana ji tana gani suka nuna mata fin karfi akan idonta Giants suka fuce da Gabriella...
Jiki asanyaye ta koma kan kujera ta zauna, idanunta suka cicciko tab da kwalla...
Matsawa yayi kusa da ita tare da sunkuyar da kanshi gab da fuskarta"fushi kike dani"? Ya faɗa tare da ɗage mata gira..
*DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE🔥✍️*
*Ga me bukatar karanta littafin kurkukun kaddara, 500 ne za'a tura Via Opay, 8103884440 Hafsat Bature Muhammad, shaidar biya za'a tura ta whatsapp, 08169856268 ko 08103884440*
[14/10, 6:06 PM] Amin@ M Yusuf Yol@: _______________________________✍️🔥💋💔🫀🌹☠️❓😈👹💞💘
Yar dariyar takaici ta yi, "Elder kenan, ka jima kana nuna min fin ƙarfi, wlh tun ranar dana gane asalin wa nene kai, na ji ka fita araina, wlh na tsaneka kamar mutuwa, babu abunda nake kwaɗayi da ya wuce inga bayanka, dan Allah ka mutu mana, na gaji ! na gaji !! da irin baƙincin da kake ƙunsa mini, wai kai wani irin mutunne? ko sau ɗaya baka ta6a jin nadamar irin zunubban da kake aikatawa ba? Na jima ina kokwanton anya kai mutunne? Saboda babu zuciyar imani a ƙirjinka... "
Bata ƙare maganar ba, ya daka mata tsawar da tayi silar rikicewarta tuni tasha jinin jikinta, nuna ta yayi da yatsan shi, "Bansan a ina kika samu ƙwarin gwiwar gaya min magana cikin idona ba, koda yake dama haka kike da kafiyar tsiya, ke kin sani bada son raina na jefa ki cikin kurkukun nan ba, kece sila, shisshiginki da bin kwakkwafinki ne suka ja maki, naso mu dawwama acikin farin ciki amma kin 6ata komai, wallahi ba don son da nake maki ba da tuni najima da kashe ki, amma saboda ƙaunar da nake maki shiyasa na killaceki anan saboda kada ki tona min asirina..."
Cike da taikaici ta yi murmushi haɗi da ɗan girgiza kai ta ce, "Ai ni tuni kajima da kashe ni, me kuma ya rage? Tsawon shekaru ashirin rabona da inga hasken rana, tsawon shekara ashirin rabona da inga wani dangina, dan Allah ka kashe ni in huta, na roƙe ka Ka kashe ni mana...!" cikin jin kunar rai ta faɗa.
Lumshe idanunshi yayi akan fuskarta tare da buɗe su, da wata irin siga ta jan hankali yace,
"Idan na kashe ki, kamar na kashe kaina ne, nafison in ma mutuwar zakiyi mu mutu atare."
"Elder kenan, makomarmu ba zata ta6a zama ɗaya ba, ni da nake so In mutu Cikin rahamar ubangiji, taya za kai min fatan mu mutu atare?"
Tuntsirewa ya yi da dariya, cike da tsana take kallon shi....
"Bazan bari ki 6ata min ranata ba, yau ina cikin farin cikin zagayowar ranar da muka kafa gidan kurkukun ƙaddara, ko murna baki tayani ba..."
Wani kallon rainin wayau ta jefa ma shi a cikin ranta ta furta, "In Sha Allah yau ce rana ta ƙarshe da zaku yi black night a duniya, Ubangiji Allah Yasa su kawo maku farmaki su tarwatsa tawagar azzalumai..."
"Me kika ce?" Firgigit ta kalle shi cike da fargaban kada ace Yaji ta, duk da ta dai san a zuciya tayi maganar amma tasan yana iya karantar abunda take saƙawa acikin zuciyarta.
"Kaji nayi magana ne?" Girgiza mata kai yayi.
"Ni zan Shiga fadata, ko zaki raka ni?" Banza tayi da shi,
"Ki kula min da kanki." Bai tsaya yaji amsarta ba, Ya 6ace ma ganin ta..
Me ya faru bayan Giants sun tafi da Gabriella?
Tana ta kuka tana tirjewa, a haka suka miƙi hanyar komawa cikin Kurkukun da ita, adaidai zasu karya wata kwana kwatsam saiga Tsohuwa Inno ta fito daga fadar elders karaf idanunta suka hango mata Gabriella...
A sukwane ta dakata da yin tafiya ta zuba mata idanu, yarinyar da take nema ruwa ajallo sai gata yau Allah Ya haɗasu..