← Book details Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 136 OF 238

Sashe 136

Kurkukun Kaddara Takun Karshe Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Okay, bana son kizo da kowa, ke kaɗai zaki zo..."

"Amma daddy suna son ganin baby junaid, na riga na fada masu mun hadu da aunty anila kuma sun kwallafa rai da son ganin ta"

"Look, kija baki kiyi shiru, kada ki fada masu game da zuwanta, kin riga da kinsan komai ba sai nayi maki bayani ba, idan har yaran nan suka zo zasu iya furta wata kalma da zaisa agane wani abu game daku, kuma hakan ya sa6ama dokar aikin mu, shiyasa nace kizo ke kadai, ke ma din dakyar na samu chief ya amince su ganki, Ina fata kin fahimce ni"? Shiru tayi da alama bata ji dadi ba

Fahimtar yanayin ta yasa shi sassauta muryar shi"Idan ki ka kwantar da hankalin ki, next time zasu sake dawowa ne in yaso sai su hadu da su"

ajiyar zuciya ta sauke"toh daddy, na fahimce ka, amma ya zanyi da batool? Ta riga da taji komai, namanta tana adakin, dan Allah daddy kabari in zo da ita"

shiru yayi baice mata komai ba

"Daddy, naji kayi shiru, pls ita kadai, batool ba zata bamu matsala ba, tana da hankali, zan ja mata kunne akan kada ta furta komai da zaisa su san wani abu dangane da rayuwar mu, nasan zata fahince ni"

Numfasawa yai kafin yace"ya zanyi dake tunda kin matsa akan son zuwa da ita, kuzo amma kinsan Allah idan aka samu matsala ki kuka da kanki" ya fada da zolaya, dariya tayi"ba abunda zai faru in sha Alah"

"Okay," ya fada tare da yi mata kwatancen inda sitting room din yake.

"Pls kada ku dauki lokaci, suna jiranku" cike da zumudi ta amsa mashi da toh, katse kiran yai tare da juyawa ya dubi su dr shureim sunyi shiru suna jiran tsammani, kallon benazir yayi ta kifa kanta kan sofa hand, idan yace baiyi kewarta ba yayi karya, almost 17yrs rabon shi da ita, ta canza mashi ba kaɗan ba, ya danyi mamakin girmanta, ta zama babbar mace ba kamar lokacin daya aureta ba, yar siririya da ita sai rashin kunya cike da kai, daurewa kawai ya ke yi ba ya san ta gane ya yi kewarta yafi so ta ɗanɗani irin ɗacin da ya ji aran shi na irin bakin cikin da ta kunsa mashi, Abun Ya ta6a zuciyar shi ba kaɗan ba, ƙwara itama taji ajikinta kamar yadda yaji, batare da sanin su ba, Ya fuce daga sitting room din Ya koma waje Ya tsaya zuciyar shi cike fal da tunaninta, Allah sarki tsohuwar zuma, yajima yana tambayar kanshi meyasa zatay mashi haka? Laifin me yayi mata? bai ta6a tsammanin tsanar da tayi mashi takai harta haifa mashi jinjira ta ajiye acikin kwamin wanka ta gudu tabar su, kusan shekara goma sha bakwai, bata ta6a waiwayarsu ba, taya zai iya yafe mata cikin sauƙi? Idanunshi ne suka ciko tab da kwalla, da sauri ya jingina kanshi jikin bango, Allah kadai yasan radadin da yake ji acan kasan zuciyar shi,

Maganar anila ya fara tariyowa inda take ce mashi bafa yin kanta bane, shiga akayi tsakaninsu, bada son ranta ta gudu ba, har yanzu tana son su, girgiza kai yai cikin karyayyar murya ya furta"ban yarda ba, nasan wacece Benazir, zata iya aikata fiye da haka ma, dama ba sona takeyi ba..." shi kadai yake sambatun shi abunne ya dame shi.

"Har yanzu shiru basu ƙaraso ba, ko dai Azeezatyn tana a school ne"? Dr shureim ne yayi maganar

Anila tace"nima nayi tunanin hakan, watakil sai an daukota daga school, mu dan kara hakuri" ta fada tare da kallon Benazir da ta langwa6e kai jikin sofa, ta lumshe idanunta... Tsantsar tausayinta ne ya kamata, dr shureim yayi tunanin saboda azeezaty ta shiga halin damuwa hakan yasa shi yi mata gyaran murya ta buɗe ido ta kalle shi"meke damunki ne? Tun da muka shigo na lura da yanayinki! Nasan bai wuci saboda azeezaty bane ko"! Murmushin yaƙe ta sakar mashi cikin sanyin murya tace"kamar ka sani ya shureim,
wlh na ƙagara da in ganta, kamar zan zauce" yar dariya yayi tare da miƙa hannu kan table din gaban sofa din, Ya dauki juice Ya zuba a cup, yana kokarin kaiwa bakinsa Ya ɗan dakata Yana sauraron muryoyin da kunnuwanshi suke jiyo mashi

"Mu je ciki mana"

"Dan Allah ki fara shiga, ni wallahi kunya nake ji,"

"Meye abun kunya a ciki, Aunty Anila ce fa, tare da aunty Benazir, ni ki wuce mu shiga..."

Kusan atare Anila da Benazir suka dubi ƙofar sitting room din, su biyu ne ɗaya ta rurruƙe ɗayar da ta turje akan ba zata shiga ba, Kamar zasu yi dambe, kwata kwata basu ga fuskokin su ba, Ita Batool mayafin da ta yi rolling akanta ne ya warware ya rufe fuskarta, sakamakon ingizatan da unaisah takeyi, Yayin da ita kuma Unaisah take abayanta tana kokarin tursasa mata akan ta shiga, murmushi Anila da benazir suka saki suna kallon ikon Allah

Cikin sanyin murya dr shureim Ya furta"Ki bi ta a hankali pls, kada ki ja ta fadi taji ciwo"

Sponsored Post
Tags
Kurkukun Kaddara
YOU MIGHT LIKE
POST A COMMENT
Idan kuna da tambaya akan abinda Baku game ba ko kuma kuma Neman littafin da babu a nan kawai ku ajiye tambayarku a ta comment ko wani shawara da Zaku bamu.

Previous Post
Next Post
GET IN TOUCH
Facebook
twitter
YouTube
Instagram
Whatsapp
SUBSCRIBE US

OPINION
FACEBOOK
COMMENTS
CATEGORIES
Africa
(1)
Al'adu
(1)
Alkamawa
(3)
Article
(3)
Blogger Tips
(1)
Economy
(5)
Education
(2)
Entertainment Gist
(1)
Gyaran-Jiki
(5)
Health
(13)
Jikar Iya
(11)
Kimiya
(1)
Kiwon Lafiya
(54)
Kukan Zuci
(5)
Kwalliya
(4)
Labaru
(23)
Lifestyle
(1)
Ma'aurata
(1)
News
(300)
Nigeria
(5)
Noma
(1)
Opinion
(3)
Picture
(3)
Politics
(15)
Profile
(2)
Q&A
(1)
Ramadan
(9)
Ramadan Tafsair
(1)
Siyasa
(1)
Sports
(72)
Tarihi
(5)
Technology
(1)
Tips
(3)
Video
(3)
YouTube
(5)
Zain Abeed
(1)
Zamantakewa
(1)
Novels Elite
Get the Most Exciting News and Read Your Favorite Hausa Novels. Let us be your source for exciting news reports worldwide, as well as access to a wide variety of blogs and blogging tools. We also offer novels in different languages including Hausa so you can easily read what interests you! Plus with our Google Adsense partner program, monetize when readers engage with your content.

Novels Elite
SUBSCRIBE
Posts
Comments
Links
Post a Job

LATEST POSTS

ADVERT
Novels Elite
Copyright © 2024 Novels Elite | All Rights Reserved
DMCA.com Protection Status
Disclaimer |
Privacy Policy |
Terms and Conditions
[14/10, 6:06 PM] ‎Amin@ M Yusuf Yol@: Home
Kurkukun Kaddara
Kurkukun Ƙaddara Takun Ƙarshe page 44 Complete by Boss Bature
by
Novels Elite Admin
September 06, 2024
Sponsored Link

BOSS BATURE✊

Jin maganar dr shureim yasa ta saki Batool da ke ta faman yin haki, tana ta ƙoƙarin Gyara veil ɗinta daya rufe fuskarta Unaisah taja hannun ta suka nufi Ciki, Gaba ɗaya idanun su Benazir na akan su, Yadda suke tafiya a tsanake cikin nutsuwa yayi matuƙar burge su, Tamkar tagwaye komai na jikinsu kala ɗaya, gwanin ban sha'awa suke kallon su, Batool sai kiciniyar gyara mayafin takeyi takasa ga ɗan kunnanta da ya maƙale gashinta kwata kwata Unaisah bata lura da halin da take a ciki ba, sai janta ta ke yi.

"Babyna" Benazir ce ta kira ta da sauri ta dubi inda take atsaye lokaci ɗaya ta saki murmushin farin ciki, ta saki hannun Batool cike da zumudi ta nu fe ta Benazir ta rugumota a kirjinta kamar zasu koma mutun ɗaya, wani irin sanyi ne Ya ratsa zukatan su, kamar sun yi shekara ba su haɗu ba sunyi kewar juna.

Fuskar Aneelerh ɗauke da murmushi take kallon su har cikin ranta taji dadin faranta ransu da ta yi...

"Babyna, nayi kewarki, shi ne kika tafi kika barni, fushi nake dake baki damu dani ba" ta fada tare da ɗago kanta ta haɗe fuska alamar bata ji dadi ba' rufe fuska unaisah tay da tafukan hannayenta cike da jin nauyinta ta furta"i'm really sorry mommy na, wallahi na damu dake, ban manta dake ba kina araina"

Murmushi Benazir tay, tare da manna mata peck a forehead ɗinta, ta tallabo fuskarta da tafukan hannayenta, wani irin kallon so da kauna take bin ta da shi kamar zata maida ita cikin cikinta, tuni Unaisah tasha jinin jikin ta da ganin irin kallon ƙurullan da take yi mata.

 Bakomai take tunawa ba face lokacin data barta a kwamin wanka yar jinjira da ita cikin jini, sai gashi Allah ya raya abun shi, ta girma ta zama ƴar budurwa da ita, tsakaninta da taj sai godiya yayi namijin ƙoƙari gurin rainon Angel, har abada bazata ta6a rabuwa da shi ba, ko da bazai kula ta ba sai ta san yadda tay ta maida auran su ko dan saboda Unaisah, ganin bata da alamun daina kallonta ne yasa ta ƙara rudewa muryarta adabarbace ta furta"Ya jikin naki? Kin ji sauƙi"? Yar dariya Benazir tay don ta fahimce unaisah ta gano ta

Ɗaga mata gira tay"Alhamdulillah my baby, naji sauƙi sosai..."

"Yanzu kin gane ni wacece" dariya suka yi gaba ɗayan su, Hakan Yasa ta fahimci taji sauƙi yanzu tasan ita ba ƴarta bace.

.

"Ki ɗauka har yanzu ban dawo cikin hayyacina ba, saboda bana so ki daina kira na da sunan mamanki, kuma bana so na rasa kulawar da kike bani" tattausan murmushi unaisah tay"in dai wannan ne baki da matsala dani, zan cigaba da kiranki mamana, babu abunda zai canza"

Gaba ɗaya Sun maida Hankali akan Unaisah, In ka cire dr shureim wanda gaba ɗaya ya tattara Hankalin shi akan Batool dake ta ƙoƙarin gyara mayafinta ga raɗaɗin da kunnanta ke yi mata duk tabi ta burkice, ajiye cup din hannun shi ya yi kan table tare da miƙewa ya je gabanta ya tsaya ya ruƙo Veil ɗin Zai gyara mata jin hannun mutun yasa muryarta na rawa ta furta"Earring ɗina Ya maƙale gashina za fi nake ji" 

'Okay, calm down, I'll help you."
Chapter 136 · 0% Book details